Showing 174001 words to 177000 words out of 218703 words

Chapter 59 - Sakayyah 2 Hausa Novel Complete

riƙe dashi akan ki?”.
Kai ta gyaɗa cikin tabbatar tace.
“Tabbas kuwa har abada bazan manta number motar nan ba saboda na ganta alokuta uku maban-banta na ganshi a Jauro Yaya.
Na ganshi a bakin Makarantar mu.
Sannan ranan da muka yi rabuwa ta ƙarshe da Yah Jameel na ganshi yana bibiyarmu”.
Numfashi ya fesar tare da faɗin.
“Yanzu zaki iya faɗa min?”.
Kai ta gyaɗa mishi.
Ganin hakane yasa ya
ɗauki wayarsa ya danna kan number Sheikh Jabeer ya shiga wajen text yace.
“Gashi sa”.
Karɓa tayi ta rubuta number motar da komai da komai harda collor ta miƙa masa number ya tsirawa idanu sai kuma ya kalleta yace.
“Kin tabbatar shine dai-dai?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Na tabbata shine babu shakka ko Haufi ko yanzu na rufe Idanuna ina kallon number motar”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Ok ba laifi”.
Ba ɓata lokacin ya yiwa Sheikh Jabeer sending.
Ahankali ya maida hannunsa kan cikin nata wanda zuwa yanzu ya fara bayyana kallonta yayi tare da langwaɓar da kai yace.
“Minha yunwa nake ji mai zan samu?”.
Tana lunshe Idanunta cikin nasa tace.
“Mekake so?".
Muryansa cike da kasala ya sake narkewa jikinta tare da cewa.
“Me kika yi min?”.
Manyan Idanunta ta juya sai kuma ta sakar masa da murmushi tare da cewa.
“Nayi maka abinda kake so?”.
Ɗan ware idanunsa yayi yana cigaba da shafa cikinta yace.
“Mene?”.
Langwaɓar da kai tayi tace.
“Nayi dambu a tunanina zan iya ci sai kuma naji bazan iya ciba”.
Wani kallo ya mata me cike da tarin tausayi da jin ƙai yace.
“Ke kuma me yake miki daɗi In banda Fakala ba”.
Da sauri ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta tare da cewa.
“Kai Yah Mu'allim”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Ehem sai an jima da daddare zaki ce min kina son pakala”.
Marairaice fuska tayi kana tace.
“Ni dai wallahi kabar faɗa min haka kar kayi min sharri”.
Idanunsa ya buɗe kanta tare da faɗin.
“Sharrine ma?,Toh bari zan kama kine?”.
Murmushi tayi tare da faɗawa jikinsa amma bata ce komai ba.

AnanTaraba shirye-shiryen biki ya kankama tuni aka fara gyara amare an killace su.

Momy da kanta je gyara Asma'u Asiya ita ke mata Dilke sai wani ƙyalli suke sunyi kyau gwanin ban sha'awa soyayyar ta da Dr Jameel ɗin ta kuwa na tafiya hakama su Asiya.
Yau ya kama Auren saura kwana goma wanda ya rage saura kwana uku Moddibo su taho da Angwaye da ƴan ɗaurin Aure.

Yau tun safe Ummi da kanta da Asma'u suka tafi gidansu Innayi kasancewar key na hannunta Ummi da kanta ta shiga Side ɗin Moddibo da kanta ta gyara masa ta killace Asma'u kuwa gefen Innayi ta gyara ta killace ko ina yayi gonin ban sha'awa.
Ga kuma sabbin part guda biyu da ake ƙenƙesa sabon gini, na alfarma wanda tuni an gama komai nasu, wanda bisa shawarar inanayi aka tsara da umarnin Abualeey tare jagorancin Abban Jameel abune na kuɗi shiyasa tuni an gamsu wanda nanne masauƙinsu in sun iso.

Morocco Khausar ce kwance akan kujerar bisa alamu da Momy take waya cike da farin ciki ta gyara kwanciyarta tare da cewa.
“Momy In sha Allah mun kusa zuwa".
Murmushi Momy tayi kana tace.
“Toh Khausar me kike so in shirya miki idan kin zo.
Ga Raudhat baki ɗaya lissafinta da tunani Adda Khausy ta kusa daeowa.
da an taɓa ta sai tace sai Addah Khausy tazo, wanka ma ƙinyi tayi yau wai sai Addah Khausy tazo tayi mata”.
Dariya Khausar ta sanya tare da faɗin.
“Yau mun bonu kafin inzo ai datti zai kashe ki Raudat ”.
Ta ƙare faɗin haka jin muryan Raudat ta amshi wayar Raudat kuwa itama cikin dariya tace.
“Addah Khausy datti bazai kashe niba fa zan riƙa fesa turare sannan insa humran Momy saboda nayi kamshi sai kinzo ki min wanka”.
Dariya suka sanya Dukansu daga nan suka cigaba da hira.
Suna gama waya dasu Momy ga Mamaki ta sai ga kiran Hajja Nana ya shigo tana ɗagawa tace.
“My Kakus”.
Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin.
“Ƴar tselen Uwa tunda muka dawo sau ɗaya mukayi waya dake baki sake kirana ba”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Kai Hajja Nana kuma abin harda Sherri ne?
kin manta cewa garin ku babu network in baku kuka kira ba baya shiga, kullum fa kina raina”.
Dariya Hajja Nana tayi tare da faɗin.
“A yayi kyau yaushe zaku zo?”.
Cikin sauri tace.
“Next week”.
Cikin so da ƙauna Hajjaj Nana tace.
“Yau da kaina na ɗibo ƙafana har bidhiyar ƙare zancenka saboda inji Labarin Ƴar jikata dan nayi kewarki ina so in San yaushe zakuzo”.
Khausar na murmushi me ɗauke da ƙaunar Kakar tata tace.
“In sha Allah nan da kwana uku dai muna cikin Nigeria”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh Allah Ubangiji ya kawo ku kafiya”.
Bayan ta gama wayar ne ta miƙe ahankali kasancewar tun safe bata leƙa Didi ba kallon jikinta tayi ganin dogon riga ce budadde da mayafinsa babba yasa ta sauƙa falonta ta wuce Side ɗin Didi.

Tana shiga Falon ta samu Didi zaune da ahlinta, Modibbo Sai Zakariyya da Dr Jameel, Sai kuma Lalla Khadijah da Lalla Salma da Hafsat wanda ga duk kan alama sunzo tafiya bikin ne Didi na ganinta ta miƙa mata hannu idanunta akan cikinta,.
Sai lokacin itama ta kalli cikin ta ga Mamaki ta sai taga cikin nata har ya tura rigar ta kaɗan cikin jin kunya ta zauna gefen Didi cike da kulawa Didi tace.
“Barka da yamma?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Yawwa Barka dai Didi”.
Didi na gyara zama tace.
“Yau tun safe nake ta zuba ido zan ganki ban ganki ba ki shigo ba, nace Rahama taje ta du baki data dawo sai tace kina bacci”.
Tana kallon Moddibo tace.
„Eh Didi ina bacci ban daɗe da tashi ba shine nayi wanka sai kuma na ɗanyi waya da Momy na Momy tace in gaishe ki ma”.
Fuska a sake Didi tace.
“Ina amsa wa Masha Allah fatan suna lafiya?".
Kai ta gyaɗa tare da faɗin.
“Lafiya ƙalau”.
Ita kuwa Khausar kallonta ta mayar kan Lalla Khadijah da Lalla Salma da Hafsat cike da girmamawa ta gaishesu cikin sakin fuska suka amsa mata suna tambayar jiki.
Kallonta ta mayar kan Didi jin tana cewa.
“Khausar ya shirye-shiryen tafiya?”.
Dariya Khausar ta sanya tare da faɗin.
“Aini har na gama shirya wa ma”.
Ahankali Moddibo ya ɗago Idanunsa ya kalleta kana yace.
“Toh da kika gama shirin ma ai ke ba zuwa zakiyi ba”.
Zare idanunta tayi sai kuma ta kwaɓe fuska ahankali ta maida kallonta kan Didi dake murmushi tace.
“Didi kiji fa abinda yake cewa".
Ɗan dariya Didi tayi ganin yanda ta kwaɓe fuska yasa tace.
“Rabu dashi waya isa ya hana ki zuwa Mamana ai kece agaba idan baki zoba amaren ma baza su zoba”.
Ware idanu Dr Jameel yayi tare da sanya dariya yace.
“Anya kuwa Didi wannan zai saɓu dan bata jeba ace Amare baza su zoba ai ita ta zauna gidan mijinta mu muje mu ɗauko Matan mu". Cikin murmushi Zakariyya cewa.
“Gaskiya dai kam”.
Dariya Didi ta sanya kana tace.
“A'a Zakariyya har kaima wato zama da Jameelu ya dawo da kai mai surutu da baki”.
Dariya Lalla Khadijah ta sanya tare da faɗin.
“Aikam Didi Hausawa sunce zama da maɗaukin kanwa shi ke kawo farin kai".
Dariya suka sanya Lalla Hafsat ta karɓe da cewa.
“Aikam dai ko kurma ne ya zauna da Dr Jameel Sai ya koyi magana".
Zakariyya kuwa ƙeya ya sosa tare da sunkuyar da kai...

Ɗago kansu sukayi atare tare da kallon Ibraahim dake shigowa cikin mamaki suka haɗa bakin cewa.
“A'a Ibraahim kuma”.
Kai ya gyaɗa tare da buɗawa Rahama hannu wacce ta nufo kansa da gudu da murmushi afuskarsa yace.
“Surprise dama bazata na shirya muku Yah Jameel ba jiya muna waya kana zaton bazan zoba, har kana fushi”.
Ya ƙare maganar tare da ƙarasawa gefen Lalla Khadijah ya zauna kana ya ɗaura kansa kan kafadarta Dr Jameel cikin murmushi yace.
“Aikam da har nayi fushi da kai”.
Jujjuya idanu yayi yace.
“Amma dai yanzu ka huce ko?”.
Kai Dr Jameel ya gyaɗa tare da cewa.
“A na huce tunda kazo”.
Lalla Salma ce tace.
“Toh dama taya za'a yi Auren Yayun ka har biyu baka nan ai dole saida babban ƙanin ango za'a ɗaura Aure”.
Dariya yayi tare da faɗin.
“Aikuwa dai Lalla Salma kin gane”...
Haka dai suka cigaba da hiransu.

Ana gobe zasu tafi da misalin karfe goma na dare Moddibo ne kwance a gefen Khausar yana romance ɗin ta tare da shafa cikinta ahankali ya ɗago Idanunsa ya kalleta tare da cewa.
“Gobe idan munje Nigeria gidan Innayi zamu sauƙa” .
Idanunta dake shanye kamar na mai jin bacci ta buɗe tare da tura baki tace.
“Yah Mu'allim gidan ku kuma? Nikam dai inje gidan Momyna ”.
Da sauri ya ware idanunsa tare da dafe ƙirjinsa kana yace.
“Na isa ki tafi kibarni da waye idan kin tafi gidan Momy?”.
Cikin tura baki tace.
“In barka da Innayin ka mana”.
Kissing ɗin goshinta yayi tare da cewa.
“Innayi zata bani abinda kike bani ne Minha?
Innayi bazata bani abinda kike bani ba Minha sabida duk duniya babu wanda yake bani abinda kike bani fa Minha ya za'a yi kice dan ina tare da wasu za kiyi nesa dani ai bazan iya jura ba”.
Ahankali ta fesar da numfashi tare da cewa.
“Kai Yah Mu'allim Kuma fa kasan nayi missing na Momy”.
Tafin hannunta ya riƙe cikin nasa yana matsawa yace.
“Nayi miki alƙwari idan munje kullum zan na kaiki ki wuni amma kwana bazan barki ba.
Babyna ma bazai iya ba saboda yana son ɗumin jikin Abbansa”.
Ta buɗe baki da niyar magana ta fasa jin wayarsa na ruri ahankali ya miƙe tare da janyota jikinsa yana shafa bayanta ganin number Sheikh Jabeer yasa ya dauka muryansa can ƙasa yace.
“Kai baka san dare yayi bane?".
Ware idanu Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.
“Ƙaniyarka ne ni kake faɗawa dare yayi?”
Cikin kwaɓe fuska Modibbo yace.
“Toh Amman dai kasan inada iyali ko?”.
Wani irin murmushin mai cike da tuna baya Sheykh Jabeer yayi tare da cewa.
“Hmmm yaro man kaza da kake cemin bansan dare yayi bane shin baka san cewa duk abinda ɗanyen ganye ya sani ya kuma ganiba bushesh-she ya riga saba".
Murmushi Moddibo yayi tare da cewa.
“Can maka dai da karin maganar ka Ni ban fahimci me keke nufi ba".
Dariya Sheikh Jabeer yayi kana yace.
“Ai baza ka fahimta ba,
amma dai kasani duk abinda kake tunanin kasan shi na fika sanin shi kai abayana kake”.
Moddibo kuwa hannu ya cusa cikin sumar kan Khausar yace.
“Toh naji Ni dai yanzu ka faɗa min me yake tafe da kai ina da abinyi”.
Cikin so na kaka da jika Sheykh Jabeer yace
“Eh Ya maka kyau.
Dama akan batun number motar da kuka turo min ne tun jiya nayita kiranka baka ɗauka ba bansan me kake ba”.
Cikin sauri Moddibo ya dai-daita nutsuwarsa tare da cewa.
“Kuma banga Miss call ɗin ba”.
Cikin fesar da numfashi Sheik Jabeer yace.
“An samu motar cikin motocin da aka kamo sannan acikin mutanen ana so gane su waye ke amfani da motar dan mutanen kusan su ashirin da biyar aka kama.
Toh muna so mu gane su waye ke amfani da wannan motar sannan su waye suka sace Jameel suka kashe sa”.
Cikin fesar da numfashi da kuma rauni Moddibo yace.
“Alhamdulillah in Sha Allahu Jinin J bazai tafi abanza ba”.
Kai Sheikh Jabeer ya jinjina tare da faɗin.
“Yanzu shine abinda muke so tunda har ita mai ɗakin ka ta gansu tasan Fuskarsu tunda jibi kuna hanya idan kun iso kafin ku wuce sai munje kun gan su”.
Cikin sauri Moddibo ya runtse idanunsa yace.
“Yah Sheikh bana son ganinsu”.
Ahankali Sheikh Jabeer yace.
”Meyesa?”.
Araunane ya girgizar kai tare da cewa.
“Bana son ganin waɗanda suka kashe min J idan na gansu bansan me zanyi musu ba, kar nazo nima nayi abinda bashi bane, bansan mai zan musu ba, na tabbatar dai in na zan ga wanda ya kashe J.
Bazan iya barinshi arayeba zan iya yi musu komai”.
Cike da nutsuwa da dattako Sheikh Jabeer yace.
“In sha Allah babu abinda zaka musu dole zaku zo ku gansu ”.
Idanunsa na tara hawaye yace.
“Bazan gansu ba bazan iya ba har abada bana ƙaunar ganinsu.
Babu wa'anda na tsani gani a duniya sama dasu”.
Ahankali Khausar ta miƙe ta zauna Sheikh Jabeer kuwa ahankali yace.
“Toh ba laifi ku dai ku shirya idan kun zo sai kun biya nan”.
Kai ya gyaɗa tare da katse kiran sai kuma ya maida kallonsa kan Khausar cike da rauni lokaci ɗaya mutuwar Jameel ya dawo masa sabo idanunsa muryansa cike da sanyi da kuma rauni yace.
“Kinji fa waifa cewa yayi inje in Kalli waɗanda suka kashe min J.
Ina zan iya kallonsu?”.
Hannunta tasa ta tallafo kansa tare sa ɗaura aƙirjinta kana tace.
“Yah Mu'allim zamuje ko domin mu tabbatar da cewa suɗin ne suka kashe sa sannan mu tabbatar da cewa suɗinne an kamasu, sannan ayi musu hukunci dai-dai da laifinsu.
Ni na tabbatar muddin na gansu wallahi zan gane su da Izinin Ubangiji”.
Araunane ya girgiza kai tare da cewa.
“Muje kuma Minha?, Minha bazan iya ganin suba fa”.
Kansa ta tallafe tana ɗan shafa bayansa alamar kontar da hankali tace.
“Yah Mu'allim zamu iya zamu iya ganinsu kodan ahukuntasu abinsa cutar damu da sukayi”.
Zuciyarsa na ƙuna yace.
“Minha zan iya musu abinda basuyi tunani bafa”.
Sake tallafo kansa tayi tare da cewa.
“Yah Mu'allim babu abinda zaka musu hukumane za tayi aiki akansu kamar yanda Shari'a ta tsara”.
Ta ida maganar tana shafa kansa ganin yanda mutuwar Jameel ya dawo masa sabo ahankali ta haɗe lips ɗin su waje ɗaya wani gauron numfashi ya saki tare da janyo jikinsa ya fara shafa sassan jikinta ahankali ya ɗago kai ya kalleta tare da yin murmushi kana yayi ƙasa da rigar baccin jikinta muryansa ashaƙe yace.
“Minha kina ganin gaba ɗaya abin nan sai sake girma suke”.
Shanyayyun idanunta ta ɗago ta kallesa tare da sakin murmushi hannunta na shafa kansa tace.
“Yah Mu'allim ba dole su sake girma ba gaba ɗaya ka buwaye su ka gigita su sannan ka hanasu nutsuwa da kwanciyar hankali ”.
Hancinta ya lakace yace.
“Ba dole ba waɗan'nan kayan marmarin ai ba'a barinsu Minha suna da matsayi babba dama rashin samun hannu ne shiyasa basa girma sosai yanzu kuma kinga sun samu”.
Dariya tayi haka tayi ta yi masa abubuwan da suka mantar dashi damuwa da kuncin daya shiga haka suka kwana cikin farin ciki...

Ranan dasu tafi Misalin 12:00pm jirginsu ya tashi daga kasar Morocco zuwa Nigeria.
Kasancewar Private Jet ne shida Khausar suna First class daga can ƙarshe Zakariyya,Dr Jameel, Abualeey, Galadima, Waziri, suma na cikin First class daga gaba sai Innayi kana Didi, Lalla Khadijah da Lalla Hafsat duk suna baya.
Misalin ƙarfe biyar dai-dai jirginsu ya sauka a Adamawa kai tsaye motoci suka zo suka ɗauke su daga Airport zuwa fadan Mai martaba sarki Jabeer Nuruddeen Bubayaro.
Kyakkyawan masauki na musamman aka basu anan suka kwana bayan anyi musu tarbar na mutuntaka Didi takasance ga Mahaifiyarta da Mahaifinta sannan ga Ummi Kakarta Ummei Jakadiyarsu.
Washe gari da safe Misalin ƙarfe bakwai na safe Sheikh Jabeer da kansa ya wuce Masauƙin da aka bawa Moddibo da Khausar yana shiga ya samu Moddibo na haɗa mata tea.

Juyawa Moddibo yayi ya kallesa tare da faɗin.
“Wai ya kake shigo mana haka ba neman izini”.
Kallonsa Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.
“Ka manta nan Fada tace ba Fadar kuba da zaka ce sai na nemi izini”.
Murmushi Moddibo yayi yana mikawa Khausar tea ɗin yace.
“Toh me kake nema da sanyi safiyar nan da kazo mana?”.
Sheikh Jabeer na gyara tsayuwar sa yace.
“Tashi zakuyi mu tafi inda zamuje”.
Langwaɓar da kai Moddibo yayi tare da faɗin.
“Ni bazan jeba”.
Cikin sauri Khausar tace.
“Kayi haƙuri Yah Mu'allim muje”.
“Gwara kam ki faɗa mishi muje mu tabbatar dan kada aɗaurawa wasu laifin da bana su ba”.
Haka dai suka ta lallaɓa Moddibo har ya amince suna fita sai ga Amintaccen Hadimin Sheikh Jabeer ya ɗauke su a mota suka tafi kurkukun dake cikin Yola suna isa bisa sirri akayi musu jagora da iso, aka wuce da ciki.

Duna shiga Khausar tayi saurin komawa bayan Modibbo tare da riƙe hannunsa gama, cikin rawan jiki ta ɗago hannunta tana nuna wasu ƙattun mutum biyu da babu alamun imani tare dasu, shiyasa aka ɗan waresu gefe suna zaune sai kuzurai suke.
Cikin tashin hankali gami da tsanarsu ta fashe da kuka murya narawa tace.
“Ga sunan wallahi Yah Mu'allim sune, sukayi ta bin motarmu da Yah Jameel randa aka sace shi, kuma sune suka je Jauro Yaya sannan kuma sune suka je bakin Makarantar.
Wallahi tallahi sune suka bibiye mu aranan da muka rabu da Yah Jameel na ƙarshe har da muka tsaya a suma suka tsaya”.
Cikin Tsananin tsana takaici da ƙunar rai Modibbo ke binsu da wani irin kallo mai nuna jin zafin illar da sukayi mishi.
Shi kuwa Sheikh Jabeer nan take yasa aka killace su waje na musamman da kansa ya tsananta bincike Matsayin sa na SS mai zaman kansa wanda yasan kansa da aikinsa da ƙirewa.
Bisa jagorancin Jalal yasa aka musu ɗan banzan bugun da ya karya ƙarfin zuciyarsu.
Kana yacewa su Modibbo su shiga.
Cikin tsaresu da ido ya nuna musu Khausar tare da cewa.
“Kunsanta?”.
Agalabaice suka ce.
“Eh mun santa itama an bamu kwangilar kashe ta”.
Aruɗe ta zare ido kana ta ɗaura hannunta aƙirji tace.
“Kasheni kuma nima? me nayi muku”.
Kai Sheikh Jabeer ya jinjina kana ya nuna Moddibo dake binsu da wani irin kallon tsana gaba ɗaya jikinsa rawa yake shi kuwa Sheikh Jabeer cikin sanin makamar aikinsa yace.
“Wannan fa kun san shi”.
Kai na farkon ya gyaɗa tare da faɗin.
“Eh ai dama shi tare aka bamu kwangilar karshe sa da Malam Jameel”.
Zama sheikh Jabeer ya gyara tare da faɗin.
“Waya baku kwangilar kashe su?
Sannan akan me zaku kashe su?”.
Ɗayan da yafi galabaitane ya ɗago fuskarsa da duk halittarsa ta canza saboda azabebben bugu da ya sha yace.
“Mu mutanen garin dake gefen Jauro Yaya ne, kuma manyanmu ne suka bamu kwangilar karshe su".
Akai Khausar ta ɗaura hannu tare da faɗin.
“Ai kune ma na gani a Jauro Yaya ”.
Cikin tsawa Sheikh Jabeer yace.
“Me ya kaiku Jauro Yaya kuma?”.
Na farkon ne ya karɓi zancen da cewa.
“Mu muka kashe Garkuwan Rugar Jauro Yaya Umaru”.
Wani irin raunataccen kuka ne ya kubcewa Khausar yayinda gaba ɗaya jikinta ya ɗauki rawa.
Jalal kuwa a hankali ya gyara riƙon da yayiwa wayarsa saboda video'nda yake yi musu.

Zama Sheikh Jabeer ya gyara tare da ci gaba dayi musu tambayoyi.
Shi kuwa Moddibo gaba ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake ji yake duniyar tayi masa ƙunci ji yake tamkar ya fisge bindigar dake hannun Sheikh Jabeer ya kashe su kowama ya huta”.
Amma ya kasa motsa wa saboda Khausar dake rungume dashi ita ta hana shi motsi.
Dayan ne ya karɓi maganar da cewa.
Kamar haka uuna ɗaya daga cikin mutanen dake Maƙoftaka da Rugar Jauro Yaya wanda sun kasance arna ne sannan manyan sune suka bamu umarnin su kashe Garkuwan Rugar Jauro Yaya saboda shine yake shiga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login