Showing 153001 words to 156000 words out of 281271 words

Chapter 52 - Wani Gari Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1213

why you're my favorite Safiyya kin fi kowa fahimtata da kusantar inda nake”

Ta rike hannunsa.

“Ka yi min alkawari zaka canja Yayana?”

“Sure for you only”

Taja hancinta sai ta yi dariya ta mike tsaye.

“Daddy yana kiranka zaku ci abincin dare”

Ya busar da iskar bakinsa.

“Oh... Okay ina zuwa”

Ta masa waving sannan ta fice. After like ten minutes da fitarta ya rufe littafi ya mike tsaye yana gyara rigarsa ya fito daga dakin. Ko da ya shiga bangaren Daddy ya same shi har ya fara cin abincinsa.

“Yunwa nake ji ba zan iya jiranka ba”

Ya kalli dinning din da aka cika da kuloli, ya kalli plate din Daddy dake cin tuwon shimkafa da miyar kubewa sannan yaja kujera ya zauna.

“Yau kam Mommy ta yi min favorite dina kai ma kuma ta yi maka na ka”

Daddy ya fada yana cin tuwo fuska sake kamar babu damuwa a tare da shi, tun a lokacin da abubuwan nan su faru Ameer ya daina ganin kwanciyar hankali da far'a a fuskar mahaifinsa sai yau. Daddy ya dauki plate ya mika masa.

“Ka zuba abun da kake so”

Ameer ya karba ya aje plate din a gabansa ya bude one of expensive warmers da suke gurin ya fara zuba White rice da aka sakawa green beans da carrots da green pepper da yellow, haka yake son a dafa masa farar shimkafa sai a hada masa da miyar hanta zallar hanta, a yankata kanana ta yadda kowane spoon sai ya ci da ita a ciki.

“Dazun mahaifiyarka ta zo, sai dai na hana ta ganinka saboda kar ta takuraka i know baka son ganinta a yanzu”

Daddy ya fada yana kai yankan nama a bakinsa. Sai Ameer ya tari numfashinsa.

“ZAHRA na ganta”

Daddy be damu da kiran sunanta da yayi kai tsaye ba, daman yasan indai Ameer ne komai ma zai iya faruwa.

“Oh really? Ka yi magana da ita?”

“Yeah na fada mata karta sake zuwa gidan nan”

“Saboda gidan nan gidanka ne?”

Ameer ya kalli Daddy.

“Daddy don't joke about this”

“I'm not joking shiyasa da tace zata ganka na hana, amman idan zata zo gurina ko gurin Matata wannan ba huruminka ba ne? Ka fi kowa sanin bana son ana wulakanta mutane”

“Daddy bana son ganin matar nan, da bata min duk wani tsari da tunani na rayuwa”

“I know amman dukan dam'adam ajizi ne Ameer, tana da laifi tabbas kuma ta cancanci duk wani hukunci da zaka yanke mata, amman ni ma ina da nawa laifin, meyasa ban nuna maka haka tun farko ba? Wata kila da duk wannan rudanin be same ka ba”

“Daddy ka yi hakan ne saboda tace ta yafe maka ni, domin ita tana da wasu yayan da suka fi soyuwa a ranta”

“Ameer ko da babu zuwan wannan ranar da ita zata fada maka, ni na san wata rana idan bana raye za'a fada wannan, domin yana rubuce a cikin wasiyar da zan bari, saboda hakki ne da ba nawa ba dole kuma na sauke shi, saboda akwai yan'uwana da suka san da wannan maganar, na tabbatar idan bana raye za a dago maka da wannan maganar, a can ina tunanin kamar idan bana raye abun zai fi zame min kwanciyar hankali, sai dai halin da na ganka ciki a yanzu, ya saka na ji cewar ka san komai a lokacin da nake raye zai fi sauki fiye da bayan raina, domin zafin zai zame maka biyu, amman a yanzu zan iya kula da kai, zan ganka na yi farinciki, domin babu abun da zai canja daga matsayinka na ďana da nake kallonka da shi”

Ya yayinda ya fara cin abincin kamar an masa dole. A lokacin ne Daddy ya aje spoon dinsa ya hade hannayensa yana kallon Ameer.

“Wallahi da za a iya shiga abun da yake zuciya, Ameer da ka kara gode Allah da wannan abun ya bayyana, domin ya kara maka kima da kauna da tausayi a idona, ina jin kaunarka a yanzu fiye da da”

Tsayar da cin abincin yayi ya kalli Daddy.

“Ba dan nasan kudi ba zai siye kudi ba, da na ce kudi matar nan ta baka har ka sauya nan take, wata kila ta siye ka da kalamai ne”

Dariya sosai Daddy yayi.

“Sai kuma gashi kudi baya siyen kudin, ashe wannan ya isa ya fahimtar da kai cewar tunani ne irin na babban mutum mai shekarun da ya isa ya haifeka, kalamai sun yi kadan su siye zuciyata Ameer, ni dai ina da saukin kai da saurin sauka idan na yi fushi ina bude zuciyata na fahimci ciwon wani ba ciwona ni kadai ba, zuwan Mahaifiyarka a gidan nan, ya fahimtar da wasu abubuwan da ada ban fahimta ba, akwai labarai masu matukar tausayi da sosa zuciya a bayan shafin faruwar komai, wata kila da bata ba ni kai ba, da yanzu ban san dadin zama uba ba, ban san zafin rabuwa da kai ba. Ameer bari na fada maka wani abu da ban taba fada maka ba, Mahaifiyarka ta taba ceton rayuwata a lokacin da babu kowa a kusa da ni, da ace bata ceto ni a lokacin ba, da yanzu duk wannan rayuwar ba mu yi ta ba, tana da tsohon cikinka ta gudu daga garin Kano ta tafi wani kauye da yake zaria saboda ta boye cikinka ta haihu a can so that idan ta haihu ba zata bawa Jamila kai ba, baka yi tunanin kauna ta saka ta yin haka ba irin ta uwa da ďa? Zan tafi gurin wani business trip jirgina ya fadi a cikin wani daji da ban san kowa ba, karfen jirgin ya danne ni, mahaifiyarka ita ta taimaka ta fito da ni, ni kadai na tsira a cikin jirgin nan da bata taimaka min ba da ni ma ban rayu ba (Masu makaratu kun tuna lokacin da Zahra ta ceto Mr Bashir a cikin littafin farko CIWON SO?) a lokacin ban samu taimakonta ba saboda ta bar garin tana zubar jini aka kaita asibiti jinina aka saka mata, sai dai tsoron kar ta rasaka ya saka ta sake guduwa daga nan ban san a inda ta koma ba, kudin na na bada a bata ma bata karba ba, ka ga dace kudi ne a gabanta, babu abun da zai hana ta tsaya ta karbi kudin, ban sake ganinta ba sai da Jamila ta aikata abun da ta aikata, sai ya zama nonon Jamila da madara da duk wani nono a duniyar nan baya baka lafiya a ciki, sai nonon Zahra, a dole ta gidan da zama saboda ta samu kusanci da kai”

Ameer ya aje spoon din ya kalli Daddy.

“Daddy abinci ka ce na zo mu ci ba hirar wata ba please”

“Baka yarda da ni ba kenan? You can google it ai tarihi baya boyuwa zaka ga lokacin da hadarin ya faru, Ameer ba ina fada maka wannan ba ne kawai saboda ka sauko daga tudun daka hau, no ina fada gaskiya ne da kuma abun da na fahimta. Da zaka bawa mahaifiyarka dama ka tambaye ta wasu abubuwa wata kila da baka sake yin fushi da ita ba, ni dai na san baka dukan abun da zan iya domin samun farincikinka, shin baka tunanin lokaci yayi da ya kamata ka rama min abun da na yi maka? Ka saka ni cikin farincikin nima? Kai ai kana da sauran lokaci, amman ni na sha ruwa shekaru sun ja, ga kuma ciwo yana yawan kawo ziyara, kar sai bayan bana raye ka ce zaka nuna min kauna, lokacin nan is too late komai ya kare”

Ido Ameer ya kura masa yana kallonsa shi ma kallonsa yake da damuwa a fuskarsa.

“Ba wani abun nake son daga gareka ba, ni dai ina son ganin farinciki a fuskarka, ina son na ga kun shirya da mahaifiyarka, ina son na ga ka sadu da dangin mahaifinka da na mahaifiyarka a lokacin da nake raye da idona, domin mutuwa zata iya zuwa min anjima ko yanzu”

“Me da me ta fada maka lokacin da ta zo gidan nan?”

“Bata fada min komai ba, but i see the pain in her face, i read it in her eyes, i hear it in her voice, ta rasa yarta three days ago Ameer, but she still care for you, bayan kuma you're the reason behind her daughter's death, idan ba uwa ba wace mace ce zata so ka? Bayan mutuwar yarta? Kasan wani abun da ya ba ni mamaki? Zuwa ganinka da ta yi, babu wanda ya fada mata kana ciwo, sai alakar dake tsakanin uwa da ďa ita ta sanar mata. Ban ce dole ka yafe mata ba, ban ce dole ka sota ba, amman ina son na roki wannan amfanar a gurinka, dan Allah ka saurareta a duk lokacin da zata zo maka da wani uzuri ko da na magana ne, sannan ba ita kadai ba, Ameer na dade ina fada maka ka bude zuciyarka ka rika damuwa da damuwar wasu, idan wani ya shiga matsala ka rika jin kamar kai ne a ciki, wannan shi ne imani da soyayya ta musulunci. Daga karshe ina son na fada maka, iyaye komai suka aikata mana basa yin laifi, kashe ka kawai za su yi su yi laifi a gurin Allah, bayan Allah da Annabinsa, babu na biyu sai iyaye, da ace na wulakanta iyayena da ban samu kaina a halin da nake ciki a yanzu ba, da rayuwata bata yi albarka kamar haka ba, ni dai kam ina matukar alfaharin da iyaye, ko da kuwa za su siyar da ni a kangin bauta...”

Daddy na kaiwa nan ya mike tsaye yaja kujera baya, ya zagayo ta inda Ameer yake zaune ya dafa shi.

“Shin baka marmarin sanin waye mahaifinka? Su waye yan'uwan mahaifinka? Miye mahaifinka ya yi kamin ya rasu? Miye ma silar mutuwarsa? Baka son saduwa da yan'uwa da danginsa? This is right time da zaka kyautatawa iyayenka ka samu aljannarka cikin sauki, duk wanda zai fada maka wani abu bayan wannan ba masoyinka ba ne, ai yanzu ne lokacin da ya kamata ka yi hanzarin kwace muhallin duka yayan da Zahra take da su a zuciyarta, kai da ka zama ďan gata mai gida biyu iyaye hudu? Baya fika Ameer? Ka ci abinci lafiya...”

Daddy ya karasa yana bubbuga kafadarsa tare da murmushi sannan ya fice daga dinning din. Ameer ya juya yana kallon mahaifinsa sai kuma ya juyo ya kurawa abincin da yake ci ido, kalaman Daddy nata masa yawo a madafar tunanin da nazari, har ya fara tace su yana sakawa a babin lura. Kasa cin abincin yayi tun bayan four spoon da yayi a dazun duk kuwa da irin dadin da abincin yayi da kuma kasancewarsa favorite food dinsa. Tashi yayi ya fito daga bangaren Daddy ya fito waje ya tsaya yana kallon yadda Allah ya kawata saman da tausarari masu kyau da gaske.

Ya dauki tsawon lokaci a gurin sannan ya shiga parlour ya zauna for few minutes, ya tashi ya shiga dakinsa. Miss calls ya tarar kusan 9 daga number Ummi, daman kai ko da ta kira wayar na hannunsa ba zai yi picking ba balle kuma har yayi calling back. Shi be ga reason din da zai saka ta dame shi a yanzu ba, bayan ta kasa bashi kulawa a lokacin da ya fi bukata. Daddy was right idan zai bukaci wani abu a yanzu to tahirin mahaifinsa ne, not her or her family, ba zai son jin haka daga bakinta ba sai dai abu ya zame masa cilas shi ne tambayarta a ina yan'uwan mahaifinsa suke, a gurinsu yake son samun labarin komai ba a bakinta ba. Yana kokarin jifa da wayar akan gado wani kiran ya sake shigowa a take ya danna rejected. Kamin ya aje wayar sako ya shigo masa.

“Waira ce take son magana da kai, ta takura tana son ta tambaye ka wani abu”

Ya karanta sakon, kamin yayi decided zai dauka ko ba zai dauka ba, kiran ya sake shigowa, sai da ta kusa yankewa sannan ya daga ya saka wayar a hands-free, kuma yaki yayi magana har sai da Waira ta fara magana.

“Allo Ammir”

A dayan bangaren sai Ummi ta matso kusa ta karbi wayar ta saka hands-free saboda ta ji muryar ďanta.

“Ya aka yi?”

“Ina ta kira baka daga ba”

“Yanzu na daga ai”

“Baka son magana da ni?”

“Me yasa na daga wayar to?”

“Gashi nan kana bata fuska”

Ta fada ba dan ta ganshi ba, sai dan ta karanci hakan a muryarsa da yadda yake amsa mata. Ya nufi boutique dinsa ya tsaya gaban madubi yana kallon kansa, da gaske fuskarsa a hade take.

“Zan aje waya sai ka yi far'a sai na sake kira”

Ta fada. Jin haka sai ya saka ya sassauta fuskar yayi ya sauke numfashi.

“Wayar tana kusa da ke ko? Ita tace na ki fada min haka?”

Ummi ta yi saurin girgiza ma Waira kai.

“Aa Ummi tana dakinta”

“Ni na sauko ina falo”

Ya jimmm for some seconds sannan ya ce.

“Me mike son ki tambaye ni?”

“Abubuwa da yawa, na ce Ya Maleek ya kawo ni, sai yayi min ihu wai ba za a sake zuwa ba, kuma idan na sake yin maganarka ma sai ya min duka”

“Saboda shi ubanki ne?”

“Aa shi Ya Maleek ne”

“Baki da alaka da shi ai, ba shi da hujja”

“Shi yaron Ummi ne ai”

“Baki da alaka da Ummi baki da alaka da kowa a gidan nan, so babu wanda zai saka ki dole ko hana ki abun da kike so, idan ma akwai wannan to ni ne, domin ni na dauko ki daga daji, ni ne sikar zuwanki garin nan and that stupid house, remember?”

Ta kalli Ummi sannan ta daga masa kai.

“Yes”

“Good so no one has power over you, tambaye ni abun da kike son ki sani”

Ummi ta yi saurin rada mata a kunne.

“Zaka zo sai na tambaye ka?”

“No”

“Please”

“No”

“Abubuwa da yawa ne, ina son na sani zaka zo saboda ni?”

“Aa”

“Baka damuwa da matsalar kowa kai?”

Yayi shiru, ya saka hannunsa ya taba hancinsa ya runtse ido ya bude.

“Dole sai na zo wai?”

“Eh”

“Zaki iya tambayata a waya”

“Bana so a waya, kai baka da tausayi Ameer ko? Shiyasa ka tafi ka bar ni a lokacin da maciji ya cije ni a daji, ban manta ba i will hate you more”

“Zan zo”

Ya amsa ba tare da shiri ba.

“Yanzu?”

“No”

“Gobe ina zuwa school da safe”

“Zan same ki school din”

“Kasan ina ne?”

“Ki turo min address a waya”

“Okay zan aje waya”

“Good night”

“Good Night”

“Yeah Good Night”

Sai ta sake fada.

“Good night”

“Okay sai da safe”

Sai da ta yanke kiran sannan ya fito daga dakin ya jefar da wayar akan bed, shi yana da alot of questions da zai mata, sai dai hakan ba yana nufi ko da ya tafi ya shiga gidan ba sai dai ya tsaya daga wani gurin ta zo ta same shi.

“Bata manta ba, mata suna rike abun da yayi musu ciwo a zuciyarsu”

Ya fada yana tuna zancen da ta yi masa cewar ya barta a daji bayan maciji ya cijeta.

“Storyteller”

He said, sannan ya nufi bathroom dinsa.



UMMI's POV.

Ummi da mamaki take kallon Waira, bata taba tunanin tana da wayo ba irin yau, a yanzu ta gane Waira ta tashi daga karamar yarinya da take mata kallo zuwa baba mai wayo da basira. Domin bayan maganar farko data rada mata cewar zai zo ta tambaye bata sake ce mata komai ba, ita ta tsara masa komai.

“Baki taba fada mana cewar kin san Ameer ba Waira, ashe shi ya dauko ki ya saka ki a motar Nimra?”

“Ban san waya saka ni ba, amman dai na ganshi kuma ya gan ni, yana kallona a lokacin da maciji ya cijeni na yi ta neman taimakonsa be taimaka min ba har na suma ban san an saka ni a mota ba, ni dai na gani a wani guri tare da Sulem”

Ummi ta shafa kanta ta sumbaceta ta rumgumeta.

“Ina kaunarki Waira, yanzu kin san abun da nake so da ke, gobe idan kin tafi school, school bus ba zata dawo da ke ba, ina son ki roke shi ya kawo ki gidan nan, na san zai yi domin na lura kina da wani sirri a muryarki da mu'alamarki dake karya duk wata izza da fushi ko girman kai a gurin namiji, daman ko wace mace da yadda Allah ya halicceta, kin ga ni da ina kamarki farinjini na yi sosai da kiriniya, step father na ya sha wahala ta a lokacin har karyashi an yi saboda ni, Mamana kuma ba a magana Allah dai yayi mata rahama (Lallai kam dan mahaifin Deen da Deen sun sha duka saboda Zahra)”

Waira ta amsa.

“Toh Ummi, amman Ya Maleek ba zai yi ihu ba?”

“Ba zai yi ba, babu abun da nake bukata a yanzu kamar kusanci da ďana”

Ummi ta dago Waira daga jikinta.

“Gobe zan miki cake mai dadi ki tafi da shi”

“Okay”

Ta nufi upstairs tana jindadi zata ga Ameer a gobe ta yi masa tambayoyi akan abun da ya shige mata duhu.

She wake-up early saboda ta kwana rumgume da baby rabbit dinta da kuma tunanin haduwarta da Ameer. Tun asuba ta sauko kasa da zomonta ko wanke baki bata yi ba, ta nufi kitchen domin ta san Ummi ke shirya mata abun zuwa makaranta kuma tun da har ta fadi cewar zata yi mata cake. Ta leka Kitchen din kamar yadda ta saba sai ta samu Ummi da Mahmood a ciki yana taya ta aiki. Da kuzarinta ta shiga Kitchen din.

“Laaaa”

Ya juyo ya kalleta yana murmushi.

“Laa zaki ce yau ni nake taya Ummi aiki ko?”

Ya daga kai.

“Daddy ne ya raba mana aiki, yace yau idan na gobe Maleek ne, jibi Namra gata kuma ke, haka zamu yi ta yi har mu saba”

Ta juya ta kalli Ummi.

“Ummi Good Morning”

“Good Baby tafi ki wanke fuska ki yi wanka, zan hada miki tea yanzun nan kamin cake ya zama ready”

“Okay”

Ta juya ta fito daga kitchen din ta nufi stairs. hakan yayi daidai da shigowar Maleek falon, daman idan ya gama sallah azuba baya tashi a masallaci sai ya gama azkar dinsa, sannan yake shigowa gidan. Tsayawa ta yi sai da ya iso inda take ta gaishe shi kamar yadda ta Ummi ta koya mata.

“Good Morning”

Tsaye yayi yana kallonta sai ta sauke idonta kasa.

“Morning”

Ya amsa sannan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login