Showing 174001 words to 177000 words out of 281271 words
ta kalli dan karamin akwaitin dake back seat ta kalli Ameer da ke juya kan motar ta ce.
“Sukenan kayan da zaka dauka daman?”
“Eh ai ba tufafi zan dauka ba, wasu abubuwan da nake son amfani da su zan dauka, idan mun je gida zan yi Order sabon tufafin da duk wani abu da zan yi amfanin da shi sai a kai min a can”
“Okay kana da kudi shiyasa amman kana aiki ko?”
“Aa bana aiki, ni zan zaman banza ne, shiyasa nake son zama a gurin Ummi saboda na samu kudin”
Ya fada yana murmushi da yafi kama da dariya saboda fitar sautin murmushin.
“Ummi zata baka mai yawa kuwa bata da rowa, tana da yawan kyauta”
“Haka addininmu ya koyar da mu....”
Muhimmanci kyauta da sadaka yayi ta fada mata, da kuma falalarsa har suka isa gidan Ummi. Kamin su shiga gidan gabanta ya soma faduwa tunawa da Maleek da ta yi. Horn yayi aka bude masa gate ya shiga ya faka a compound din gidan, Fiyya ta faka a gefensa tana karewa harabar gidan kallo daga cikin motar da take zaune. Maleek na zaune a one of set din kujerun da suke Entrance din rike da waya hannu, yana sanye da kananan kaya mug a center table. Kallo daya ya yi ma motarsu ya dauke ido be sake kallon inda suke ba, har iso gurin Ameer ya bude ma Waira kofar falon ta shiga tana matsar hannu kasa kasa take satar kallon Maleek har ta shiga, sannan shi ma ya shiga. Fiyya ta iso gurin tana kallon Maleek da be san ma da wanzuwarta a duniya ba, kallonsa kawai take har ta isa bakin kofar falon, kyaun nan nasa mai daukar hankali da kuma kamshin turarensa mai jan hankali ya hana ta wuce ba tare da mika masa gaisuwa ba.
“Sannu ina wuni”
Ya dago ya kalleta daga sama har kasa ba tare da amsa ba, ya maida kansa kasa ya cigaba da abun da yake. Ta dan bude ido.
“Shi kuma haka yake?”
Ta fada murya kasa kasa sannan ta tura kofar falon ta shiga da sallama Ummi ta dago tana amsa mata fuskarta da annashuwa.
“Lale marhabun da zuwa”
Ameer ya kalli Waira dake nunawa Ummi perfume din da Mummy ta bata ya ce.
“Waira kin san ma'anar Sallamu Alaikum da kuma Wa'alaikassalam?”
“Aa me yake nufi?”
“Peace be upon you, Wa'alaikussalam kuma peace be upon you too”
“To meyasa ake cewa haka?”
Ameer be amsa mata ba ya kalli Ummi ya ce.
“Ummi duk tsawon zaman da ta yi a gidan nan ne bata san komai akan addinin musulunci ba? Baki zaunar da ita kin fada mata matsayi da martaba ta addinin musulunci ba, da irin aminci da natsuwar da yake da shi?”
Kalmar Ummi da Ameer ya kira Ummi da ita tafi komai yi mata dadi, ba yau ne karon farko da ya taba kiran sunan ba, sai dai a yau ne ya fara kiran sunan cikin girmama sa karamci, ya kirata kai tsaye kamar yadda sauran yayanta suke kiranta sai kuma ya dora da bayanin abun da ya kara mata kaunarsa wato son addinin da kokarin ganin Waira ta koya.
“Ni uwace ina da abubuwa da yawa a gabana, shiyasa ban maida hankali akan haka ba”
“Cika uwa yana nufin kula da yaya har ta bangaren addininsu, nauyin Waira yana kanki a yanzu kamar yadda kika fada”
“Yana kam mu gaba daya”
Ta gyara masa zancensa na karshen, sannan ta kalli Fiyya ta ce.
“Ya Mamanki take?”
“Lafiya kalau, tace a gaisheki”
“Ina amsawa, Ameer na gyara maka dakinka da kaina, amman ban sani ba ko akwai abun da ba zai burgeka ba, zaka iya min magana a gyara”
“Bari na duba”
“Waira wuce ki kaishi dakin dake kusa da nawa”
Waira ta wuce gaba Ameer ya bi bayanta Fiyya ma ta rufa musu baya. Sun dauki lokaci a dakin yana duba abubuwa, be dauka sabon furniture Ummi zata zuba masa ba, amman ga mamakinsa sai ya ga har tawul da bathrobe duk sabin Ummi ta aje masa, hakan kuma ba karamin faranta ransa yayi ba. Ya sauko yana magana da Fiyya yayinda aka bar Waira a dakin tana kara duba wasu abubuwan.
“Ummi za a samu direban da zai kaita gida yanzu? Bana son na sake driving sai gobe idan zan fita duba Kakarsu Humairah daga nan na wuce office”
“Eh za a samu wanda zai kaita mana, drivers dai sun tafi gida yanzu amman Maleek ma zai iya sauketa”
Da gangan Ameer yayi murmushi saboda ya san waye Maleek ya san abun da yake soda kuma wanda baya so.
“Okay ki masa magana ya sauke ta, ga key din motarki na dauko tawa”
Ya mikawa Ummi sai ta karba cikin jindadi da farinciki marar misaltuwa. Sannan ta nufi wani karamin side table dake tsakanin kujerun falon ta dauki wayarta.
“Lemme call him”
Ta fara kiran Maleek tana fadar.
“Gobe tare zamu tafi na duba matar, sai na dawo kai kuma ka wuce gurin aikinka”
Ameer be ce mata komai ba, har Maleek ya amsa wayar.
“Hello”
“Maleek kana ina?”
Ta dayan bangaren Maleek ya juyawa ya kalli hagu da daman inda yake sannan ya amsa mata
“Entrance”
“Please zaka sauke...”
Ummi ta za last sentence din tana kallon Fiyya har sai da ta furta sunanta.
“Safiyya”
“Yauwa Safiyya gidansu”
Maleek yana daya daga cikin irin yaran nan da basa son musawa iyayensu wani umarni da suka musu, biyayya ce kawai zata saka ya yarda ya kai yarinyar gida domin ya gane wanda ta zo tare da Ameer Ummi take nufi, ba kuma dan ya san sunanta ba sai dan sanin ita kadaice bakuwa a gidan, wata kila ma Ameer ne zai saka Ummi ta bukaci ya kai yarinyar gida.
“Okay”
Ya amsa sannan ya sauke wayar zuciyarsa na mugun ƙuna, zafi kirjinsa yake masa ga bacin rai da be san na minene ba, ya busar da iskar bakinsa ya jingina jikin kujerar for some seconds sannan ya mike tsaye tare da mug din ya shiga falon, shigarsa ta yi daidai da saukowar Waira dake fadin.
“Dakin yayi kyau Ummi komai ya ji”
Kallon kawai yayi ya kawar da idonsa, yana kokarin danne abun da yake ji na bacin rai a zuciyarsa, to me zai saka ma ya damu bayan ya san ya daukarwa kansa alkawari ba zai sake damuwa da duk wani abu da zai shiga tsakaninta da Ameer ba.
“Lemme get my keys ta jira ni waje”
Yana fadar hakan ya nufi stairs, Ummi ta kalli Fiyya tana murmushi ta ce.
“Ki jira shi a waje zai zo ya kai ki yanzu nan”
“Toh na gode, sai da safenku”
Ta musu sallama ta fice, Ameer ya haur sama ya shiga dakinsa domin yin wanka, Waira kuma ta zauna a kusa da Ummi ta aje wayarta tana kallon Ummi wanda ta nufi kitchen. Maleek be dade ba ya sauko rike da keys din a lokacin Waira ce kawai zaune a falon tana ganinsa ta sha jinin jikinta ta sauke kai kasa. Yana saukowa gabanta na faduwa har ya iso inda take zaune, tsayawa yayi yana kallonta har ya bude baki yayi magana sai wata zuciyar ta tuna masa da alkawarin da ya dauka. Jin yana tsaye a kanta ya saka ta dago kanta ta kalleshi da idanuwanta masu daukar hankali, raunin dake cikin idonta ya baibaiye fuskarta ya dira zuciyar Maleek a madadin ya ji haushinta sai tausayinta ya dirar masa.
“Oh Ya Rabbi”
Kawai tausayinta yake, zuciyarta ta kasa natsuwa da alakar dake shiga tsakaninta da Ameer, ta dayan bangaren kuma yana jin damuwa ganinta da Ameer. Numfashi yaja ya sauke da karfi sannan ya dauke kai ya fice daga falon.
[7/18, 10:14 PM] My S Line: 57
Da hannu yayi ma Fiyya alama da ta shiga motar da yake nufota, sai ta isa gurin taja ta tsaya kwarjininsa na cikata, har sai da ya shiga motar sannan ta bude ta shiga. Ta natsu sosai fiye da yadda ta saba natsuwa idan tana tafiya da mutumen da bata sani ba, kwararran motsi sai ta kasa yi, tana son ya juya ta kalli inda yake ta kasa, daga ita har shi hankalinsu yana gurin titi har ya isa bakin gate din gidan. Son ya tabbatar ta sauka lafiya ya saka shi yin horn aka bude masa gate ya shiga har ciki ya faka motar harabar dake kusa da kofar falon, sai a lokacin ta samu damar kallonsa shi ma kuma saboda ta yi masa godiya ne.
“Thank you”
Be kawota arajin kansa ba, dan haka ba godiyarsa ce abun da yake bukata a gurinta ba a yanzu. Ko kallon inda take be yi ba balle ma ya amsa tana fita motar yayi gaba a makeken compound din gidan ya juya motarsa ya fice. Da gangan ya yi ta tafiyar da zata dauke shi lokaci be dawo gida ba, and he don't know why. Bayan kusan awa daya da rabi a titi finally ya iso bakin gate din gidansu yayi horn masu gadi suka bude masa gate. To his surprise sai ya samu Abiey tsaye yana lasa wayarsa hannunsa. Maleek na fakawa ya bude motar ya fito yana matsa key din hannunsa ya nufi gurin mahaifinsa.
“Abiey lafiya?”
Abiey ya dago ya kalleshi a karo na biyu bayan kallon da yayi masa a lokacin da yake shigowa cikin gidan.
“Me ka gani?”
“Kawai dai na ga kamar ba lafiya ba, fuskarka ta nuna akwai damuwa”
Abiey yaja dogon numfashi ya sauke.
“Damuwar gidan nan ba zata wuce ta mahaifiyarku ba...”
Kamin Abiey ya kai aya Maleek yayi karaf ya karbe yana juyawa ya jera tare da Abiey.
“Zuwan Ameer gidan nan ko? Ni ma bana son haka, sai kuma na kyale ne kawai saboda Ummi ta samu natsuwa da kwanciyar hankali, amman ina jin tsoron kar Ameer ya sake sakata cikin tashin hankali wata kila ba saboda kwanciyar hankalinta ya dawo, zai iya amfani da Waira ya cimma wsni burinsa ne sannan ya jefar da ita, na nunawa Ummi haka amman ta kasa fahimta sai kokarin ganin laifina take, alakarsa da Waira tana kokarin wuce gona da iri, ita bata da hankali da wayon da zata gane”
Abiey ya sauke wayar da yake latsa gaba daya yana kallon dansa da mamaki, domin Maleek ya bude cikinsa ne ba tare da ya sani ba, shi dai kawai yana neman abokin tattaunawa ne.
“A cikin zaman Ameer a gidan nan da kuma alakarsa da Waira wanne ya fi kona maka rai?”
Kai tsaye ya amsa.
“Alakarsa da Waira mana Abiey, gida ai yana da hakkin zama saboda ka amince masa kuma mahaifiyarsa tana ciki, amman miya kawo issues din Waira a ciki? Why her? Idan ya lalata mata rayuwa fa? Na nunawa Ummi haka amman ta kasa ganewa, ina tausayin yarinyar nan Abiey tausayi take ba ni, bana son alakar dake shiga tsakaninta da Ameer, kawai dai ina dauke idona ne a yanzu saboda Ummi ta bukaci haka, but still ina jin kamar ba zan iya jurewa ba”
Maleek ya karashe maganar har wani furzar da numfashi yake saboda abun da yake ji a zuciyarsa. Da mugun mamaki da kuma tunani kala kala Abiey ke kallon dansa, this is the first time da ya zama mutum kamar kowa, yake jin kishi akan wani abu da ada can baya damunsa, wani abu da be taba samu muhalli a rayuwarsa ba. Ya dade da ganin canji a rayuwarsa ďansa, sai dai canjin ba irin wannan ba, abun da matarsa Zahra ta dade tana mafarkin faruwarsa da kuma tana jiran zuwansa.
“Kana jin ba dadi idan ka ganshi tare da ita right?”
“Yes kawai ina controlling kaina ne, if not Wallahi ko duka zan iya masa”
Abiey yayi murmushi yana jin dadin a ransa, hannunsa daya ya kai yana bubbuga kafadar Maleek.
“Karka damu, zan daukar masa mataki, ba zamu bari ya lalata rayuwar yarinya karama ba, kuma ya kamata mu maida hankali mu san waye iyayenta ko dan gaba”
Maleek ya sauke numfashi yana kallon wani gurin na dabam.
“Haka ne, amman dai for now kamata yayi mata ace ka yi duk wani abu da zai yanke hulda tsakaninsu, if ba haka ba shakuwa zata shiga kuma zai iya amfani da wannan damar ya cutar da ita”
“Haka ne, karka damu na san abun da zan yi, amman kai ma ya kamata ka rika kyautata mata, ka rika sake mata tana jin sanyinka, ita tunanin yana amfani da weakness dinta ne ya yana janta a jikinsa”
“No ni ba zan iya haka ba, ai sai ta raina ni, kuma na fi damuwa da alakarsu da Ameer ba wai dole sai ta saki jiki da ni ba”
Abiey yayi murmushi
“Ba zaka gane ba Maleek. Apart from wayar da ka tarar ina yi a yanzu ina magana da Doctor Hassan ya fada min abubuwan da ya kamata ace mahaifiyarka tana yi saboda lafiyarta amman taki, ban san yadda zan yi convince dinta ta yarda ba, musamman a yanzuda Ameer ya dawo gidan nan”
Abiey ya tattauna da shi akan abubuwa da yawa suka shafi Ummi, sai kusan ten Abiey ya shiga bangarensa Maleek kuma ya nufo bangaren Ummi. Yana shiga falon Waira ya fara cin karo da ita kwance a kujerar daya barta, sai dai wannan karon tana rumgume da zomonta ne, sai sharbar Bacci take kamar wacce ta yi wani aiki ta gaji. Tsaye yayi a kanta yana kallon fuskarta, bachi ma kyau yake mata kamar yadda idan tana farke take kara kyau da haiba. Wayarsa ya ciro ya shiga instagram for few seconds sannan ya dago kansa ya duba ko'ina na kusuwar falon, ganin shi kadai ne sai Waira ya ba shi kwarin guiwa fitowa daga Insta ya shiga camera ya saita wayar saitin fuskar Waira ya dauke ta hoto har sau biyu sannan ya maida wayar aljihunsa ya kai hannunsa ya buga gefen kujerar sai ta farka a firgice ta kalleshi.
“Tashi ki je daki ki kwanta”
Ta mike tsaye tana wani rangaji kamar zata fadi, hankalinsa sai ya dauku akan karta je hawan stairs ta fadi kasa, dan haka ya bi bayanta be matsake ta daf ba, sai dai damuwa da yayi da karta fadi ta kai kasa ya saka shi tsayawa a space din idan zata fadin ma zai iya tareta, haka ya bita har sai da ta shiga dakinta ya tsaya bakin kofa tana fadawa kan bed ya kashe wutar dakin ya janyo mata kofar a hankali. Dakinsa ya nufa he can't tell why yake damuwa da ita, at first yana tsoron kar Ameer ya bata mata rayuwa ne, yanzu kuma ya gane ba tsoro ba ne kawai har da tausayinta yana yi, na rashin wani gata sai su, bata da family sai su, da ace Ummi zata koreta a yanzu a bata da wani gurin zuwa sai da ta shiga wani hali.
Sai 11pm ya saka tufafin bachinsa sannan ya kashe first switch na dakin, ya kashe bedside lamp yana kokarin kwanta daga zaune da yake sai ya ji kamar akwai mutum a gefensa, ya kai hannunsa ya taba sai ya ji ya taba jikin mutum amman akwai gashi da sanyi sanyi a jiki, da sauri ya kai hannu ya kunna bedside lamp din ya juya be ga kowa ba, ya kai hannu ya taba gurin ya ji babu komai, for the second time ya kashe wutar ya kai hannunsa ya lalaba ko zai sake jin wani abu amman be ji ba. Gaba daya ya kunna wutar dakin ya tashi zaune da kyau yana kallon gadon, be taba jin wani abu makamancin wannan ba gidan gaba daya balle kuma a dakinsa. Ya duba hannunsa ya jimke hannun ya bude yana mamakin me yaji haka? Ya sauko da kafafuwansa kasa ya zauna bakin gadon kamin ya tashi ya nufi bandakinsa alwala yayi ya fito ya sake zama a inda ya zauna dazun ya sake kashe first switch na dakin ya dauki wayarsa dake gefen gadon ya bude qur'ane application dake ciki ya karanta Suratul milk, bayan ya gama yayi addu'ah ya kwanta ba tare da tsoron komai ba. Haka nan kawai bachi yaki daukarsa, jikinsa kuma yaki yi masa dadi daga kwanciyar da yayi, a dole sai da ya tashi ya jigina da kan gadonsa ya dauki wayarsa dan rage dare, sai gashi ya shiga Whatsapp yana duba sakowannin da be shirya amsa sako ko daya ba, ya fito ya leka Instagram ba shi da wani abun yi a gurin dan haka ya fito ya sake komawa Whatsapp, sai dai wannan karon status din mutane yake kallo, kamin ya shiga camera dake status nasa, daman he update a status on whatsapp once in awhile, kara ma Insta ya kan dora hotonsa time to time musamman a lokacin da suke yawan zama tare da abokansa. Yana shiga camera hoton Waira ne first abun da ya fara cin karo da shi domin shi ne last picture da ya sauka a wayar, he can't tell what take him so long zoom the picture yayi ta kallon kamar wani da be taba ganinta ba
*** *** ***
Can cikin bachinta mai nauyi ta ji ana kokarin saka mata hannu a cikin rigar dake jikinta. Yanayin sai yayi mata kamar mafarki take dan haka ta kara gyara kwanciyarta tana sake jiki ba tare da ta sani ba. Hakan be wadatar ba har sai da ta ji ana tashinta daga bachin tare da kiran sunanta da muryar da ta haddace tun farkon zuwanta gidan.
“Waira... Waira... Waira...”
Ta amsa cikin magagin bachi sannan ta bude idon daker, arba da ta yi da fuskar Maleek ya saka ta tashi zaune da sauri tare da buge masa hannunsa dake cikin riga yana kokarin kai wa ga kirjinta.
“Ya Maleek”
Ta fada tana matsawa baya da sauri sai ya haura saman gado da wata kalar fuska shi ba dariya yake ba, kuma ba murmushi ba, ba kuka ba da damuwa ba, haka ma fa far'ar ba ba kuma kishiyarsa bakinciki ba. Still hannunsa yake son kaiwa ya taba kirjinta abun da ba taba mata ba, bata san haramci hakan ko halacci ba, sai dai tana jin abu na wani yanayi na dabam saboda abu ne da bata saba da shi ba, wani be taba kwatanta yi mata haka ba. Sai ta kara matsawa baya taba bata fuska kamar zata yi kuka gashi tsoron take yace ta masa ba daidai