Showing 87001 words to 90000 words out of 281271 words
zaune tana kallonsa da idonta masu kamar na mage. Tashi tayi ta dauki wayar Ummi dake kusa da ita ta haura sama, bata dade ba ta sauko har lokacin yana tsaye gurin Plasma doing nothing thinking nothing, zuwa ta yi ta boya bayan cushion din da ta kwanta. Sai da ya fara kallon gurin for like 15 to 20 seconds sannan ta taka a hankali ya leka, sai ya same ta ta kwanta a kasa ta takure guri daya take rike da wayar Ummi, ba tabawa take ba ta dai rike wayar kawai. Upstarts ya nufa yana hawa ya tura kofar ďakinta a hankali sai ya hango Yesmin kwance a kan gadonta, slowly ya rufe kofar ya nufo downstairs, saukowa tai daidai ta fitowar Ummi daga bangaren Abiey rike da cup a hannunta.
“Aljanin dare baka kwanta ba?”
Ya ďan yi murmushi kaďan kamar na amsa mugun dole.
“Abinci nake son ci”
“Okay”
“Yarinyar nan bata kwanta ba”
Ummi ta juyo tana kallonsa domin ta yi rabin falon, jin muryar Ummi ya saka Waira ta fito daga inda take ta nufo Ummi.
“Waira Baby kin tashi?”
Ta daga mata kai.
“Kina jin yunwa”
Ta daga kai.
“Zaki sha tea? Ko madara?”
“Tea”
Ta amsa, sai Ummi ta kama hannunta.
“To zo muje mu hada tea”
A tare suka shiga kitchen din Ummi ta hada tea a cup biyu ta bata ďaya ďayan kuma ta ce ta dauka ta kaiwa Maleek, sai ta girgiza mata kai.
“Aa”
“Dauki ki kai masa ba ni na saka ki”
Ta aje nata cup din ta dauki na Maleek ta fito kitchen din tana tafiya a hankali ta nufi inda yake zaune a dinning yana cin nasa abincin daren, kusa da plate din da yake cin abinci ta aje masa tea a hankali. Sai ya dago ya kalleta.
“Tea Ummi ta ce Waira ta kawo Tea..”
Ta fada sannan ta juya ta nufi hanyar komawa Ktchen din yana binta da kallo.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 29
“Kin kai masa Tea”
Ta daga sai Ummi. Ta girgiza mata kai.
“Bude baki yi min magana”
“Waira ta kai ma Ya Maleek Tea”
Ta saka Yaya ne saboda haka Nimra ke kiransa.
“Ba haka ake cewa ba, cewa zaki yi Na kai ma Ya Maleek Tea din”
“Na kai ma Ya Maleek tea din”
Ta maimaita kamar yadda Ummi ta bukata, sai Ummi ta yi murmushi.
“Good daga yanzu idan na yi miki magana ki rika bude baki kina amsa min, kin ga dazun na ji haushi duk zamana da ke a gidan nan baki taba bani labarinki ba, amman wani yana zuwa kin fada masa komai har dariya kike masa sosai ana jin muryarki ko'ina”
Ummi ta yi sad face tana bayyana damuwarta a fili, sai Waira ta kama kunnenta ta ce.
“I'm sorry Ummin”
A karo na biyu Ummi ta sake yin murmushi.
“Good na yi hakuri amman karki sake kin ji ko?”
Har ta daga kai sai ta tuna da Ummi tace ta rika bude baki tana mata magana, a take ta ce.
“Tohm”
“Minene Good ma?”
Ta mata thumps up tana dariya.
“Yayi kyau”
Ummi ma dariyar ta yi ta dauki tea ta mika mata, muje falo ki zauna ki sha idan kika gama sai ki kwanta. Kamar mai jiran umarni sai ta karba ta juyo ta fito kitchen, gurin da set din kujerun falon suke zata nufa sai Ummi ta dakatar da ita.
“Zo ki zauna a dinning”
Ta juyo sai ta kalli Maleek dake zaune yana ci abinci ta kalli Ummi, Ummi taja mata kujerar dinning dake kusa da Maleek, ta mata haka ne saboda ta sake jiki da shi, domin shi ne kadai mutumen da bata shan inuwarsu sai kuma Namra. Bata son musu hakan ya saka ta taka a hankali ta isa gurin ta zauna a kujerar da Ummi taja mata, ta rike tea da hannu biyu marikin cup din ta yi sama da shi, haka take idan tana shan tea ko a abu a cup sai ta rike da hannu biyu. Bayan ta zauna Ummi ta bar dinning din zuwa duba bakinta, jikinta ya bata Maleek kallonta yake hakan ya saka ta juyo ta kalleshi sai ta ga idonsa yana kan zoben dake wuyanta, ta kalli zoben sannan ta dago sai suka hada ido.
“Ummi tace Waira ta zauna nan”
Ta fada da sauri gudun kar yace ta masa laifi. Shi kuma sai ya amsa mata a ransa.
“Kin ji nace miki wani abu ne?”
A zahiri kuma sai ya dauke idonsa daga barin kallonta ya cigaba da cin doyarsa, juyawar da yayi sai ya bata damar rama kallon sarkar wuyanta da yayi, sai dai ita a yanzu a fuska take kallonsa kamar wani hoto ko kyaftawa bata yi, ta gefen ido ya ga tana kallonsa kuma kallon ya kasa barinsa ya samu natsuwa har sai da ya dago ya kalleta, abun ka da wanda be iya munafurci ba sai ta kasa dauke idonta taga barin kallon nasa, idonta suka fara blinking babu tsayawa kamar marar gaskiya, can dabara ta zo mata sai ta rumtse idon gaba daya. Samun kansa yayi da murmushi a cikin zuciyarsa ya dauki ruwan dake gabansa ya sha ya ja kujerar baya ya tashi ya bar mata dinning din.
Ummi dakinta ta fara dubawa sai ta tarar har Dr Zainab ta yi bachi, gudun kar ta yi motsi mai karfi ta tasheta ya saka ta shiga a hankali ta bude bathroom ta yi wanka tare da wanke baki sannan ta fito ta dauko kayan bachinta ta saka ta fito tana ta kamshin turare. Dakin Namra ta fara budewa ta leka saita same ta ita kadai tana bachi, daman can ta san Namra ba zata kwana da kowa a dakinta ba, idan har wani zai kwana akan gado daya da ita kara ta kwana akan kujera, ita dai bata son ta motsa ta ji wani a kusa da ita. She has so many rules and regulations na banza da take sakawa kanta just to be unique. Ac dakin Ummi ta rage ta ya janyo mata kofar ta maida ita a yadda take. Sannan ta nufi dakin Nimra abun ka da mai son jama'a sai ta same ta ita da Juwairiyyya suna kwance a gado daya, sai dai da alama Nimra bata shiryawa bachi ba, domin wayarta ta fado kasa hannunta kuma yana lilo a gefen gadon ga wutar dakin a kunne ba kamar Nimra da ta kashe nata ba. Ummi ta karasa ta duka ta dauki wayar sai ta ga missed calls biyu daga heart emoji guda uku, ga kuma wani sako a saman screen din wayar.
(𝑫𝒐𝒏'𝒕 𝒕𝒆𝒍𝒍 𝒎𝒆 𝒌𝒊𝒏 𝒚𝒊 𝒃𝒂𝒄𝒉𝒊 𝒕𝒖𝒏 𝒚𝒂𝒏𝒛𝒖 𝒌𝒊𝒏 𝒃𝒂𝒓 𝒏𝒊 𝒅𝒂 𝒌𝒆𝒘𝒂𝒓𝒌𝒊, 𝒈𝒂𝒏𝒊 𝒂 𝒏𝒂𝒏 𝒔𝒂𝒊 𝒋𝒖𝒚𝒊 𝒏𝒂𝒌𝒆 𝒂 𝒃𝒆𝒅 𝒊𝒏𝒂 𝒔𝒉𝒂𝒌𝒂𝒓 𝒌𝒂𝒎𝒔𝒉𝒊𝒏 𝒕𝒖𝒓𝒂𝒓𝒆𝒏𝒌𝒊, 𝒃𝒚 𝒕𝒉𝒆 𝒘𝒂𝒚 𝒌𝒊 𝒔𝒂𝒏 𝒊𝒓𝒊𝒏 𝒌𝒂𝒓𝒚𝒂𝒓 𝒅𝒂 𝒛𝒂𝒌𝒊 𝒚𝒊 𝒈𝒐𝒃𝒆 𝒎𝒖 𝒉𝒂𝒅𝒖 𝒊 𝒂𝒍𝒓𝒆𝒂𝒅𝒚 𝒎𝒊𝒔𝒔 𝒚𝒐𝒖, 𝒊 𝒄𝒂𝒏'𝒕 𝒘𝒂𝒊𝒕 𝒇𝒐𝒓 𝒚𝒐𝒖𝒓 𝒉𝒖𝒈 𝒂𝒏𝒅 𝒌𝒊𝒔𝒔 𝒌𝒊𝒏 𝒔𝒂𝒏 𝒃𝒂𝒏𝒂 𝒈𝒂𝒋𝒊𝒚𝒂 𝒅𝒂 𝒌𝒆 𝒊 𝒍𝒐𝒗𝒆 𝒚𝒐𝒖 𝒔𝒘𝒆𝒆𝒕 𝒅𝒓𝒆𝒂𝒎)
Wani irin tashin hankali da fargaba irin na uwa mai ƴaƴa mata ne ya bayyana a fuskar Ummi, jikinta ya dauki rawa as well as zuciyarta dake bugawa, she can't believe ta ga sakon nan a wayar ƴarta ƴar ma Nimra wacce zata rantse idan aka saka mata yatsa a baki ba zata ciza ba, a cikin sakon babu abun da ya fi daga mata hankali kamar inda yake cewa ta san kalar karyar da zata yi su hadu? Su hadu a ina? Ina suke haduwa? Why not ya zo gidansu idan sonta yake? Wani ta hadu da shi yake mata wayo haka? The hug and kiss part ma abun tashin hankaline, Nimra zata iya rumgumar wanda ba mijinta ba har ta sumbance shi? Bayan wannan sai kuma me? Ummi ta kalli Nimra dake sharar bachinta hankalin kwance bata san abun da ke faruwa ba. A hankali Ummi ta aje wayar a gefen gadon ta juya ta nufi switch din dakin ta kashe sannan taja kofar a hankali ta fice, gaba daya jikinta yayi sanyi, tunani kala kala ya fara zuwa mata har da wanda be kamata ta yi ba a lokacin, tafiya kawai take tana saukowa basa not knowing downstairs take saukowa har sai da ta ji Waira kira sunanta.
“Ummi ta shanye tea”
Ta kalli saitin inda take ta sauke wani uban ajiyar zuciyata ta kai hannu ta dafa zuciyarta, tunanin mai kokarin gurbata mata tarbiya ƴa take, kawa ta hadu ita marar tarbiya ko kuma saurayi? Amman idan kawace ya akayi bata san da ita ba a matsayinta na uwarta? Sai a yanzu take gane maganar da hawasa suke cewa mai ƴaƴa mata hannunsa a kirji yake har sai ya aurar da su, idan kuma ya aurar ba ya rufe ƙofa. Ta bawa Yayanta yarda 100% saboda tarbiyar da take ganin ta yi musu hakan ya saka wanin abun bata damuwa ta zafafa bincike kwakwaf akansu ba.
“Waira zo muje ki kwanta dare yayi sosai”
Waira ta taso ta nufo inda Ummi take sai Ummi ta rike hannunta suka haura sama, ta shiga da ita dakinta ta bude wardrobe ta dauko mata kayan bachi ta aje mata akan gado.
“Shiga ki yi wanka ki yi brush zan jira ki a nan”
“Tohm”
Ta nufi bandakin, Ummi ta zauna baki gado tana ta tunani kala kala, for how long alakarsu take da wannan mutumen waye ma shi? Mace ne ko kuma namiji, domin a yanzu a wane hali da mata suke neman mata yan'uwansu, maza ma su nemi maza yan'uwansu, miyasa ko da rana ďaya bata gabatar mata da shi a matsayin saurayinta ko wanda take son aure ba? Ita dai saninta a yanzu babu mai zuwa zance gurin Nimra kara ma can da ana zo jefi jefi amman ban da yanzu, balle ta yi zargi wani ne a cikin masu zuwan. Bata son ta munana mata zato hakan ya saka ta fara kokarin yakar zuciyarta ta kawar da abun a ranta. Waira ta yi wanka ta yi brush kamar yadda Ummi ta koya mata idan zata kwanta sannan ta fito ta saka kayan bachin Ummi ta nuna mata turare, sai ta nufi inda turaren yake ta dauka ta fesa a jikinta.
“Baby Waira kin san miyasa mai miki lessons be zo ba yau?”
“Aa no aa”
Ta fada har sau uku a kokarinta na bin umarnin Ummi na amsa mata da baki ba da kai ba.
“Be fada miki komai ba a jiya yace ko ba zai samu zuwa yau ba?”
“No be fada mata”
“Mini”
Ummi ta gyara mata
“Mini komai ba”
“To zo ki kwanta”
Ta hau ssman gadon ta kwanta gefe nesa da inda Yesmin take kwance, sai Ummi ta bude wani karamin kwando ta dauko safa ta saka mata a kafa.
“Kin gani da ace addininmu kike yi sai na ce ki yi addu'a kamin ki kwanta, saboda ki samu tsari wani abu ba zai cutar da ke ba, mutum ko aljani ko wani ƙwaro mai cutarwa”
Waira dai bata ce komai ba sai sauraren Ummi take, can kuma ta ja blanket ta lulluba, sai Ummi ta kai hannu tana shafa kanta tana ta tunani har bachi yayi gaba da ita, sannan ta tashi ta ja windows din dakin dake bude ta rufe ta kashe musu hasken dakin taja kofar ta fice. Da tunanin abun da ta gani a wayar Nimra ta kwana a ranta, har mafarkin abun sai da ta yi tana ta tunanin yadda zata bullowa abun. Hanne ta shirya abun karyawa da taimakon Ummi, bayab ta gama shiryawa mijinta nasa abun karin domin baya cin na masu aiki, sanin wannan ya saka ta rike wannan al'adar ta yi masa girki da kanta a kullum ko da kuwa ruwan tea ne.
Ya baro bangarensa ya dawo bangaren Ummi yayi breakfast tare da yar'uwarsa suna ta hiran baya, kowa da kowa yana falon ana karin safe idon Ummi yana kan Nimra she just can't believe ace Nimra ce aka turawa sakon jiya, ko da yake hausawa sun ce ka yi naka ka barwa Allah sauran, domin tarbiya a yanzu duk yadda ka yi sai idan Allah ya tsare maka kawai. Ita kuma Waira nata idon yana kan Ummi tana tunanin abun da ta gani jiya har yanzu zuciyarta cike da tausayin Ummi, Maleek kuma nasa idon suna kan Waira a sirrance kallon da take yi Ummi ne yake ba shi mamaki, da haka kuma wata ilar ta ja shi ya fara kallace surarta.
Bayan kowa ya gama karyawa Ummi ta saka suka kwashe kayan suka kai kitchen, Maleek da Mahmood da Namra suka yi shirin tafiya aiki. Daman Waira tuni ta yi shirya a uniform dinta na makaranta school bus ta wuce da ita ita First fita a gidan sannan Maleek da Mahmood, daga baya Namra ita ma ta fice. Jabir kadai aka bari a gidan sai Umar da Nimra, shi ma be dade ba ya fita tare da Dr Zainab da Umar zuwa gurin wasu yan'uwansu da suke cikin garin Abuja.
Misalin 12pm Ummi na kitchen tana hada ma Waira cake Nimra ta shiga sanye da doguwar rigar material sai black hula dake kanta, jikin kofar kitchen din ta tsaya tana kallon Ummi.
“Ummi me kike yi”
“Cake”
Ta amsa mata ba tare da ta juyo ta kalleta.
“Waira ake yi ma ko? Toh a saka da mu, Ummi ina son zan tafi gurin saloon din nan jiya ban samu ba, amman yau na yi da ita zata gama min da wuri”
Shiru Ummi ta yi kamar ba zata amsa ba, tana ta kallon harabar gidan da take hangowa ta windows din kitchen din sai kuma ta juyo ta kalli Nimra.
“Miyasa ba ayi miki ba a jiya?”
“Akwai jira ne sosai kuma da kika kira ni cewar Mommy ta zo sai na fasa na dawo gida”
Ta daga mata kai.
“A dawo lafiya”
Har ta juya ta fita sai kuma ta juyo ta ce
“Ummi lafiya kike yau kuwa?”
“Me kika gani”
“Na ga kamar kina cikin damuwa yanayin ki ba kamar na kullum ba”
“Daman akan samu hakan ai a gurin ko wace uwa, wata rana farinciki wani lokacin kishiyarsa karki damu tafi inda zaki je Allah ya tsare”
“Ameen”
Ta juya ta fita, tana fita Ummi ta wanke hannunta a tap ta fito Kitchen din da sauri ta haura sama Hijabinta kawai ta dauko ta saka ta ta dauki key motarta ta koma jikin Windows din dakinta tana kallon waje, har sai da ta hango Nimra ta fito sannan ta sauko da sauri kamar zata fadi, a jikin kofar falo ta tsaya sai da Nimra ta shiga mota murza key sannan Ummi ta fito ko da ta shiga tata motar Nimra ta fice daga gidan, masu gadin suka fasa rufe gate din suka budewa Ummi. Ta yi sa'ar hango inda Nimra ta bi saboda titin unguwar mai tsayi ne sosai kamin ka kai karshen road din ka dauki wani tafiya ce mai dan nesa. A hankali Ummi take binta sai dai tana nesa da ita ta yadda Nimra ba zata iya hangota ba, ko kadan bata jindadin abun da take kokarin aikatawa na bibiyar sawun yarta, sai take jin kamar be kamata ta yi hakan ba, sai dai ya zame mata dole ko dan ta wanke zuciyarta daga zargin da take yi na Nimra. Sannu a hankali Nimra ta tuka motar har cikin unguwar da gidan Ameer yake, Ummi na binta sau da kafa har ta hango ta tsaya a bakin gate din wani gida ta danna horn, wani maji karfi ya leko gate din sannan ya koma ciki ya bude mata ta shiga. Ummi ta ji wani abu mai karfi ya tsaya mata a makoshi, zuciyarta ta hau bugawa fiye da kima, yaushe Nimra ta lalace haka? Miyasa zata watsar da tarbiyar gidansu ta dauki wata bakar dabi'a? Tun yaushe take mata karyar fita zuwa wani gurin tana zuwa nan? Gurin wa take zuwa?
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Ta furta tana saka hannu ta dafe zuciyarta.
“Allah ka gani na iyawar iyawata, na ba su tarbiya daidai gwargwadon yadda zan iya, Allah ka kama min, na shiga uku ni Zahra, farko Ameer ta shi ta wuce, daga baya Maleek shi ma ya fara samun sauki a yanzu, sai kuma Nimra, bayan ita kuma sai wa”
Ta lumshe ido hawaye na sauko mata, son sanin me take aikatawa kuma da wa take aikatawa ya saka ta share hawayenta ta bude motar ta sauko, ta taka da kafa har zuwa inda gidan yake da tunani kala kala. Ta dade a tsaye sannan ta kai hannu ta kwankwasa gate din gidan, babu jimawa mutunen da ya budewa Nimra ya bude mata.
“Dan Allah tambaya nake ko masu gidan na ciki?”
Ta kalli Ummi sama da kasa, yana ganinta ya san ba irin masu zuwa manyan gidaje roko ko neman wani abu ba ne domin hannunta ma rike yake da key mota.
“Aa baya nan lafiya kike nemansa?”
“Lafiya kalau, na yi magana da shi ne yace na zo na same shi a nan”
“To gaskiya be iso ba, tukuna amman dai yana kan hanya tun da kika ga wannan matar ta zo”
Ummi ta hade yawun bakinta daker.
“Ko zan iya shiga na jira shi a ciki?”
“Aa gaskiya, saboda be yarda na bar kowa ya shiga gidan nan ba”
“Amman yanzu na ga wata ta shiga”
“Eh to ita ya san da zamanta, shi ya bada umarni da zarar ta zo na bude mata ta shiga”
“Amman dan Allah ta dade tana zuwa nan ne?”
“Wannan kuma wani abu ne da be kamata ki ji shi a bakina ba, domin be kamata na fadi wani abun da ya shafi gidan a gurin bakuwar fuska ba, dan Allah ki jira shi ya zo ko kuma ki kira shi”
“Haka ne, na bar wayata a mota bari na dauko na kira shi”
Ta juya ta nufi gurin motarta hawaye masu zafi na sauko mata, tana barin gurin mai gadin ya juya ya koma ciki ya dauki tasa wayar ya kira Ameer ya sanar masa abun da ya faru. Ummi na shiga motar ta dafe saka hannu biyu ta dafe kanta ta fashe da kuka....
AMEER POV.
“Oh Really”
“Kasan ai ba zan iya ce maka No ba, amman dai ka yi sauri domin ba zan dade ba, kasan dole na tafi gurin saloon