Showing 129001 words to 132000 words out of 281271 words
da zancen dashen kwan da aka fada mana, yace ya fi son haihuwar ta zo daga Allah kai tsaye”
Ta tsinke zancen da take ta dauki ruwan dake kusa da ita ta sha. Sannan ta cigaba.
“Akwai wani Yayana sunansa Dr Hamid, kwararen likita ne dake aiki a Kano, da shi na hada kai yayi min duk abun da ya kamata na magani da allura na fara laulayi irin na masu ciki, kuma ya bani duk wani evidence da zan tabbatar wa da Mr Bashir da gaske cikin ne, farincikin da na gani a fuskarsa shi ya kara min kwarin guiwar cigaba da abun da nake, yan'uwansa suka dawi suna kaunata kamar sun lashe, daman na tsara cewar idan zan haihu zan bar kasar kamar yadda shi ma Mr Bashir ya bukata, na yi ta rainon cikina ni da Yayana muna ta neman inda zamu samu macen da zata ba mu ďa, ba mu samu ba saboda abu ne dake bukatar sirri, wata rana tsawan Yayana ya kira ni cewar an samu wacce zata siyar da cikinta saboda ayi wa mijinta aikin, na yi matukar murna kuma na jidadi, shi ya nema mana inda zamu hadu har muka ga juna muka kulla yarjeje ta saka hannu nima na saka, na bata copy takardar daya na rike daya dayar kuma tana hannun lauyana, a lokacin da zan haihu sai na ki yarda na bar kasar na haihu a gurin yaya a private hospital da yake aiki, tana haihuwa aka karbo yaron aka kawo min sannan na sanar da dangina da mijina cewar na haihu, mun dawo gida cikin farinciki sai dai yaro idan ya sha nono na baya Lafiya, idan aka bashi madara ko nonon wasu sai yayi ta zawo yana kuka, daga karshe a dole aka yanke shawarar gwada ba shi nonon mahaifiyarsa ta asali, ana gwadawa sai ya karba kuma be bashi matsala ba, hakan ne ya saka na rika aikawa ana tatsar nononta ana bashi daga baya kuma sai tace ba zata yarda da haka ba, sai na biyata kuma zai dai ta dawo gidana ta zauna, babu abun da ya wuce bin umarninta saboda ina son yaron, na sama mata gurin a gidan ta dawo ta zauna, ashe na matso da mutuwar aurena kusa ne ban sani ba, ta ko'ina akwai camera a gidan mu, kuma kanwar mijina Ummiter ta saka min ido sosai a lokacin saboda tana ganin kamar bana sonta na mallake yayanta kuma na kori yar'uwarta, zuwanta a cikin gidan shi ya tona asirina ya wargaza shirina, har mijina ya gano gaskiyar komai ya mallaka mata ďanta yace ba zai iya cigaba da zama da ni ba, babu kalar magiyar da ban masa ba, amman be saurareni ba, ni kuma hankali be tashi ba sai bayan da ya sake ni saboda soyayyar yaron ta shiga raina, sai dai kamin ya sake ni yayi min alkawarin ba zai fadawa kowa abun da na aikata ba, saboda rufin asirinsa da nawa, ba zan iya fadar dalilin dawowar yaron a hannun Mr Bashir ba, wata kila uwar yaron bata da bukatarsa a wacan lokacin ne, wata kila kuma mijin da zata aura yace baya son yaro, ko kuma tana tsoron fuskarta shari'ar yan'uwan uban yaron na asali ne, ko kuma dai arzikin Mr Bashir ta yi ke ma ďanta sha'awa saboda idan ya girma ita ma a sha miyar da ita, ni dai kam na san uwar da ta amsa sunan uwa take kaunar yaronta da gaske, kuma take son uban yaronta to zata zabi rike shi ne a ko wane hali ta shiga, yaran da muke naman Allah ya ba mu, amman ita ta samu ta wofintar? Wannan ai kamar butulcewa Ubangiji ne. Bayan rabuwar mu da Mr Bashir ya dade be yi aure ba, saboda ya gwada son uwar yaro sai dai tsoron saurayinta da ya dade yana farautarta yayi masa shigar rago, daga baya sai ya bar kasa tare dan saboda yana matukar kaunarsa da ya dawo kuma sai be zauna a Kano ba ya zauna a Abuja, ya saka ďansa makaranta mai kyau da yayi wayo sai ya fitar da shi waje, a duk tsawon lokacin nan kullum ina bibiyar rayuwar yaron ina zuwa ganinsa wannan ya saka shakuwa da aminci a tsakaninmu, amman ko na rana ďaya ban taba jin mahaifiyar yaron ta zo ganinsa ba, ban taba jin ta kira waya ta tambaye lafiyarsa ba, daga baya ma sai na samu labarin cewar ta haihu tana rayuwarta ta dabam, har sun bar garin Kano, sai dai ban san inda suka koma ba, na yi matukar takaici Ameer da yaron nan be girma a hannuna ba, da na nuna masa soyayya da gata fiye da yadda mahaifinsa yai masa, da be san wani abu maraicin rashin uwa ba... (Full story yana a cikin littafin farko wato CIWON SO labarin Zahra da Abiey da Deen da kuka Hajiya Jamila da mijinta Mr Bashir har ma da wasu, mai son zai iya min magana ya siya domin shi ma na kudi ne 08036126660) ”
Tare da shesshekar kuka ta karasa labarin.. Ameer ma hawaye ne ke sauwa daga cikin idonsa suna jika kumatunsa sannan su isa saman rigarsa.
“Wa... Wa.... Ne... Ne... Wa... Wa.. Wa.. Nan.. Na.. Na.. Nan... Ya.. Ya... Ya... Yar..... Yaron...?”
Yana tambaya kalamansa na tsinkewa, numfashi na ta kaiwa huhunsa hari....
“Ka yi tunani mana Ameer... Waye ya rike yaron? Meyasa mahaifinka be taba nuna maka hoton mahaifiyarka da ya ce ta mutu ba? Har yau be tana nuna maka danginta ba? Shin bata da family ne? Ko na rana ďaya yan'uwanta ba su tana ziyararka ba, kai ma baka taba zuwa ba, amman na mahaifinka suna yawan zuwa, kuma ya sansu, be fada maka inda aka binneta ba bayan mutuwar da yayi maka karya ta yi? Baka yi tunanin yadda kake fari kal kamar ďan larabawa ba? Mahaifinka kuma baki ne? Kai ba ka dubi madubi ba? Ta ina kake kama da Mr Bashir? A hanci ko ido ko haske fata? Mr Bashir ya boye maka wannan gaskiyar ne baya son ka sani har sai bayan ransa, baka yi tunanin miyasa yake ta mallaka maka dukiyarsa ba? Ko wane abu ya ce ya baka a saka shaida da sunanka, miyasa be ba kanenka ba? Saboda ya san baka gadonsa, babu wanda ya san kai ba dana ba ne, sai shi da ni da kannensa, duniya tana kallonka a matsayin ďan Jamila da Bashir, har matarsa da take cikin gidansa a yanzu bana jin ta san da cewar kai ba ďan Mr Bashir ba ne, saboda ya boye wannan sirrin da nufin ya zauna har bayan ransa”
Wani irin abu ne ya ratsa zuciyar Ameer ya rabata biyu...
“How could I believe this?”
“Me zai saka na yi maka karya? Bayan kuma kai ka bukaci sanin gaskiya, kuma ka bukaci kar na boye maka? Ban san dalilin na son dawowa a gareka ba yanzu, ban san me take nema ba, ba zan iya fadar abu da ta shirya ba, amman uwar data ba rike ďanta a lokacin da yake bukatar lokaci ba, bata rumgume a lokacin da ya fi kowa son dumin jikinta ba, bata cancanci kasancewa da shi a lokacin da ya saba da wasu iyayen da babu ita a ciki ba, da ace tana kaunarka Ameer da ta kashe aurenta ko kuma ta fasa auren mutumen da take aure a yanzu ta auri Mr Bashir saboda ta rike yaronta, miyasa ma zata cefanar da kai tun kana ciki? Ni fa kawai wadda ta yi shege na so na karba domin su daman basa bukatar yaran, sai gashi na samu mai halal, anya tsananin talauci ko neman mafita na saka uwar da ta amsa sunan uwa rabuwa da ďanta? Amman ban san manufarta na aikata hakan ba. Zan dauki hoton takardar yarjejeniyar da muka yi da ita na turo maka yanzu a whatsapp, domin tabbatarwa da kuma yarda da abun da na fada maka zaka iya zuwa ka tambaye idan har yanzu tana ajeye da takardar zata suna maka, sannan kuma zan hada ka da Yaya Dr Hamid dake Katsina domin ya warware maka zare da bawa, idan har gaskiya ta bayyaba mararan Ameer Zahra na bukatar amsa tambayoyinka...”
“Bayan bayyanar gaskiya Ammy, bana bukatar ta a kusa da ni, bana son yawun bakina ya hadu da nata”
Ya danna red circle ya yanke kiran, kansa yayi masa nauyi kamar an dora masa dotsin dala, kwakwalwarsa ta rikece ta birkita tunaninsa da abun da ya kamata yayi tunani da wanda be kamata ba duk kuwa masa yake, har wani na shiga cikin wani. Ya cire wayarsa dake phone holder ya shiga whatsapp dinsa da sauri, chat din Ammy ya shiga kamin ta turo masa hoton har ya kagu... Yana kokarin fita ya kirata sai ga hotuna guda hudu sun shigo sun bude kansa. First picture ya fara dubawa dokokin yarjejeniyar ne haka ya duba su har zuwa na karshe da inda Zahra da Hajiya Jamila suka saka hannu amincewa, sai kuma hannun lauya da na shaidu wato Dr Hamid. Ya jefar da wayar a kujerar dake kusa da tashi ya tashi ya daman motar a kunne take takata kawai yayi da karfi....
WAIRA POV.
Zamanta ta yi a cikin motar bayan sun iso saboda tana tsoron kar taje bude motar ta bata masa mota da hannunta da ya lalace da chocolate, har sai da Jabir ya fita ya zagaya ya bude mata sannan ta fito ta dauki ledar.
“Thank You”
Ta furta in soft voice tana murmushi shi ma murmushin yayi mata, hakan nan dai take burgeshi, daman can Jabir yana da saurin sabo da mutane domin wayeyen mutum ne da ya iya jan mutane jiki.
“Kin ga mun fita kina kuka yanzu mun dawo kina dariya”
Ta sake yin murmushi mai sautin, har ta juya sai kuma ta juyo ta kalleshi.
“Zaka kira kin Sulem? Ko mu je?”
“Inda yake?”
Ta daga kai.
“Toh ai kin ga ni ban ga Sulem din ba balle na san yadda fuskarsa take ba, kuma ban san masaukinsa ba, labarinsa kawai aka ba ni, kuma babu number sa a nan ban san number shi ba”
“Ka sani”
Ta fada da kamar shagwaba tana son dawo masa da kukan, a iya gaskiyar take fadar ya nemo mata Sulem ko ya kira mata shi, bata gama wayewa da abubuwan garin ba dan haka ba san idan baka da number mutum baka iya kiransa ko kuma shi idan ba shi da number ka ba zai iya kiranka ba, ita dai tana ganin ana waya a kara waya a kunne a ji magana, kuma a iya saninta garinsu idan ana neman mutum ba shi wahalar ganewa.
“Idan ina da number shi me zai hana na ki kira miki shi? Ba ni da number shi”
“Kana da”
Idonta har ya fara zubar da hawaye. Matsawa yayi kusa da ita ya ciro wayar ta shi ya mika mata.
“Idan kina da mumber shi saka a kira shi”
Ta kalli wayar ita dai tana jin ana cewa numbers kuma ana nuna mata su a makaranta, does that mean kowa yana da number shi kenan, sai ta kama ring din dake wuyanta, ta duba S ne a jiki tunanin ya bata cewar number Sulem dinta kenan.
“Na shi alphabet ne, ka saka S”
Jabir be san lokacin da dariya ta subuce masa ba.
“Ba haka ba ne, ita number kira ai tana da yawa ba kadan ba ce balle ace daya, kuma kin ga number dabam alphabet dabam na daya ba ne”
“Ka kira haka nan”
“Ko na kira ba zai yi ba look here kin ga babu inda S take a nan duk numbers ne”
Ya nuna mata wayarsa, sai ta taba 5.
“Gata nan, ita ce ta canja ka kira haka nan zai yi”
Ya fita gurin ya shiga gurin kira ya nuna mata numbers din mutane.
“Kin ga yadda numbers suke kowa da kalar tasa kuma suna da yawa”
“Ka saka 5 da yawa”
“5 dabam S da am ba a banbance muku ba a makaranta? Kuma 5 din har guda nawa zan saka?”
“Da yawa”
“Okay”
Ya saka 5 din kusan guda ashiri sannan ya kira ya saka mata a speaker, ta ji ana the number you try to call is not exist, sai ta fashe da kuka.
“Ka cika da yawa, ka saka kamar na su”
Ya rage ya saka daidai ya sake kira the same thing.
“Idan mun shiga ki ce Ummi ta kira shi ni wayata ta lalace bata kira kin ce ai abun da take cewa”
“Okay, ni meye number na?”
Gudun rigimarta ya saka dole ya bata number.
“2”
Ta share hawaynta da rigar jikinta sannan ta shiga falon, shi kuma ya juya ya shiga motar daman yana da gurin zuwa bata bari sun tafi ba tace ya kawo ta gida.
[6/24, 4:36 PM] My S Line: 43
Idonta be sauka a ko'ina sai akan Tea da ta bari dazun, kamin ta kalli dinning room tunawa da a nan ta bar Maleek a lokacin da suka fita, ba ta yi zaton Ummi ta dawo ba dan haka bata haura sama ba sai ta zauna a kasan kujerun da suke nan ta bude wani chocolate din tana ci, tana daf da cinyewa zomonta ya zo gurinta da gudu ya fara shinshina jikinta. Tana ganin haka ta tashi ta shiga Kitchen ta kunna tap ta wanke hannunta sannan ta dauki cup ta aje ta zuba ruwan zafi ta saka Lipton kamar yadda ta ga Ummi tana mata, sugar da sauran kayan hada tea da suke kitchen din sun mata tsawo domin suna a cikin cabinets ne, ita kuma ba wani tsayi ne da ita sosai ba idan ma zata ce ta dauko sai idan zata hau wani abun ne, dan haka ta dauko ta dawo dinning ta aje cup din ta bude sugar ta saka fiye da cube din da Ummi take saka mata sannan ta dauki daya ta kai baki tana tsotsawa, daki-daki ta bi har ta hada wa kanta tea ta dauko ta fito dinning area din ta dawo falo ta zauna, tana busawa saboda ya rage zafi.
“Idan Ummi ta dawo zamu ce ta kira Sulem ko?”
Baby rabbit dinta take tambaya da yarenta tana shafa kansa.
“Zill na baka labari? A can garin mu ina da bera da yawa a dakina, kuma ina da zakaru, kuma ina da Eid, na san yanzu ya manta ni, ko kuma yana jin haushin guduwa da na yi shiyasa ba zai zo ba na yi kewarshi sosai”
Shi dai zomon ya zauna a jikimta shiru sai saurarenta yake kamar fahimtar abun da take fada.
“Yanzu ni da kai Ummi ce mamanmu ko? Ko kuma ni ce mamanka kai ni kuma Ummi ce mamata”
Ta dauki tea zata kai baki sai ta kalli stairs Maleek dake tsaye rike da key ta gani tsaye yana kallonta. Babu annuri a fuskarta ba kuma fushi yake ba, rashin walwala ne irin ba wanda ke cikin tsananin damuwa domin idanuwanta sun nuna haka as well as fuskarsa. Aje cup din ta yi ta mike tsaye tana kallonsa a zatonta fada zai mata saboda fitar da Jabir yayi da ita, a kokarin ta na kare kanta ta duka ta dauki ledarta da cup din ta nufi inda ta saba boya ta zauna tana sauraren ta ji ko binyo ta zai yi. Shi kam bata ita yake ba, a zahiri ita yake kallo amman a badini tunaninsa da hankalinsa suna gurin damuwarsa ne. Ganin be wuce ba ya saka ta sake lekowa sai ta ganshi tsaye har yanzu inda ta tashi yake kallo sai dai wannan karon ta ga abin da ya daga mata hankali, hawaye ta gani a idonsa, saurin boyewa ta yi gabanta ba faduwa. Tana jin saukowarsa ta takure guri daya ta yi zaton gurinta zai zo, sai ta ji shuru hakan ya saka ta sake lekawa ta ga baya gurin, fitowa ta yi gaba daya, ganinsa ta yi zaune akan kujera ya cije ya cije baki yana kallon wani gurin dabam.
“Ya Maleek”
Yesmin ta kira shi be amsa mata ba be kuma juyo ba, sai yayi saurin tashi ya fice daga falon ba tare da ya bari ta ga hawayensa ba. Waira ta kalleta ba wani sabo ta yi da ita ba dan haka bata ce mata komai ba ta koma ta zauna a inda ta saba boya ta dauki tea ta rike da hannu biyu kamar yadda ta saba yi ta shanye duka. Sannan ta sake fasa wata ledar chocolate din ta fara ci tana yi tana lashe hannu, sai da ta gama sannan ta fito rike da cup din ta nufi kitchen jin motsi ya saka ta boye sai ta fara lekawa ta ga Yesmin ce ke kokarin kunna gas sannan ta shiga ta aje cup din ta wanke hannunta, bata san rike sunan Yesmin ba, dan haka ya saka ta matsa kusa da ita ta taba rigarta.
“Zaki kira min Sulem”
“Waye kuma Sulem?”
“Wanda ya zo, ko ki kira Ummi”
“Ummi tana dakinta, shi kuma Sulem ban san shi ba”
Tana jin haka ta yi saurin fita kitchen din ta nufi stairs da gudu ta fada dakin Ummi sai ta tarar da Ummi a bathroom.
“Ummi... Ummi”
Ta kira sunanta daga bathroom din Ummi ta amsa muryarta a shake.
“Na'am Baby Waira gani na fitowa”
Gurin kofar Bathroom din Waira taje ta tsaya har sai da Ummi ta fito, sai ta rumgume ta tana murnar ganinta ita dai idan Ummi bata cikin gidan bata da natsuwa da kwanciyar hankali duk sai ta ji kamar bata da kowa a duniya ta zama marainiya.
“Oyoyo Yata i miss you”
“Ummi baki tafi da ni ba”
Waira ta fada tana kallon idonta dake kumbure har bata oya bude da kyau.
“Waira ko dan kin ji ina ce miki Baby? Ke fa ba yar karamar yarinya ba ce da zan rika yawo da ke, daman can ai ba fita nake da ke ba, dan haka ki daina cewar ma ban tafi dake ba”
“Ummi idonki ya dahu”
Ummi ta yi dariya tana murza idon.
“Ciwo yake”
“Kuma Ha Maleek yayi kuka”
“A ina kika gani? Maybe saboda Nimra bata da lafiya ne, kin san tana asibiti ko?”
Ta daga kai, Ummi ta sake ta ta nufi wayarta dake