Showing 135001 words to 138000 words out of 281271 words
direban Daddy yayi ikama, mai bawa fulawowayin gidan ruwa yaja Sallah, kamin su sallame mamaki ya cika kowa. Ya sallame kamar yadda ake sallame ko wace sallah magarib, ya karanta addu'o'in sallah as usual ya daga hannunsa zai yi ma mahaifiyarsa da be taba manta ta mutu ba addu'ar samun rahma a kabarinta, sai ya tuna she's alive and healthy, hawaye suka zubo masa, saurin rumtse ido yayi ya hade yawu, ya mike tsaye sannan ya bude idon ya fice daga masallacin. Fitowarsa ta yi daidai da shigowar Motar Daddy, saboda kauna irin ta uba da ďa sai Daddy ya kasa tuka motar ya wuce ďansa sai sauke gilashin motar yayi yana tukin daidai tafiyar Ameer da ya ki yarda ya kalleshi, but murmushi yake saboda ya boyewa Daddy damuwar da ta bayyana kanta a fuskarsa.
“Yau na yi latti ka riga ni samun jam'i”
“Mu ma yanzu muka gama sallah”
Yanayin yadda ya amsa masa da kuma muryarsa da kallonshi da Ameer ya kasa yi ya kuma damuwar da ya gani a fuskar dansa, ya saka yayi saurin isa inda yake aje mota ya faka, domin shi yake tuka kansa da alama fitar ba mai nisa ba ce, domin jallabiyar dake jikinsa ama ta nuna haka. Kamin Ameer ya iso Daddy ya fito motar yana kallonsa. Sai Ameer ya kasa karasawa inda yake ya yanki hanya ya shige bangaren Mommy. Daddy na ganin haka ya ciro wayarsa dake pocket ya kira Hajiya Jamila. Kamar tana jiran kiransa domin ringing daya ta fara ta yi picking.
“Kin kira ni dazun, kina tambaya ta Ameer na fada mikin nima na kira shi be daga ba, and now yarona ya dawo gida, baya son kallon idona, na ga damuwa da ban taba ganin irinta ba a fuskar ďana, ya kasa karasowa kusa da ni ya shige bangaren Mommy, fada min me kike fada masa?”
Hajiya Jamila dake sanye da hijabi tana zaune gaban TV ta yi shiru for a seconds sannan ta ce.
“Gaskiya na fada masa, saboda ya bukaci na fada masa, kuma ya yi min ikirarin cewar idan na masa karya zai tsane ni, ba kuma zai sake yarda da ni ba, ba zan iya rusa wannan alakar dake tsakanina da Ameer ba, domin na fika sonsa, na san komai daren dadewa gaskiya zata bayyana”
“Da gaske kike yi? Ba duk gargadi da na yi miki?”
“Me yasa baka gargadi Zahra ba? Sai ni? Kana tunanin har yanzu kana da iko da ni? Ko kana tunanin zan manta irin butulcin da ka yi min bayan duk abin da na aikata saboda ka samu farinciki mu jidadin rayuwar aure na aikata? Amman duk baka duba wannan ba, a tsame ni a gidanka, ka raba ni da ďan da nake kallo a matsayin nawa, ďanta ruwan nonona ya taba zauna cikinsa, ďa daya tilo da na taba rumguma a hannuna a matsayin jaririna, ďan da duniya take kallo a matsayin ni na haife shi, kana tunanin duk zan manta da wannan? Ai kaima ka cancanci ka ji dacin da na ji”
“Idan har zaki iya fadawa Ameer gaskiya, to ba son gaskiya kike masa ba, kuma a yanzu na gode Allah da ya raba ni da ke tun wuri, kuma fada masa gaskiya ba zai canja komai ba, Ameer is still my son, babu wanda ya isa ya kwace hakan daga hannuna, har ita mai ikirarin uwarsa, na yi ma mijinta gargadi saboda ya ja mata kunne, idan kuma ba su ba, na san yadda zan yi da su all, and from today babu ke babu Ameer”
Ya yanke kiran ya nufi bangarensa yana takawa da karfi, kana ganinsa kasan ransa a bace yake. Ameer sai da ya kwatanta Daddy ya shige cikin sannan ya shiga bathroom dinsa ya wanke fuskarsa ya fito rike da towel yana goge fuskar. Boutique dinsa ya shiga ya tsaya a dakin yana kallon yadda Daddy ya zuba masa tufafin sakawa kamar shi ya fi kowa gata a duniya.
*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660 ki huta karanta na hakki*
Juyawa yayi kadan ya kalli kansa a katon madubin dake nuna har talkamin kafarsa. Zafin yana kirjinsa da idanuwansa, kansa yake kallo amman a badini gobensa yake hangowa, this is the most painful truth he has ever know gaskiya mai mugun daci da dafi a zuciyarsa. Hoton fuskar mahaifinsa dake jikin moton da Ummi ta ba shi yana ta dawo masa a ido yana ganin kansa a matsayin mahaifinsa. Ya jefar da tawul din a tsakar dakin ya fito kamshi na tsara shi ta ko'ina the women he thought is his step mom tana sakawa a gyara masa dakin a saka masa kamshi kamar yadda yake so saboda tasan abun da yake so kenan, kuma Daddy ya fada mata zaman lafiyarta ta yi ďansa abun da yake so.
Ya fito waje ya sauko falon ba tare da ya bar kowa ya ga fuskarsa ba, one of his fav Sis tana masa magana ya ki kulata ya fice daga falon. Cikin motarsa ya koma ya zauna ya dauko takardar yarjejeniyar ya sake karantawa countless times ya dauki hoton Deen ya kura masa ido, sai a yanzu ya lura sam baya kama da Daddy ta ko'ina, but how come be taba lura da hakan ba? Bude motar yayi ya fice rike da takardun bayan ya dauki wayarsa ya nufi bangaren Daddyn feel dizziness.
NAMRA POV.
Ta yi murmushi tana daidaita tsayuwarta.
“Mai jiki da sauki sosai”
“Maa Shaa Allah, Allah ya kara mata lafiya, ke fa ya kike?”
Shuraim ya tambaya a dayan bangaren.
“Ina nan kalau, saboda kana kusa ni, yaushe zaka sake shigowa kasan dai ba zaka wuce ba tare da mun sake ganin juna ba ko?”
“Zan zo hakan, ko dan ma yarinyar nan Waira, saboda na kasa manta yadda na barta a gidanku, tana ta kuka ta shiga damuwa, kanwarki ma na so na zo an dubata, amman ina tsoron yanayin da yan'uwanki ko iyayenki za su kalleni”
Iyakar kokarin da ta yi na danne abun da ta ji ne a lokacin da ya ambaci cewar zai so zuwa ko dan Waira.
“Ban gane ba, me ka gani a gurin iyayena kuma?”
“Sai na ga kamar ba jindadin zuwa na ba, bayan na gama bayyana musu ko ni waye, especially your Dad yanayin yadda yake amsa min ya nuna cewar ya san mahaifina, kuma kamar be yi maraba da ni ba”
Alamar mamaki ne ya cika fuskarta domin bata jin wannan ba, saboda ba a gabanta ya gaisa da su ba, kuma tashin hankalin da suka samu kansu a ciki na ciwon Nimra ya saka ba ta yi maganarsa da kowa ba.
“Ka fada masa wanin abun da be dace ba ne? Ko kuma akwai wani abu a nasabarka da be dace kowa ya sani ba?”
“To ban sani ba a halin yanzu, har sai na samu mahaifin mun yi magana da shi, amman ni ma san babu wata illa a nasabata sai dai kamin na tafi ina bukatar sake ganin ki gaskiya, kuma ina son ganin yarinyar nan please”
“Kana dai son ganinta, ba da ni ba”
“Both ke da ina ina mamarin ganinku, ita saboda na kwantar mata da hankali ta natsu, ke kuma saboda nawa hankalin ya kwanta, so please ki saka mana meeting point kuma ki zo min da ita”
“When?”
“Yau if possible, idan kuma ba zai samu ba zan hakura har zuwa gobe, ba dan haka ba babu abun da zai saka na sake kwana garin Abuja”
“Zan kiraka idan abun da kake bukata zai samu”
“Ganinki mai samuwa ne na sani, sai dai fitowa da Waira ne ba ni da tabbaci, amman dai ki min kokari please”
“Okay”
“That's my Babe Girl i love you ”
Ta samu kansa ta kasa amsa masa da i love you too kamar yadda ta saba sai sakon godiya data aika masa ta kashe wayar, ta juyo yana kallon Nimra dake bachi. Me yasa Abiey yayi masa haka shi ne abun da ya fara zuwa a ranta kamin ta fara jin kamar ta tsani Waira saboda yawan maganarta da Shuraim yake dan zuwan nan da ya yi. Daf da zata zauna aka turo kofar dakin sai ta fasa zaman ta kalli Maleek da ya shigo fuska babu walwala ba kuma zata ce ransa ne a bace ba, domin ba ta ga alamun haka ba, ya kusa cin karfin damuwarsa dan haka bata bayyana a fuskarsa ba, yana a wani yanayi da abu ne mai wahala ka bayyana halin da yake ciki, damuwa ce ko bakinciki ko rashin lafiya da jindadi ba kuma zaka ce yana cikin farinciki ba, haka kuma baka isa ka ce yana nishadi ba.
“Sannu da zuwa”
Da kai ya amsa mata ya zauna a kujerar dake fuskantar Nimra, yana kallon kanwarsa ta rame sosai kamar ba ita ba, har yanzu oxygen ne a bakinta da hancinta numfashinta na tafiya wahala kamar dai wanda yake daf da bankwana da duniya.
“Ya jikinta?”
“Da sauki, gashi har ta samu bachi, da bata iya bachi kuma likitan yana tsoron yayi mata allurar bachi saboda yanayinta, amman ga dukan alamu yanzu sauki ya fara zuwa”
Hannu ya kai ya shafa kanta da babu dankwali yana jin tausayinta, domin ta fada tarkon mutumen da ya tabbatar ko sama da kasa za su hade ba zai aureta ba, gashi tana ta wahala akansa. Namra ma kallonta take har sai da wayar Maleek tayi ringing sannan hankalinta ya koma gurinsa.
“Ina asibiti gurin Nimra”
“Akwai maganar da nake son mu yi mai muhimmanci Maleek, akwai abun da ya kamata ka sani”
Mahmood ya fada a dayan bangaren.
“Akan ciwon Ummi?”
“No akan Ameer”
“Me ya kuma ya faru?”
“I can't tell you on the phone, sai dai fada min inda kake ko kuma ka same ni”
“Kana ina?”
“King and his Kingdom”
“Okay gani nan zuwa”
Ya sauke wayar, gabansa na faduwa zuciyarsa na raya masa ko Ameer ya sake shirya wani abun ne, domin King and his Kingdom ba gurin zuwan Mahmood ba ne, it's a very right or appropriate place for rich kids like them amman ba gurin zuwansu ba ne, kara shi ma yana dan taba fita da abokansa sometimes amman Mahmood ya zama Mommy's boy, idan ya dade ya be dawo gida ba har kira take ta ji yana ina, not like Maleek da ta san baya son zaman gida saboda halinsa a can ba, duk da haka kuma ba zata yi bachi ba sai duka yaranta sun dawo gida. Waceaganar ce da ba zai iya fada masa ta waya ba? Shi ne dalilin karin kuzarin Maleek na fice daga asibitin ba tare da jiran kanwarsa ta farka ba...
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[7/1, 9:32 PM] My S Line: 45
Ya shiga falon Daddy a wani yanayi da be taba shiga ba, wannan ne karon farko da yake jin wani abu mai kamar kunya da bakinciki saboda zai tunkari Daddy yayi magana da shi, tafiyarsa ma ta banbanta da yadda ya saba yinta. A kofar dakin Daddy ya tsaya ya share hawayen da suke masa zuba sannan ya kai hannu ya kwankwasa kofar ďakin sai kuma ya fasa ya duka a gurin ya dafe kansa hawayen da tsaya suka dawo suna masa zuba. Ganin yake kamar ba gane ba ne ace Daddy ba mahaifinsa ba ne, ya kuma kasa karbar karyar da zuciyarsa take masa. Sai da yayi da gaske sannan ya iya controlling kansa ya share hawayensa ya mike tsaye ya kwankwasa kofar dakin.
“Yes come in”
Gabansa na mugun faduwa ya tura kofar dakin ya shiga, kunyar da bata san ta ina ta fito ba ta lullube ya kasa kallon Daddy har ya zauna a couch, Daddy ya aje wayar hannunsa yana kallon Ameer cikin wani yanayi na tsoron da gargabar rasa ďansa.
“Baka saba kwankwasa min kofa idan zaka shigo dakina ba, kana shigowa ne kai tsaye idan kana so ko da kuwa bana cikin dakin nan, ka dauki abun da kake so, ko kuma ka fadi abun kake so, miyasa yau zaka shigo min tare da kwankwansa”
Ya daga kai ya kalli Daddy sai ya kasa, a take kallon da yake masa a matsayin uwa ya sauya zuwa na maigida da yaronsa. Daddy ya nufi kujerar da Ameer yake zaune ya zauna yana kallonsa.
“Ameer fada min damuwarka me kake so? Fada ka yi da wani? Wani ya taba ka? Ko ka sake kade wani? Mommy ce ta taba ka? Or...”
Daddy na tambaya Ameer na hawaye kuma ya kasa dagowa ya kalli Daddy har lokacin.
“Me ya same ka Ameer? Waya taba ka? Fada min komai kake so a duniyar nan zan maka”
Sauka yayi daga kan kujerar da yake zaune ya zauna a kasa ya kama kafar Daddy ya rike ya dora kansa a cinyar Daddy sai ya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya. Daddy ya danne abun da yake ji a zuciyarsa ya cikawa bakinsa iska yana tunanin yadda zai bullowa Ameer domin bayan son ya nuna masa ya yi magana da Hajiya Jamila.
“Babban tashin hankalina a duniyar nan na ga tashin hankalin ďana, ina jure komai a duniyar nan ban da damuwarka, ka fi kowa sanin yadda nake gudun rigimar da kake shiga ko dauko magana, amman ni ne mutum daya da zaka gudu ka boya a bayana kuma na yi maka rumfa, na hana kowa taba ka, fada min Ameer me ka aikata? Wallahi ko rai ka kashe wannan karon na shirya baka kariya”
Sai a sannan Ameer ya samu gwarin guiwar dagowa ya kalli Daddy idonsa sun rine sun yi ja sosai kamar wani mashayi.
“Da rai na kashe da zan fi farinciki fiye da sanin abun da na san shi ne silar ajalina”
“Me kake nufi?”
“Daddy....”
Sai ya kasa furtawa sai hawaye yake kamar ba shi ba.
“Daddy i know it maganar da Mahafiyar Nimra fa fada i talk to Ammy ta tabbatar min da cewar gaskiya ne, and i confront her too ta kara tabbatar min”
Daddy yayi murmushi.
“Baka jin magana ta Ameer, rashin bin abun da nake fada ya jefa a cikin hali da dama, kuma zai sake jefaka a nan gaba, zuciyarka bata raya maka Jamila tana da alaka da Zahra ba? Shiyasa har ta furta sunanta? Saboda ta san zata goya mata baya su rusa tunaninka”
Ameer ya sake kallonsa da mamaki domin be tana sanin sunan matar da take cewa ita uwarsa ba ce sai a yau a bakin Daddy
“How do you know her name”
“Who?”
“Zahra?”
“Oh... Oh... Because a called her Husband kuma na gargade shi akan ya jawa matarsa kunne, ba zan dauki iskancin da take yi ba, ba zan lamuncin ta saka min tashin hankali a gida ba, and i already told my lawyer, idan ma akan hakan ne kakae wannan kukan da tashin hankali ka daina duk wani abun da za su fada maka karya ne”
“Me yasa za su yi karya?”
“I don't know, maybe suna da wata manufa akan hakan, musamman ma Jamila zata iya shirya wannan saboda na ko yarda na maida ita gidana”
“Daddy you can't hide this anymore, Ammy ta fada min komai ciki har da dalilin fitarta a gidanka, ta fada min dalilinka na boye min cewar mahaifiyata ta mutu”
“Kuma ka gamsu ka karya mahaifinka? Wane irin abu ka sha ne Ameer? Da rana tsaka wani zai kalleka yace kai ba dan Bashir ba ne dansa ne kuma ka yarda?”
Ya saka hannunsa aljihu ya ciro takardar yarjejeniyar da Zahra ta ba shi ya mikawa Ummi.
“What about this?”
Dauke wuta Daddy yayi for a seconds yana kallon takardar sannan ya mika hannu ya karba, sai da ya gama karantawa tsab sannan yayi murmushi mai sauti dake nuna be amince da abun da ya gani ba.
“Ina tunanin na haifi ďa mai tsananin basira da saurin gane komai, amman yanzu dan wannan abun zai saka ka karaya? Baka san muna a wani zamani da cigaba zai iya sakawa a yi komai ba?”
Ameer ya ciro hoton mahaifinsa ya mikawa Daddy.
“Wannan fa?”
Wannan karon dariya Daddy yayi.
“Karka ba ni kunya mana Ameer, wannan hotonka ne aka canja saboda a karkata hankalinka ka yarda da abun da suka shirya”
Ameer ya girgiza kai.
“Na san kana kokarin boye min komai ne saboda kai ma baka son karbar wannan gaskiyar mai daci, Daddy ina son ka sani, no matter how you try ko da ka yi nasara a yanzu, bayan mutuwarka dole gaskiya zata bayyana, sanin gaskiya ba zai canja komai a zuciyata ba, sai karin kimarka da daraja a idona”
Daddy ya saka hannu ya shafa kan Ameer.
“Karya suke fada maka Ameer idan baka yarda da ni ba, za mu iya yin gwajin jini tsakaninka da su da kuma tsakanina da kai, ta nan ma za a iya tabbatar da komai, kana yawan janyo min abubuwan tashin hankali, amman wannan da ka dauko ya fi ko wane daga min hankali, cuta kake kokarim haifar min da bana tunanin zata warke min da wuri”
“Daddy, ina son ka kalli cikin idona ka ratse min da Allah cewar Zahra karya take, ba mahaifiyata ba ce, ka karya hoton nan da yake hannunka, kuma ka tabbatar min da cewar kai ne ka haife ni ba sadakata aka baka ba”
“Tsaurin idonka ya kai har ka kalli idona ka fada min haka? Ba ka yarda da duk abun da nake nake fada maka ba? Idan da su kake son zama tashi ka tafi, zan iya hakura da rashinka”
Daddy ya fada a tsawace yana mikewa tsaye ya nuna masa kofa.
“Idan har zan fita daga nan, zan tafi ne a inda kai da ita ba zaku sake ganina ba balle jayayya ta hada ku, zan yi fatar mutuwa ne kai tsaye Daddy, na gode da duk wata kyauta da kulawa da ka ba ni, kuma an yi amfani da wannan damar na roki yafiyarka na abun da na aikata maka tun kurciya har kawowa yanzu dan Allah ka yafe min Daddy”
Ya mike tsaye ya nufi kofar da zimmar fice, gaba daya sa jikin Daddy yayi sanyi zuciyarsa ta karaya sai dai har lokacin be shirya fadawa Ameer gaskiya ba, da gaske baya son tashin hankalin Ameer kuma shi ma be shiryar karbar tashin hankalin cewar shi ba