Showing 171001 words to 174000 words out of 218703 words
shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
*SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!*
*PART OF OUR DESTINY*
*Shin ko kunsan shahararriyar marubuciyar nan me suna *FATYMASARDAUNA* marubuciyar *SHU’UMIN NAMIJI* *SOORAJ* *LAYLERH MALEEK* *MAJNOON* ta sake kawo muku sabo kuma dadd’an littafinta dake cike da tarin zazzafar soyayya me gigita hankali, sadaukarwa, k’addara, da kuma hamshakiyar Kaunar dake gudana acikin jinin jikin mazaje guda biyu da suka kasance y’an uwan juna, duk acikin littafin nata me suna *PART OF OUR DESTINY* kada ku sake abaku labari domin samun karantawa da kuma shiga cikin group din marubuciyar zaku biya 500 ne kacal ta wannan account number din 2268498748 Fatima Abubakar UBA bank, ko ku tuntub’eta ta WhatsApp number dinta kamar haka 07069917168.
Kada ku Bari abaku labarin wannan littafi me suna *PART OF OUR DESTINY* littafine dake cike da tarin zazzafar soyayya....
Ahankali ya kwantar da ita kan cikinsa, tare da yi mata pillow da ƙirjinsa, sai kuma ya jawo blanket ya ɗan rufe su. ahankali ya haɗa tafin hannunsa waje ɗaya tare da karanta addu'oin bacci _Falaƙi, 3 Nasi 3, Ƙulhuwa 3, Ayatulkursiyyu, 1 kana ya haɗa da Amanarrasulu1 Laƙadja'akum_ yanayi yana hura hucin numfashi nai cikin tafukan hannunsa.
Cikin kulawa ya shafa mata kana.
Yayi kansa shima ya shafa ajikinsa yana mai lumshe Idanunsa, hakanan yake jin wani irin farin ciki wanda tunda yake a iya tsawon rayuwarsa bai taɓa riskan labarin da yasa shi farin ciki da jin daɗi ba kamar wannan labarin ba, ko labarin kasancewar su Didi iyayensa baisa shi farin ciki kamar wannan labarin cikin nasa ba, ya rasa ya aka yi labarin ya kasance masa baƙon lamari abin yazo masa abazata, sabodaai kawo hakan a ransa da sauriba, shi ganima yake ai Khausar ɗin ƙaramace.
Haka ya kwana cikin tsananin jin daɗi da farin ciki kusan a zaune ya kwana da zaran ta motsa zai gyara mata kwanciya.
A gefen Hajiya Bunayya ma ita ma haka ta kwana da azabebben ƙaiƙayin dake addabar rayuwarta Rayuwa tayi mata ƙunci haka ta kwana ƙaiƙayi ya hanata kataɓus.
Ana kiran Sallar Asbah ta fara sauƙe numfashi saboda jin ya fara lafawa, kamar abin Jaraba ƙaiƙayin ya daina wunin ranan haka tayi tana rama bacci da bata samu ta yi shi a daran ba.
Ana kiran Sallar Maghriba ƙaiƙayin na Assalamu alaikum yana sake dawowa haka wannan ranan ma haja ta kwana ƙaiƙayi, gaba ɗaya ta rasa inda zata sa kanta jin ƙaiƙayin ya gallaza mata yasa ta haɗa ruwan zafi da gishiri ta cika Baho da ruwan ɗumi da gishiri ta shiga cikin.
Numfashi wahala ta fara sauƙewa jin abin ya fara lafawa,
Sai kuma tayi saurin sunkuyar da kanta jin yadda wasu abubuwa caccakarya a wurin.
Ido ya kuma fiddawa sosai saboda ganin wasu ƙananan tsutsotsi masu baƙin baki suna fita ta gabanta asaman ruwa bisa alamu sune suke sa mata ƙaiƙayin kuma suke hanata bacci.
Shiyasa idan ta shiga ruwan zafi sai take jin sauƙi idan ta fita kuwa ko awa ɗaya bazai kai ba zai da meta..
Haka dai take fama da wannan rayuwar da zaran dare yayi tayi sallama da kwanciyar hankali da bacci sai kuma safiya.
Haka ta rayu tsawon Makonni biyar tana fama da wannan azabebben ƙaiƙayin da bai nuna alamun akwai sauƙi ko sassauci ba.
A gefen Samira Sani ma ita baki ɗaya rayuwa ta sake yi mata ƙunci da duhu abin ba a cewa komai.
Morocco Acan gefen su Khausar kuwa rayuwa tayi daɗi Khausar na samun kulawa na musamman daga gefen uwar mijinta da kuma Kakar Mijinta Niyna kana da Innayi.
Hadimanta nayi mata komai daya kama na rayuwa har zuwa yanzu bata iya wani cin abinci amma ko yaushe cikin Hidima suke mata haka Didi nayi mata komai na sungullan rayuwa takowa mata wannan ta kawo mata wancan, amma bata iya cin komai yau tsawon kwana goma shabiyar da jin labarin Khausar nada ciki, wanda haka yayi dai-da cika wata biyu kenan da cikin yayi.
Kwance take akan 3sitter yayinda tayi pillow da cinyarsa.
Cikin sanyi ya shafa kumatunta tare da juyiwa ya kalli plate ɗin abincinta kwata-kwata ko cakali shida mai kyau bata yiba.
Cikin takaicin rashin cin abinci ya shafa cikinta dake lafe kamar bata da komai cike da damuwa yace.
“Minha”.
A hankali ta ɗan ɗago kanta ta kalleshi jin yadda ya kirata da alamun damu cikin kula yace.
“Rashun cin abinci kinnan yana damuna,
ina ga zan kira Momy in faɗa mata matsalar rashin cin abinci nan koda shawarar da zata bamu”.
Ware manyan Idanunta dake lumshe kamar na mejin bacci tayi tare da cewa.
“Momy kuma?”.
Kai ya jinjina mata, cikin sauri tace.
“Bana ce maka mubar maganar faɗa wa Momy nan ba”.
Yana shafa gashinta yace.
“Gsky ni dai inaga gwara mu gaya mata wata ƙil kiga mun samu mafita?”.
Kai ta girgiza tare da cunno bakinta gaba tace.
“Kenan me zaka ce mata?”.
Kallonta yayi tare da tallafo kanta ya juyo da ita suna fuskantar juna cikin sassauta murya yace.
“Ce mata sanyu Minha bata cin abinci ni kuma rashin cin na damuna”.
Lumshe Idanunta tayi tare da buɗe su akansa cikin yanayin irin mata masu fama da laulayi tace.
“ Idan tace maka me ya hanani cin abinci ke zaka ce mata?”.
Matsota yayi sosai kana yace.
“Ce mata zanyi kina da cikine kuma yana hana ki cin abinci?”.
Zare idanu tayi kamar wacce tayi wani laifi sai kuma ta kife kanta akan ƙirjinsa.
Lallausan murmushi ya saki kasancewar tun washe garin ranan da akace tana da ciki yace zai faɗa wa Momy amma fir taƙi yarda wai tana kunya, sosai ta sake mannuwa ajikinsa kana ta manna kanta da faffaɗan ƙirjinsa cike da kasala tace.
“Nikam Yah Mu'allim Ina kunya taya zaka faɗawa Momy wannan magana Taya zaka faɗa wa Momy cewa ina da ciki Fisabilillahi yanzu sai ka iya faɗa?”.
Murmushi yayi tare da cewa.
”Toh mene cikin nan fa halartacce ne, cikine mai gata mai daraja gashi da mahaifinsa na rasa kunyar me kikeji?”.
Kallonsa tayi da mamaki sai kuma ta langwaɓar da kai tace.
“Yanzu Yah Mu'allim baza kaji kunyar cewa Momy ina da ciki ba?”.
Idanunsa ya buɗe tare da karkata mata kai kana yace.
“Toh me aciki?,me abin kunya aciki don kina da ciki?”.
Wani kallo ta masa mai tattare da shauƙi da yanayi na musamman ahankali ta motsa laɓɓanta kamar mai raɗa tace.
“Yanda aka samu cikin shine abin kunya kowa fa yasan me muka yi”.
Ta ida maganar tana rufe fuskarta janyota jikinsa yayi tare da rungume ta kana yayi murmushi tare da faɗin.
“Toh shikenan tunda baki so, Sarkin kunya zanga yanda zakiyi kuma idan munje Auren su Dr Jameel ai zata ga cikin kafin nan”.
Cikin sauri ta girgiza masa kai tare da narke fuska sai kuma ta janyo hannunsa ta ɗaura akan cikinta tace.
“Toh ai cikin baya wani girma".
Yana ƙunshe dariyarsa yace.
“Ai kafin nan zai ƙaru tunda zuwa lokacin ya cika wata uku tunda kinga an ƙara wata biyu a asalin date ɗin kinga har zai shiga wata na huɗu ma kafin nan”.
Kanta ta ɗan jujjuya sai kuma ta tsirawa sajensa dake ƙyalli Ido tace.
“Ha'a sai dai-dai lokacin Auren yayi zamu tafi ne?”.
Kai ya girgiza tare da cewa.
“A'a sai bikin ya rage saura sati zamu tafi kinga kafin nan cikin ya cika wata uku har ya shiga na huɗu ma”.
Ganin yanda ta narkar da fuskarta ne yasa ya janyonta jikinsa ya sake rungumeta cikin tura baki tace.
“Nikam gaskiya ina jin kunya wallahi”.
Sosai ta bashi dariya amma baiyi ba yace.
“Uyumm idan kina jin kunya ki riƙa cin abinci”.
Narai-narai tayi da idanu tare da faɗin.
“Yah Mu'allim toh bana jin yunwa kaga kuma yanzu nasha fruit Alhamdulillah na ƙoshi”.
Janyota yayi ya rungumeta daga haka bacci ya ɗauke su.
Acan ɓangaren Amina kuwa yanzu baki ɗaya rayuwa tayi mata ƙunci gani take kamar rayuwarta yazo gangara.
Cikin sauƙe numfashi ta kalli Uncle Naseer Dake gefenta kana tace.
“Uncle Naseer bani da lafiya”.
Wani kallo ya mata sai kuma tayi murmushi tare da faɗin.
“Ba wani nan lafiyarki ƙalau”.
Cikin sanyi da kasala daya gama baibaye rayuwarta ta fesar da numfashi kana tace.
“Allah da gaske bani da lafiya Ni nasan yanda nake ji ajikina”.
Yana ɗan latsa wayarsa yace.
“Kada ki damu”.
Araunane tace.
“Ji nake kamar zan mutu”.
A wannan karon ma murmushi yayi yana gyara zamansa yace.
“Baza ki mutu ba yarinya ki kwantar da hankalinki”.
Kanta ta jinginar da jikin kushin tare da cewa.
“Uncle Naseer to yaushe zamu tafi gida naga Auren Addah Asiya ya matso du-du-du saura wata ɗaya da sati ɗaya”.
Juyawa yayi ya kalleta sai kuma ya ɗaga kansa sama alamar tunani yana sauke kansa ƙasa yace.
“Auren saura sati ɗaya zamu tafi kinga yanzu kenan saura 1month zamu tafi”.
Cikin sanyi ta gyaɗa kai tare da faɗin.
“Shikenan Toh Allah ya kaimu”.
Kafin yace wani abu wayarsa ta hau ruri ahankali ya miƙe ya fita tare da picking call ɗin.
Daga ɗaya bangaren akace.
“Ranka yadaɗe nan Veazer ka na komawa India zai fita”.
Cike da farin Yace.
“Alhamdulillah Nagode bari zuwa anjima zan kiraka”.
Kana ya katse wayar tare da komawa Falon ya zauna gefen Amina ahankali ta ɗago Idanunta ta kallesa tare da cewa.
“Uncle Naseer ya batun tafiyarmu Indi'a ne?”.
Still da murmushi afuskarsa yace.
“Sai mun dawo bikin Asiya”.
Cikin sanyi tace.
“Toh Allah ya kaimu”.
Acan gefen Hajiya Bunayya kuwa rayuwa tayi mata tsanani abubuwan ta kullum gaba-gaba yake da safe zuwa rana zata yini cikin kwanciyar hankali sai dai da dare yana yi bata da kwanciyar hankali zuwa yanzu ƙyanƙyamin kanta da kanta ta keyi.
Cikin sauƙe numfashi ta kalli Hajiya Lami Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Na lura ko ɗana Sulaiman ƙyamar zama kusa dani yake yi sannan Lamiɗo koda abinci na kai masa sai yace in tattara in fita dashi shi ya ƙoshi.
Hankalina ya tashi Hajiya Lami kaddai mugun abinda naje yiwa Khausar ya dawo kaina ya addabi rayuwata?
Ji nake kamar ƙaiƙayin yasa gabana ya haɗe da bayana”.
Zare idanu Hajiya Lami tayi cikin yanayin tashin hankali tace.
“Mun shiga ukun mu Hajiya Bunayya wannan wani irin abu muke fuskanta a rayuwar ki kalli haka Samira fa yanzu yanda ta bushe ta rame duk ta lalace sannan nima bana bacci dana kwanta da daddare sai muggan mafarkai na rasa yanda zanyi da rayuwarta”
Cike da damuwa Hajiya Bunayya ta girgiza kai tare da cewa.
“Ke koni?,Auren Asiya sai matsowa yake gashi Lamiɗo ko zama kusa dani muyi maganar Auren nan baya yarda sai kyara da hantara ina ga baƙin jinin da Boka yace Khausar za tayi ya tabbata nice nayi shi”.
Cikin mamaki Hajiya Lami ta tallafe kuncin ta tana sauraron masifar daya riskesu lokacin ɗaya duniya tayi musu atishawar kaji.
Hajiya Bunayya kuwa da damuwa ta cigaba da cewa.
“Ƴaƴana ma duk sun fita harƙana dama Asiya ita tun can ba shiga harƙana take ba.
Kuma abin mamaki itace take ɗan daurewa tana zama kusa dani shekaran juya da taga ina ta fama da ƙaiƙayin nan ina zirya da sintiri shine ta faɗa wa Lamiɗo aje asibiti koda ta faɗa masa ma cewa yayi shi bazai samu damar kaina ba inje in Kai kaina idan na kuɗine in faɗa masa ko nawa ne magana ta ƙare”.
Tallafe kunci Hajiya Lami tayi kana tace.
“Ohhh Mukam munga ta kanmu wannan al'amari wacce irin Musifa da fitinace ta Kunno mana kai”.
Kafin Hajiya Bunayya tace wani abu Asiya ta fito daga cikin Bedroom ɗin ta kana ta zauna gefen su tare da girgiza kanta sai kuma ta kallesu ahankali ta sunkuyar da kanta Idanunta na cika da ruwan hawaye murya cike da rauni tace.
“Umma ku koma ga Allah ku nemi gafarar waɗanda kuka cutar sai kuga Allah ya kawo muku sauƙi wannan ishara ne Ubangiji yai muku Allah ya soku da Rahma ne daya kama ku tunda ranku baku mutu ba dan haka kunemi yafiyar wa'anda kuka cutar tun kafin lokaci ya ƙure muku”.
Kallonta suke tunda ta fara magana har ta dasa aya basu katse taba kamar yadda suka sqba.
Karo na farko a rayuwar su da suka ji jikinsu ya mutu akan abinda suke aikatawa kana kalaman ta ya ratsa su.
Ganin yanda jikinsu yayi sanyi alamar nadama tare dasu yasa cike da girmamawa matsayinsu na iyaye taci gaba dayi musu nasiyya mai ratsa jiki kana ta nuna musu kuskuren su da basu shawarar su nemi gafarar waɗanda suka cutar kana su nemi yafiyar Allah da yardarsa...
Morocco bangaren Khausar sosai al'amura ke tafiya yau ya kama Auren Asma'u da Dr Jameel saura mako biyu haka Auren Asiya da Zakariyya da kuma Yah Aliyu da Dija saura mako biyu Cif-cif sukuma a shirye-shiryen su saura Mako ɗaya su tafi Nigeria.
Ahankali ta ɗaga kanta tare da zubawa ƙofar falonta Ido jin sanyayyan kamshin turaren Moddibo wanda da alama ya dade da dawowa harma ya shiga side ɗin sa yayi wanka kai tsaye gefenta ya nufa ya ya kwanta kana ya ɗaura kansa kan cinyarta kasancewar tana kan 3sitter sai kuma yasa hannunsa ya shafa cikinta kafin ahankali ya maida hannunsa kan cikinta yace.
“Baby ya kake kana lafiya?”.
Murmushi Khausar tayi amma bata ce komai ba.
Sake manna kansa da cikin yayi tare da cewa.
“Meimei ta baka abinci Kaci?”.
Still shiru tayi sai kuma ya ɗago ya kalleta tare da cewa.
“Kinci abinci ko?”.
Kai ta gyaɗa masa tare da faɗin.
“Eh wallahi da gaske naci”.
Cikin tsira mata idanu yace.
“Da gaske?,Me kika ci?”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Nayi wainar Fulawa kuma naci guda uku”.
Kai ya jinjina tare da faɗin.
“Masha Allah Alhamdulillah haka yayi kyau ai naga cikin ya ɗan tashi”.
A hankali ta ɗan ɗaura hannunta bisa sajenshi tana shafawa a hankali tace.
“Yau ina ka tafi tunda safe baka dawo ba”.
Saman hannunta ya shafa tare da cewa.
“Mun fita ne da Dr Jameel da Zakariyya kinsa ya dawo tun shekaran jiya sunje sun nuna min gidansu an tsara musu komai masha Allah.
Dan su bikin saura kwana goma ma zasuyi gaba”.
Cikin sauri ta kallesa sai kuma ta langwaɓar da kai tace.
”Toh muma mu tafi dasu mana Yah Mu'allim”.
Kai ya girgiza tare da faɗin.
”Tafiyarsu da ban tamu da ban”.
Sake marairaice murya tayi tace.
“Allah mu tafi dasu na ƙagu naga Raudat nayi kewar Momyna sosai”.
Cikin kwantar mata da hankali yace.
“In sha Allah zakije ki ganta”.
Kallonsa tayi sai kuma ta make kafaɗa tace.
“Ni dai wallahi da zamu tafi tare nafi so".
Yana gyara kwanciyarsa yace.
“Suɗin ma ina ga zance su haƙura kawai mu tafi tare, tunda saura sati ɗaya zamu je gwara su haƙura mu tafi”.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.
“Toh Allah yasa su haƙura mu tafi".
“Ameen”.
Sai kuma yayi saurin miƙewa daga jikinta jin wayarsa na ruri ɗagawa yayi ta kalli screen ɗin, sunan Sheikh Jabeer ya bayyana da murmushi afuskarsa ya dauka tare da cewa.
“Kaka”.
Daga ɗaya bangaren Sheikh Jabeer dake zaune cikin falonsa A'ish ɗin sa na zaune gefe ya saki murmushi tare da cewa.
“Na'am Jikalle Barka da yamma”.
Moddibo na gyarawa Khausar zama ajikinsa yace.
“Barka dai ya gida?".
Ahankali Sheykh yace.
“Lafiya lau”.
Ya ƙare mgnar yana gyara zama yace.
“Kwanaki munyi magana da kai akan ɓatan Jameel da plate number motar ɗin da muke magana akai?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin.
“Hakane”.
Anutse Sheikh Jabeer yace.
“Masha Allah idan ban manta ba cikin mutanenku akwai wacce tasan number motocin da ake zargin suna yawan binbiyarku gab da ɓacewan Jameel ”.
Kai Moddibo ya jinjina yana mai tuno J dinsa yace.
“Eh Khausar ce ma ”.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya Sheikh Jabeer ya gyara zamansa tare da faɗin.
“Toh ba matsala idan har yanzu tana riƙe da number ka turo min saboda akwai ƙungiyar da Tabital Fulani suka kama a Taraba.
Wanda an kamasu da motoci tawaga guda kusan guda goma wanda gaskiya muke zaton motoci ne da suke harkan Kidnapping dasu saboda a dokar adaji aka kama su da kuma makamai kana da tarin kuɗaɗe".
Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.
“Toh shikenan In sha Allah bari muyi maganar da ita”.
Bayan ya katse wayar ya maida kallonsa gare ta ahankali ya riƙe hannayenta cikin nasa cikin natsuwa ta zuba masa ido.
Cikin fesar da numfashi yace.
“Minha batun number motar nan da Asma'u tace kin riƙe,har yanzu kina