Showing 36001 words to 39000 words out of 281271 words
haka ba.
“To me zan mata?”
Ya tambayi kamshi kamar wanda zuciyar take tsaye a gabansa, yana shinshina rigarsa wani karni yake ji duk da kasancewar Waira bata matsa kusa da shi ba, be ma taba ta ba. Yadda zai fita daga dajin ne abun da ya fara zuwa a masa a rai, ya san tafiyar da yayi a motar kamin ya iso a nan a tafiya mai nisa da mota ma balle kuma yace zai tafi kasa, ina ma zai iya? Idan kuma ya dauki motar nan ai ba shi da zuciya ma, to ya zai yi? Gashi ba shi da waya balle ya kira wani, idan ma ya kira waye zai zo? A KT yake fa ba Katsina ba!
“Ya ilahi?”
Cikin daga murya ya fadi haka yana runtse idonsa ya bude, kamar ya kashe kansa haka ya rika ji saboda takaici, a dayan bangaren kuma Waira ta cika dajin da ihun da take yi gwanin tausayi. Sanin dole motar zai dauka ya fita da ita dajin ya saka ransa ya kara ba ci. Kamar ana kiransa haka ya rika ji har ya karasa nesa da inda Waira take kwance tana mulmula da kasa ta rike hannu har wani shidewa take kamar zata mutu. Daker ya cira kafarsa ya dan kara matsawa, sai kuma ya daga kai ya kara karewa gurin kallo, daji da za a iya samun abubuwa masu cutarwa kamar yadda zai yi wahala wani ya shigo gurin balle ya kawo musu dauki.
Ya dawo da dubansa gurinta har yanzu mamakin inda ta fito yake, kalar tufafinta da kazantar dake jikinta, akwai gari kusa da dajin ne ko kuma dai wani ya kawo ta a gurin ko kuma gudowa ta yi? Yana ta jera ma kansa tambayoyin da ba shi da amsar su, a zuwa yanzu kam zuciyarsa ta fara raya masa cewar ba aljana ba ce. Cikin wani yanayi mai kama da bata san tana yi ba ta mika masa hannunta mai ciwon tana jin kamar ya taba azabar ciwon da take ji a yanzu ta bace lokaci daya. Tsaye yayi yana kallonta ya san zafin cizon maciji ba karamin abu ba ne ko da kuwa be taba cizonsa ba ya ji labarin azabar da ake ji, tun tana mika masa hannu har hannu ya fadi idanuwanta suka fara rufewa tana numfashi daker gashinta ya tara gumi, hawayen idonta sun wanke fuskarta sai suka hadu da datti dake jikinta suka yi mata jurwaye.
Be yi unkurin yi mata komai ba har sai da ta suma, sannan yaja tsaki wata zuciyar na raya masa ya koma ya duba halin da mahaifinsa yake ciki, ba mamaki gaskiya Nimra take fada masa ya san yadda mahaifinsa yake sonsa idan aka ce wani abu ya same mahaifinsa be kamata ya musa ba, domin korar da yayi masa zata iya taba shi. Idan har akwai abun da Ameer yake kauna a duniya to yana a bayan Mahaifinsa ne, sai dai gata da tarin arzikin da ake sakar masa ya saka baya iya tsayar da fushinsa ko da kuwa a gurin mahaifinsa ne. Wani tunanin ne ya zo masa a take ya juya ya nufi inda carpet dinsa da ya shimfida yake ya cire rigar jikinsa ya nade hannunsa sannan ya janyo carpet din har cikin ciyayin da Waira take kwance wani kumfa ya zubo ta gefen bakinta dake bude. Kafasar ya saka ya rika turara ganin ba zai samu abun da yake so ba a dole ya saka hannunsa daya nade ya daga ta ya dora yana ta wani kyankyami, a cikin carpet din ya hade ta kamar wata gawa yana ta tofar da yawu, cikinsa sai wani kuka yake saboda kazantar da yake ji numfashinsa jin yayi kamar ya canja. Fita yayi a gurin ya taka har gurin motarsa yana kara waige waige ko Allah zai saka ya samu wanda zai bawa ita ko kuma ya taimaka masa ya saka mata ita mota, domin shi dai be jin zai iya taba wannan uban dattin duniyar dake jikinta even though ya nadeta a carpet da yake da tabbacin idan ya isa gida sai ya wanke hannunsa ya fi a kirga. Ganin kamar zai bata lokaci ya guri ya saka shi juyawa ya koma a samu gafen rigar dake nade a dayan hannunsa ya nade dayan ya dauketa yana kawar da fuska, gurin motar Nimra ya nufa, a dole sai da ya aje ta sannan ya bude bayan motar ya saka.
“This one is for you Nimra ina fatar yarinyar ta mutu”
Har wani daga gira daya yake, ko kadan baya jin komai a jikinsa sai ketar da yake ta sakawa, jefar da rigar hannunsa yayi ya bude motar ya shiga be saka kafafuwansa ba sai da ya cire talkamin kafarsa ya shiga motar haka, daga shi sai wando jean jikinsa ba riga sai farar fatar jikinsa da kuma mazanta dake kara fitar da zatin fuskarsa. Kunna motar yayi at first sai ta tashi sai da ya yunkura zai yi reverse sai ta tsaya, ya sake kunna ta mutu ya sake kunna ta sake mutuwa har sau hudu, jimmm yayi yana tunanin yadda rayuwa zata kasance masa idan motar nan bata tashi ba, ba zai yi mamaki ba idan ta ki tashi domin ya ci uban motar, yadda ya rika buga motar da icen dake gurin sai da gabanta ya lankwashe, abun da be saba ba sai gashi yana addu'a da fatan Allah yasa ta tashi. And he got lucky motar ta tashi abun yayi hamdala ga Allah sai gashi yana fito ya juya kanta da karfi ya koma hanyar da shigo da motar yana gudu sosai kamar an biyo shi. Babu inda ya nufa sai hanyar da zata sada shi da Abuja, tunanin yadda zai yi idan police ko sojoji suka tare shi a hanya be zo masa ba sai yanzu.
EID POV.
Yana tsaye bakin kofar dakin da Waira take yana kallon cikin dakinta dake hargitse, he felt very bad domin shi ne silar guduwarta a garin, guduwar da bashi da tabbacin Sarki zai yafe mata ko kuma ya kasheta kamar yadda ya alkawaranta.
“Waira duk saboda kar ki yi kewa babu ranar da bana kasancewa tare da ke, miyasa zaki tsorata har haka? Akan me zaki karya dokar dake nufin rayuwarki?”
Ya kai hannu ya taba kofar dakin, kamin ya sulale kasa ya zauna a hankali, tun da ta tafi kullum a gurin yake zama, idan baya dakinta to yana a gurin da ta saba zama ta ci yayan itatuwa, ko kadan baya son yayi tsafi ya ga halin da take ciki domin zuciya zata iya debarsa ya bi bayanta bayan kuma Sarki ya kafa masa doka tun a ranar da ta gudu cewar kar ya bi bayanta. Ya daurewa zuciyarsa ya bi Umarni Sarki na iya yanzu da zuciyarsa zata iya dauka, kamin ya shawo kan Sarki ya sassauta hukuncin da zartarwa Waira tun gabanin ya san zata gudu. Wani irin azaba ya ji hannunsa na yi kamar an jefa shi a ruwan zafi, an cire na kara a wuta, da sauri ya saka dayan hannunsa ya rike dayan da yayi masa mugun nauyi dafin na shiga har wuce iya inda zugin yake. Iyakar juriya yayi amman sai da ya kai kwance yana dafe da hannu tsabar azabar da ya ji hannun na masa, yanayin yadda gurin ke masa zafi dafin na masa yawo ya gane cewar maciji ne ya cizi Waira, mikewa yayi tsaye rike da hannu ya daga kansa sama ya lumtse ido. Sai ga wahala masu zafi sun sauko masa, ba Hawaye ne na kukan zafin da yake ji ba na cizon maciji ba, hawayen tausayin Waira yake a wane hali take ciki? Ta ina maciji ya cijeta? Daman tun da ta gudu babu ranar da ba ya tunanin halin da take ciki da kuma abun da zata ci, ko a ina ta boya, duk be sani ba kuma bashi bukatar ya sani a yanzu.
“Waira”
Ya fada yana jin azabar tana karuwa, har yawun bakinsa sun soma canjawa, gumin azaba da wahala na karyo masa a goshi har ya rasa inda zai saka kanshi. Lokaci daya kuma sai ya ji azabar ta dauke masa.
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2023
_©Khadeeja Candy_
1️⃣3️⃣
Wani sabon tunanin ne ya zo masa hakan ya saka shi canja shawara, gefen hanya ya rika bi har ya samu wani Karamin shagon siyar da kaya, wani almajiri ya samu ya aika shi kiran mai shagon kasancewar akwai glass sai an bude za a shiga, ba shigar ce matsala ba rashin talkami da kuma rigar jikinsa ce matsala domin baya son ayi masa kallon mahaukaci. Almajirin na isa sai gaai shagon ya fito ya biyo bayansa. Tun kan ya isa Ameer ke masa kallon kasa da sama.
“Riga nake so wacce ta fi ko wace tsada, sai talkami idan kuna da su”
Shi ne abun da ya fada ya mika masa Atm din hannunsa tare da fada masa code.
“Akwai amman ba mu da machine din cire kudin, sai dai makocina shi kuma sai ya cire carjin dinshi”
“Ba matsala”
Ya fada ba tare da ya kalleshi ba, domin mutane kazanta suke ba shi a yanzu, Waira ma dake bayan motar jin yake kamar tana saman jikinta ne, kazantar dake jikinta ta lake masa a zuciya ya kasa manta abun da ya gani. Yana ji yana gani ya bata minti talatin a gurin kamin mutumen dake shakar Ameer ya kawo masa rigar da talkamin, domin jikinsa na bashi ba Ameer ba mutumen kwarai ba ne ganin sabuwar mota da aka buge gabanta gashi babu riga a jikinsa kuma babu talkami hakan na nuna sato motar yayi ko kuma wani abun dabam. Kallo daya Ameer yayi ma rigar da talkamin ya san ba ajinsa ba ne, sai dai babu yadda zai yi dole ya saka a haka, sai da yayi tsaki sannan ya karba tare da ATM din, a gaban mutumen ya saka rigar sannan ya ja motar yayi gaba, tafiya mai nisa yayi sannan ya saka talkamin ya faka motar gafen titi ya fita zuwa gurin wani mai shagon POS ya mika masa ATM din.
“300k nake so”
“Ranka ya dade ba za su samu ba, sai zuwa anjima sai dai 100+ idan kana so”
“Ba ni”
Mutumen ya fara aikin saka ATM din, dayan dake taya shi aiki kuma ya fara karga kudin, fuska babu annuri Ameer ke fada musu pin din, in less than 20min aka ciro kudin aka bashi ya karba, be damu da saka su aljihu ba ya riko su a hannu domin sun masa kazanta kasancewarsu tsofin kudi wasu ma sun yage sa'arsa daya sun saka masa su a leda. Bude motar yayi ya shiga ya dauki hanyar Kano sai da ya kusa isa gurin da police ke bada Hannu sai ya samu guri gefen titi ya faka motar inda ba za su hango shi ba, ya fita ya zagaya bayan motar da ya bude ya saka hannunsa ya warware nadin da yayi mata da carpet fuskarta ta fito, hakan nan ya samu kansa da tsaya yana kallon yadda hawaye suka bushe a fuskarta ga gashin kanta ya kara yamutsewa, abun ka da marar juriya sai amai ya sake cika masa baki da sauri yaja baya ya fara kwara amam dake fitowa daker domin babu komai a cikinsa sai yunwa, ya amayar da dan abun da ya ci jiya, gashi yau be saka komai a cikinsa ba. Cikin motar ya koma ya dauko gorar ruwa ya wanke bakinsa da fuskarsa, after that ya tuna ya taba abubuwa da yawa da be kamata hannunsa ya kai a fuskarsa ba tare da ya wanke ba.
“Ohhhhhh”
Ya furta yana jin wani irin bakin ciki, a sake ya bar motar kamar yadda ya bar bayan motar ma a bude, ya dauki kudin dake ledar ya bar ATM din da komai a ciki, ya fito daga gurin zuwa gurin babban titi tafiya yayi mai nisa a kafa sannan ya tsallaka dayan side din da zai maida shi cikin KT yana tafiya yana taron mota har ya samu wanda bata da mutane da yawa ta tsaya, one after the other ya rika bin mutun biyu da suke bayan motar da kallo kamin ya kalli direba da yake ganin idan ya shiga motar kamin su isa KT ma mutuwa zai yi, domin irin motar nan ce da bata da Ac glass din motar ma a harfice yake balle kuma mutanen ciki.
“Ku tafi kawai”
Bayan ya gama bata musu lokaci, be tsaya jin abin da za su fada ba yayi gaba abunsa, can kuma ya sake taron wata motar, yayi haka ya kai sau biyar sannan ya samu wanda mutun biyu ne kawai a gaban motar bayan babu kowa, sai dai ita ma bata da Ac kuma motar kasuwace irin mai rawa din nan idan ana tukawa, hakan na dai ya daure ya shiga yana jin wani zazzabin wahala na taso masa, tasha ya fada masa za su kai shi he can pay ko bawa suke so shi dai bukatarsa ya ganshi a tasha.
Kamar yadda ya bukata haka suka kai shi har cikin tashar KT suka ce zai ba su 3k saboda lura da suka yi da alamar yana da su, ba musu ya bude ledar ya cire kudin da za su fi haka ya mika musu, sannan ya saka ragowar kudin aljihun wandonsa guda biyu ya bude motar ya fita.
‘What if wanda ya san shi ya ganshi a nan? Wannan ai zai zame masa abun kaskanci’
Shi ne abun da ya fara zuwa masa a rai, hakan ya saka shi nufar wani mai tereda dake siyar da facing cap ya siya ya saka ya siya bakin glass ya saka ya rufe idonsa. Sannan ya nufi gurin da yan union suke da su ya fara magana ya fada musu shatar mota mai kyau zuwa Kano, ya fadi inda za'a kai shi bayan yayi musu karyar motarsa ta lalace kuma tafiyar gaggawa ta kama shi, tun da yake a rayuwarsa be taba sanin haka tasha take a yamutse da mutane ga hayaniyar da yake ganin da ace shi da tuni ya kurmance, duk wani information na shi sai da suka karba sannan suka hada shi da direban da zai kaishi Kano, ba laifi ya samu mota mai dan kyau domin tsab take matsalar kawai bata da Ac, ba su bar gurin ba sai da ya siye lemu cake tare da ruwa da dan biscuits sannan suka kama hanya, direban ya tsaya ya sha mai a gidan mai dake hanyar fita KT sannan suka kama hanya. Kamin su isa Kano Ameer yayi amai ya kai sau hudu saboda warin man motar da yake ciki yana damunsa.
Kwanta yayi jikin motar yayi relaxing yana tunanin mahaifinsa, wannan kadai ya isa ya fahimci cewar mahaifinsa yayi masa gata, domin be san duk wannan wahalar ba, idan zai yi tafiya kamin time din tafiyar yayi an shirya masa komai, sannan jirgi yake hawa ba mota ba, sai idan zai isa Airport ko kuma daga Airport zuwa gida ne kawai yake hawan mota sai kuma yawon cikin gari, motar ma sai wanda ta amsa sunan motar da ba kowa ya isa ya hau ba, ya kwanta a gado mai kyau gida mai kyau tufafi baya saka mai karamin kudi, kudin Naija ma idan ba ganin dama ba ba zai rike ba sai Dollars kuma babu mai ce masa dan me? Wani lokacin ma a private jet ma za a kai shi inda yake so na mahaifinsa , tun da yake a rayuwarsa be taba hawa motar haya zuwa wani gurin ba sai a yau. Sai a yanzu yake jin be kamata ya bijirewa umarnin mahaifinsa ba, mi zai saka yayi haka? Why? Gashi makiyinsa ya samu yadda yake so bayan raba shi da abokansa, ya busar da iskar bakinsa ya dago kadan yana kallon hanya sosai yake son yin bachi amman ya kasa saboda babu ac a motar kuma iskar dake shigowa ta gilashin motar yayi masa yawa, abu ne da be saba da saba da shi ba. Haka dai ya daure har suka isa kano. GRA suka shiga direban be sauke shi ko'ina ba sai cikin gidan Hajiya Jamila. Yana fitowa motar ya ciro kudin aljihunsa gaba daya ya mikawa direban.
“Ka kara da wannan”
A firgice direban ya fito daga cikin motar gaba daya ya zagayo inda Ameer yake tsaye ya fadi kasa ya rike kafafuwansa yana masa godiya har da hawayensa, shi kansa Ameer ba zai fadi ko nawa ne kudin ba, balle kuma wanda aka bawa kyautar domin babu wanda ya kirga a cikinsu, sai dai ganin yan 1k da yawa ya san kudi ne mai yawa.
“Ba wani kudi ba ne fa”
Ameer ya fada domin ba ga wani abun godiya da mutumen zai masa ba, akan abun da be taka kara ba balle har ya karya.
“A gurinka ba komai ba ne ranka ya dade, amman ni a gurina kudi ne mai yawa, da tsoro na kawo ka Kano ashe ban sani ba rabo ke kirana, motar nan ba tawa ba ce amman ka ga abun da Allah yayi min”
Ameer ya dan ji wani irin for the first time domin yau ne karo na farko da yayi sadaka, not just sadaka wannan ne karo na farko da yayi ma wani abun kirki kuma har aka masa godiya, this is the first time da ya kyautataw wani. Tabe baki kawai yayi ya nufi cikin gidan da harabarsa ma ta ishe talaka da wani bakauye kallo domin kana ganin gidan ka san Ameer ya isa har ya wuce, a tunanin direban gidansu Ameer ne, shi kuma ya zabi zuwa Kano ne saboda ba zai iya jure tafiya a Abuja a motar haya da babu ac ba, kudin dake aljihunsa ma ya bashi kyautar su ne saboda baya jin zai sake taba kudi mai datti again, daman ya matsu su fita aljihunsa sai yake jin kamar tsukarsa suke.
This is the second reason da yake son zuwa gurin Hajiya Jamila kullum kofar falonta a bude take not like gidansu da sai