Showing 156001 words to 159000 words out of 281271 words
ya wuce ya fara taka stairs din, bayansa ta bi, sai gashi ya tsaya ya juyo ya kalleta.
“Waye Ummi ta ce ki dauko waya a kira jiya da dare?”
“Malamina”
A take ta kirkiri karya ta fada masa abun da ba halinta ba. Domin bata yin karya mo matter what, a yanzun ma tana tsoron ya ce zai dake ta ne. Be ce mata komai ba ya juya ya haye sama, sannan ita ma ta shiga dakinta. Karfe bakwai da rabi school bus ta faka kofar gidan, sanin lokaci yayi ya saka Waira ta aje kofin tea da take sha ta ta dauki jakarta dake gefenta ta mike tsaye.
“Ummi time yayi”
Ummi ta so daga kujerarta ta matsa kusa da Waira ta sumbancin goshinta.
“Allah ya miki albarka, ga cake din na musamman ne na yi, yayi dadi sosai ki ci da yawa”
“Okay Ummi Thank you”
Ta karbi cake din ta nufi hanyar falo, Ummi kuma ta kalli Mahmood ta ce.
“Please fita ka fadawa driver bus din ba shi zai dawo da ita ba, za a zo a dauke ta ne”
Mahmood Ummi take yi ma magana amman Maleek ne yayi tambaya.
“Waye zai dauke ta?”
Ummi ta kalleshi.
“Ni zan je na dauke ta, ina son na gwada driving ne yau”
Maleek ya juyo yana Waira da Mahmood ya rufa nata baya domin cika umarnin Ummi.
“Ba driver makarantar ke da alhaki ba, principal dinsu ke da alhaki, dole idan za a yi haka, ni ne zan kira na sanar musu ko kuma Abiey”
Ya fada bayan ya juyo da kansa.
“To ka sanar musu”
“Zan sanar musu, sai muje tare mu dauko ta, Abiey ya ce mu daina barinki kina aikin wahala”
Ya fada sannan ya mike tsaye ya bar dinning din. Ummi ta bishi da kallo tana tunanin yadda zata bullowa lamarin. Tashi tai ita ma ta nufi stairs sai da ta fara leka dakinta ta samu Dr da yaranta wato Jabir, Umar Juwairiyyya da kuma Yesmin sai yarta Namra suna karyawa, bata ce musu komai ba ta saki kofar dakin. Ta juya tana kallon bangaren da dakin Nimra yake, a take idonta ya cika da hawaye, takawa ta yi ta karasa har bakin kofar dakin ta murda kofar ta bude ta shiga ciki. Katon hoton Nimra dake manne ta fara kallo hawaye na mata zirya, sannan ta kalli wanda suka yi tare.
“Allah ya miki rahma yata”
Ta furta cikin kuka sannan ta karasa ta zauna saman gadonta kamin ta kwanta ta lumshe ido tana kuka.
[7/11, 1:27 PM] My S Line: 51
Kamar yadda Ummi ta bukata Maleek ya kira makarantarsu ya sanar musu school bus ba zata kawo Waira ba zuwa za'ayi a dauke ta, as the result of shi zai je ya dauke ta tare da Ummi.
Misalin sha biyu Ameer ya bar office ba dan ba shi da aikin ba, sai dan yana son ya cikawa Waira alkawarin da ya daukar mata, almost three days to four be je office ba sai dai kasancewar ya tashi da dan kuzari kuma da marmarin office din domin a yanzu takure yake yana bukatar abun da zai saka shi mantar da shi damuwarsa. Daga office din ya dauki hanyar makarantarsu, sai gashi ya tararda abun da ya fi tsana wato traffic, ko kadan baya son tsayawar da motoci suke, ba dan akwai motoci a gabansa ba babu wanda sai hana shi jan motarsa yayi gaba, ko da kuwa a kasar da ake cin tarar mutun ne idan ya karya irin wannan dokar balle a Nigeria da yake ganin komai yayi be yi laifi ba. Ana sakin traffic din yaja motarsa ba tare da lura da tsohuwar da ta zo da gudu zata karbi sadaka a gaban wata mota dake gefensa ba, a lokacinta na hanzari ta wuce kamin ya tashi motar yayi daidai da jan motar da yayi sai jin yayi ya bugu abu, da sauri yayi baya sai ya sake jin ya taka abu tsayar da motar yayi ya bude ya fito. Rayuwar Abuja ba ta yi ba wani lokacin, domin ba kowa yake damuwa da abun da ya dame wani ba, ba kowa ne ya tsaya kallon abun da ya faru ba, kowa ta tsabgar gabansa yake, few mutane ne suka iso gurinta mutanen da take bata a tare da su sune a suka fi yawa sai kiran Allah suke ganin yadda ya taka kafarta sai jini take. Taohuwar kuma sai ihu take kana ganinta ka san ta gama fita hayyacinta domin ya taka kafarta sosai a reverse din da yayi baya. Kansa ya shafa ya busar da numfashi.
“Innalillahi akwai yan'uwanta a nan?”
Ya tambaya yana kallon mutanen abokan bararta.
“Aa amman dai na san gidansu”
Cewar wata tsohuwar, kamin dayar ta ce.
“Akwai waya a jakar buhunta a dauko a kira iyalin”
“Kamin a kira iyalinta a yanzu dai ina son wani ya bini mu tafi asbiti”
Wacce ta fisu sauran kurciya ta kamata sai wasu mazan suka rika ta aka ciro kafarta daga karkashin motar, Ameer ya bude bayan motarsa aka saka ta, sannan dayar ta shiga ya rufe motar ana Allah ya sauwake. Da ada ne babu abun da zai saka Ameer tsayawa ba, ba tsohuwa ya kada be ko jajarin da aka haifa fa yau ne ya kade ba zai tsaya ba, kuma babu wanda ya isa yayi masa wani abu. Idan ma wadanda suka san shi ne sai dai aka kara a gidansu Mr Bashir ya dauki nauyin jinyar, wani lokacin kuma idan accident ya faru sai da ya ciro kudi ya watsa ma mutum yayi tafiyarsa. Amman yau shi ne da bude motarsa a saka masa wanda ya kade har jini na bata masa mota. Ban da private hospital din da suke zuwa be san wata asibiti ba dan haka can ya nufa da ita. Kai tsaye aa wuce da ita Emergency bangaren yan hadurra, a waje ya tsaya shi da macen da ta rakota ya karbi wayarta a jakar buhun dake hannun matar saboda ta tabbatar masa bata iya kira ba, bata iya amfani da waya ba. Da da ne ba zai iya rike wayar ba saboda ta fito a hannun da be sani ba, gashi wayar karama ce da ta kusan mutuwa har aka daureta da roba saboda murfi ya tsaya. Wannan kaddara ta sauya masa rayuwa da mu'alama, cikin har da walwalarsa da farinciki da yake a kullum. Bangaren kiransa ya shiga ya duba numbers din da take yawan kira da kuma wadanda ake kiranta.
“Kin san yadda ta yi saving number wanda za a kira”
Rasa number da zai kira ya saka Ameer ya kalli matar ya tambayeta.
“Eh ranka ya dade, sunanta Aisha jikarta ce ita kadai take da waya a gidan ma, kuma ita take cewa a kira mata idan za ayi kira”
Ya maida hankalinsa gurin wayar ya duba number farko da aka rubutawa Aisha ya kira a wayar ya mikwa matar.
“Toh Toh”
Ta karba da hannu biyu ta kara a kunne.
“Hello Aisha”
Matsawa yayi ya bata guri jin an amsa kira sai yayi gaba kadan yana rumgume hannayensa.
“Ranka ya dade ya sunan wannan Asibitin?”
Ya juyo ya fada mata tare da kallon agogon hannunsa.
“Hikima hospital”
Ta fadawa yarinyar a waya sannan ta sauke wayar.
“Tace gata nan zuwa, Allah sarki hankalinta duk ya tashi sai kuka take”
Ameer ya busar da iskar bakinsa ya sake kallon agogonsa a karo na biyu.
“Akwai inda nake son tafiya, za 'ayi muku komai a nan, karku kashe ko naira ni zan biya komai, kuma ki tsaya a nan ki kula da ita kamin jikarta ta zo, zan dawo a anjima”
“Toh ranka ya dade, Allah ya saka da alheri”
Ya kasa amsa mata da Ameen sai ya saka kai ya fice daga gurin. Daga asibitin kai tsaye ya nufi gurin wanki mota, shi ma da tambaya alexander ya isa gurin wankin motar da yafi kusa da asibitin domin be taba mai wanki mota ba, a gidansu ake wanke musu idan ma ya kama sai an kai toh ba shi yake kawai ba sai dai na bar motar a gida masu aikin gidansu, sai da isa gurin sai kuma wata zuciyar ta raya masa za su iya zargin wani abu, domin jinin mutum ne a motar ba kowa zai fahimta ba. Canja shawarar da yayi ne ya saka ya yi reverse sai ya canja hanya. Kamar ya san plan din da aka shirya isa makarantar a time din da suke daf da tashi. Waje ya tsaya ya aika mai gadin gate ya sanar da principal din yana neman Waira, har mai gadin ya ya tafi sai kuma ya dawo ya tambaya sunan babanta domin zai iya yiyu ba ita kadai cw Waira a school din ba.
“Ya sunana babanta?”
Ameer ya dan yi shiru yana nazari, be san sunan babanta ba kuma be san sunan da take amfani da shi a yanzu matsayin sunan uba ba.
“Waira Aliyu”
Ya fadi sunan mahaifin Maleek ba dan yana da tabbacin da sunan take amfani ba.
“Okay”
Ya juya ya shiga cikin makarantar. Be fadede ba ya dawo, sai aka bukaci Ameer ya shigo ciki domin tantance waye yake neman Waira. Yamutsa fuska yayi yana jin kamar yayi tafiyarsa, ya san idan ya shiga ciki za su tsare shi da tambaboyi ne da be san ma yadda zai amsa su ba. Ba dan kar tace ya karya mata alkawari ba da ba zai shiga ciki ba, haka dai ya daure ya fito daga motarsa ya shiga cikin makarantar, Security yana gaba Ameer na binsa a baya har suka shiga office din. Ameer ya mikawa mutumen hannu suka gaisa.
“Ka yi hakuri, dokoki ne na makaranta dole mu san wanda zai dauki dalibar mu, kuma dole mu san wanda ya kawo ta idan kawota aka yi, an kira mu daga gidansu an fada mana zaka zo, amman duk da haka ya kamata mu tantance waye kai, saboda hakkinmu ne kula da daliban mu matukar suna karanta”
Ameer yayi kamar yace musu shi ba daukarta zai yi ba ganinta kawai zai yi sai kuma yaji ba zai iya ba saboda gadarar ta tashi. Sun bashi littafi ya saka details dinsa, sannan aka kira Waira ta zo office din, ta shigo tana sanye da uniform, gashin kanta a fake a baya an sako shi ya sauko a bayanta, blue and black din uniform din ya mata kyau sosai. Tana ganin Ameer bata tsaya komai ta rumgume shi da murna.
“Da gaske zaka zo ashe”
“I said i will”
Ya amsa fuska ba yabo ba fallasa.
“Motana yana waje muje can mu yi magana”
“aa zaka jira mu tashi ne sai mu tafi tare, kai zaka kai ni gida zai mu yi magana a hanya”
“Let's talk first”
“Okay kaje ka jira ni a mota yanzu za a buga karaurawa”
Ya juya ya fice daga office din, sannan mutumen ya kalleta ya ce.
“Kin san shi?”
“Sosai”
“Okay ba wani matsala ko?”
Ta amsa masa babu da kai sannan ta juya ya fice. Ajinsu ta koma ta zauna a kujerar ta hada littafanta ta saka a jaka sannan ta kufa kanta a teburin da take karatun domin kowa da kujerarsa, haka take bata da sakewa a makaranta saboda suna mata kallon bare, gashi ita kuma ta kasa sakin jiki da saba da kowa, a kullum idan ta shigo makarantar tana maida hankali tayi abun da ya kawo ta ne, wannan ya saka take daga cikin students masu kwazo da saurin gane abu idan aka fada, ko aka yi musu bayani, secondly lessons din da ake mata a gida yana matukar taimaka mata sosai, sai dai sauran daliban da suka maida hankali kamar ita sun fita experience domin sun fara daga farko ne ita kuma ta hau abun ne daga sama.
Tana jin na kada ƙaraurawa ta goya jakarta da sauri ta dauko cake din da Ummi ta yi mata dake karkashin table dinta ta fice cikin zumudi ta nufi gate, a ka'ida idan za a fita daga makarantar sai anyi signed daga mai daukar har dalibai idan kuma School bus ce zata kai su gida zai sun yi shi ma mai tukin yayi da nufin shi ya kai su gida. Ita ta fara saka hannu a inda ta saba, sannan security ya nufi inda motar Ameer take ya kai masa littafi ya karba yayi sign din. Sannan ta bude front seat ta shiga yana kallonta sai ta sakar masa murmushi.
“Ya karatu?”
“Ba dadi”
Ya rage idonsa yana kallonta, he can't lie tana da kyau duk yadda zai misalta abun ya wuce tunaninsa, ba ma kamar yanzu da yake ganin nishadi da murna a fuskarta.
“Why?”
“Bana son karatun ni ai, Ummi forced to do so”
“If you don't want babu wanda zai saka ki dole, you can tell her”
“Ko na fada mata ba zata bari na zauna a gida, kuma Ya Maleek zai yi fada he hate me so much”
Ta dan bata fuska ta turo baki, irin batawar da ya kara mata kyau domin a shagwabe ta yi maganar. This is the second time da ya ji abubuwa suna burgeshi akanta, far'arta da kuma bata fuska ko wanne kyau yake kara mata. Ba dan ya tabbatar ita din ce yarinyar da ya gani a can duniyar ba mai matukar kazanta da datti da ko za a hade kur'ane a rantse masa ba zai yarda ita ce aka gyara ta zama kyakkyawa haka ba, har wani abu nata yake burgeshi, yarinyar fa ganin bera a kanta ya saka shi amai, gashi a yanzu ko yar minister ba zata gwada mata kyau gashi ba, domin an gyara mata shi ya kwanta lum ya kara baƙi sai sheki yake kamar ba nata ba.
Ta bude dan box din cake din ta saka hannunta ta gutsira cake cin ta ci. Yanzu kuma bakinta yake kallon yadda take motsa shi a hankali tana cin cake din, ta dago ta kalleshi sai ta dauki karamin spoon dake gefen box din ta saka ta dibi cake din ta kai masa saitin bakinsa. Ya kalli cake din sannan ya kalli fuskarta.
“Akwai dadi ka ci, na aje ban ci ba saboda kai, ban yi break ba”
Ya bude baki ta saka masa ya fara taunawa, ta aje spoon din ta saka hannunta ta fara ci.
“Akwai dadi?”
Ya daga mata wani irin kallonta yake kamar ya hadeta. Ta sake daukar spoon ta diba ta kai masa a baki ya karba ya ci, sai ta aje ta saka hannu tana ci.
“Ni bana ci abinci da wannan”
“Why?”
“A garin mu da hannu muke cin komai, ya fi dadi”
Ta saka saka dauka ta kai masa a baki, wannan karon da hannunta ta kai masa. Sai ya dan tsaya kallonta sannan ya bude bakin ta saka masa.
“Ummi ce ta yi min yayi dadi sosai”
Cak ya tsaya da taunawar da yake, fuskarsa ta canja daga ba yabo ba fallasa to ba yabo, hannu ya kai ya dauki tissue ya zuba ragowar a ciki ya sauke glass ya jefar. Wani iri yake ji ace mahaifiyarsa tana raye amman be taba cin abincinta ba ko sau daya, be san yadda girkinta yake ba.
“Tambaye ni abun da kike so, zan tafi”
“Kai zaka kai ni gida ai, na fadawa Ummi ba school bus zata maida ni ba”
Ya juyo ya kalleta kamar ya ce wani abu, sai kuma kwarjininta da ya cika masa ido ya hana shi kin cewa komai. Ya maida hankalinsa gaba ya jaya motar suka kama hanya, ko da wasa be sake kallon inda take ba.
“Ka yi fushi kuma? Saboda na baka cake din Ummi? Why do you hate her?”
“Why don't you ask her why she hate me from first place?”
“She didn't, tana sonka sosai Ameer”
“Kuma ta bar ni? Ita tace ki zo ki ba ni cake? Ki siye ni da kalamai?”
“Aa bana karya, bata ce tana son na baka cake ba, daman ni abincina daga cake sai biscuits ko fruits, tana yi min cake kullum”
Yayi shiru be ce mata komai ba, sai hawaye da suka cika idonsa.
“I'm sorry”
“You shouldn't”
“Ummi tana sonka sosai”
“Waira ke yarinya ba ki san komai ba”
Ta tari numfashinsa.
“Na san komai, na san komai tun kamin Ummi ta fada min na san komai”
Ya kalleta
“Taya? Wannan dan iskan Maleek ya fada min ko?”
“Ni bana hira da Maleek, he hate me shi ma kuma ni na fada masa, na sani ne ssboda ina iya sanin abun da ya faru da mutum”
This time around dariya yayi.
“Waira kina tunanin kin fini wayo? Kina iya sanin abun da zai faru miyasa kike tambaya waya koya min busa?”
“Be zama lallai ka sani ba, amman idan na rumgume ka zan iya sani”
“Then what are you waiting for?”
“Stop the car”
Ya samu guri ya faka gefen titi sai ta bude gefenta ta fita ta zagaya inda yake ta bude masa.
“Fito”
Samun kansa yayi da bin umarninta ya fito daga motar, sai ta rumgumeshi ta rufe ido, saman kanta yake kallo hannayensa na zube a muhallinsu, ta kai minti talatin tana rumgume da shi, shi be gaji ba kuma be saka hannu ya rumgume ta ba ko yace ta sake shi, duk kuwa da irin abun da yake ji. Ta dago ta kalleshi da kamar tsoro.
“Eid ya koya maka?”
Ta daga mata kai, ba dan yarda tana iya ganin past life din mutum ba.
“A garin da ka je karatu? Kana yawan busar sarewa amman baka iya mai kyau kamar nasa ba”
“Maybe kin san shi, shi ya fada miki cewar ya koya min”
“Be fada min ba, amman na san shi, shi ďan'uwa ne, na san da cewar shi kadai ya iya busar shiyasa nake mamakin yadda naji kana busawar”
“Na ji wannan sai kuma me?”
“Yau ka kade wata tsohuwar ka kaita asibiti”
“A motata akwai jini maybe kin ga jinin ne, cewa tsohuwa ce kuma wannan kin canka ne kawai, look Waira ke da Ummi ba za ku iya wasa da kwakwalwata ba”
Ya juya zai shiga sai ta ce.
“Ranar da Ummi ta fada maka ita ce mahaifiyarka, ka tafi gurin wata mata Humaira, ka fada mata damuwarka. Jiya kanwarka Fiyya ta shiga ďakinka ta yi magana da kai, kamin ka zo nan daga office kake. Kana shirya yadda zaka bar garin nan ka koma wata duniyar da babu wanda ya sanka ka zauna, ranar da Nimra ta mutu ka zo nan da