Showing 108001 words to 111000 words out of 281271 words
wanda nake so”
“Enough Nimra....! Mind you ina lallabaki ina daga miki kafa ne saboda kar damuwar ta yi miki yawa, amman ba kiji na fada miki ba zaki auri Ameer ba, ko da kuwa shi kadai ya rage a duniyar nan, ko zaki gudu ki tafi wani gurin idan ma wannan ne abun da kike da kuduri har yanzu to ki daina, gurin kowa zaki je ko ki kai kararmu ba za ki auri Ameer ba”
“Saboda me?”
Nimra ta tambaya a tsawace sai Ummi ta daka mata tsawa.
“Saboda Addinin Musulunci ya haramta aure a tsakaninku”
“Ta ina? Ummi kin san me kike fada kuwa? Ameer fa musulmi ne, ba kafiri ba. Duk wank abun da zaki fada ba zai hana aure a tsakanina da shi ba, matukar ba gawata kike son gani ba.”
“Saboda Nonon da Ameer ya sha ya saki shi kika kama kika sha har na yayeki, yadda aure yake haram a tsakaninki da Maleek haka ya haramta tsakaninki da Ameer”
Nimra ta yi murmushin takaici, abun is some how amman ta san wannan duk shiri ne
“Ta nan kuma kuka bullo...?”
Ummi ta dauke ta da mari.
“This is Reality Nimra ki dawo hayyacinki... Wai so kuke ku haukata ni?”
Ta fashe da kuka.... Nimra kuma ta dafe kunci tana kallon Ummi...
[6/17, 10:57 PM] My S Line: *Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
36
Kallon da ya fi kama da na ga mahaukaci Namra ta fara yi mata ganin ta zo a guje ta rumgume mata bako.
“Yarinyar nan fa bata da hankali”
Ta fada ta karasa inda suke zata janyo Waira da kafafuwanta ke lake da na bakonta sai Shuraim ya ja baya ya girgiza mata kai yana murmushi kana ganin fuskarsa ka san farinciki a ciki shimfide. Waira ta dago ta kalleta sai ta saka hannunta ya shafa fuskarsa ta ja kumatunsa har sai da ya kyalkyale da dariya mai sauti, ita ma ta fashe da dariyar ta kara rumgume shi kam kam kamar za a kwace mata shi, ta kasa yarda Shuraim din ta ne, mutumen da bata taba tunanin zata sake ganinsa ba a rayuwarta, mafarkin be taba kawo mata zai dawo gareta ba.
“Baby Girl”
Namra ta kalleshi da yanayin mamakin da kuma kufula da kishi a lokaci daya na rumgumar wata macen da bata san alakarsu ba. A zatonta ita yake kira shi kuma da Waira yake ita ma Waira ta san da ita yake domin a zatonta ita kadai ce yake cewa Baby girl. Ta sauke kafafuwanta ta sauko tana rike da hannunsa dayan hannunta kuma tana nuna masa zoben dake wuyanta.
“Sulem... Your ring”
Ta saka hannu ta rika zoben yana dubawa fuskarsa dauke da murmushi. Hakan yayi daidai ta fitowar abokinsa dake cikin motar ya nufo su yana murmushi with confused a the same time.
“Ban taba tunanin zan sake haduwa dake ba, lokuta da dama ina tunaninki na ce yanzu ko ina yarinyar nan take, tana raye ko mace ko wani abun ya same ta, wata kila saboda hankalina ya kara kwanciya Allah ya sake hada mu so that na ga yadda kike rayuwa”
Maganar yake kallon idonta masu matukar daukar hankali.
“Sulem.... Ina son Sulem.... So much so much”
Tana fada tana juya kai wani kalar farinciki da nishadi ne a zuciyarta da baya misaltuwa. Shuraim ya saka hannu ya taba fuskarta gaba daya ta bata masa da masoyiyarsa Namra dake gurin farincikin sake ganinta ya mantar da shi cewar shi suriki ne a gidan.
“Kin yi kyau sosai, kin canja Waira kamar bake ba”
Ta yi murmushi ta sake rumgumeshi, a nan ya dago sai suka yi ido hudu da Namra da fuskarta ke hade sai ya dan rage murmushin da yake yaja baya ta cire jikinsa daga Waira, abun ka da mai dauki sai ta kama hannunsa ta saka cikin nata ta sarkafe.
“Waira”
Ta juyo jin an kira sunanta a tsawace ta kalli saitin katon windows din falon Ummi da aka bude ta kalli Maleek dake tsaye.
“Shigo ciki...”
“Sulem ne...”
Sanin kamar ba zai maimaita mata furucin ba ya saka ta saki hannun Shuraim idonta na cika da kwalla.
“Sulem karka tafi...”
Shuraim da abokinsa sun dauke idonsu daga kallon Maleek, Shuraim ya kalli Waira yayi mata murmushi.
“Ba yanzu zan tafi ba, idan kuma zan tafi zan miki magana je ana kiranki”
“Aa ka zauna duka a nan please Sulem...”
“Shuraim...”
Ya gyara mata, a kokarinta na gyarawar sai ta sake furta sunan a yadda take fada.
“Sulem....”
Yadda ta kira sunan ma ya masa dadi, sai kawai yayi murmushi ya kalli Namra da har lokacin ta saka sakim fuska.
“She's my patient”
“Just...”
Ta tabe baki tana yatsina fuska kamar ta ga abun kazanta. Murmushi kawai yayi ya duba agogon hannunsa kamin ya kalli abokinsa da shi mamakin yake ya ce.
“Ma maybe ka manta ta amman na sha baka labarinta”
Abokin ya dan yi murmushi be ce komai ba sai kallon fuskar Namra yake yana karantarta. Ba dan kar yace ta wulakanta shi ba da a gurin zata barshi tsaye, for which reason zai rumgume wata a gabanta, at first ma ta dauka wata alaka can sai bayan sun gama murzar juna zai ba fada mata cewar patient dinsa ce.
“Bismillah....”
Ta masu ishara da hanyar part din Abiey.
“Na dauka wata alaka ce mai karfi a tsakaninku”
Suna tafiya ta fadi haka sai ya kalli yanayinta ta da ya canja ta kasa sake fuska har lokacin. Murmushi yayi ya juya ya kalli kofar part din Ummi inda Waira ta shiga ya sake juyo suka cigaba da tafiyar.
“Wata kila kina nufin alakar jini, amman a gurina alakar da zaciya zata samu samu kwanciyar hankali idan ta san wanda take tausayi yana cikin koshin lafiya ita ma wata alaka ce mai karfi, da kin san yadda na damu da aka dauko yarinyar aka ce za a zo da ita Abuja, da kin taiyani murnar ganinta da na yi a gidanku, ko ba komai na san zata samu kwanciyar hankali da tsoro a nan”
“Haka ne ina taya ka murna Congratulations Sulem”
Ta fada tana dariyar yake, a badini bakar naganar ce ta yi masa, sai dai shi kuma be fahimta ba domin be fashinci komai ba. Iyakar kokarin da ta yi na danne abun da take ji a zuciyarta ne ta kula da shi yadda ya kamata sai dai duk wani dauki da murnar da take na zuwansa ya ragu a ranta.
Kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki haka Waira ta shigo falon da kofarsa take bude tun a fitar da ta yi da gudu bata tsaya rufe kofar ba, maida kofar ta yi ta rufe sai ta tsaya jikin kofar tana taba hannunta ganin fuskar Maleek a hade.
“Ba ki da hankali? Ta yi bako ya zo gurinta kije kina ruining abun da ta shirya, ji yadda kika fita da gudu kafafuwa tsil tsil kamar tsuntsuwa, ku a garinku ba ku da tarbiyar girmama bako ne? Haka ake tarbon bako?”
Yana mata fada tana turo baki daman tuni hawaye ya cika idonta domin bata so rabuwa da Sulem dinta ba, gashi kuma yanzu ya tsare ta da fada. Takawa ta fara yi ta bi ta gabansa zata sai ya daka mata tsawa.
“Ba magana nake miki ba shi ne zaki wuce”
Zabura ta yi ta hawayen dake makalle a idonta ya sauko saman kyakkyawan kumatunta, hakan kuma ba karamin kyau ya kara mata ba, dana da kwarjinin da har kuka kyau yake mata idan tana yi.
“Sulem ne ai”
“Ba Sulem ba sule, ina kika sanshi?”
Ta kai hannu ta rika sarkar wuyanta ta soma magana muryarta na karkarwa irin wanda kuka ke daf da subucewa.
“Ya bani wannan ya saka min”
“Miya faru?”
Mahmood dake saukowa stairs ya tambaya ganin hawaye na sauko mata wasu na bin wasu.
“Wallahi yarinyar nan bata da hankali yau na gani, wanda zai auri Namra ne ya zo sai kawai ta tafi ta rumgumeshi baka ga yadda Namra ta bata rai ba, idan ba hauka ba ina aka taba haka”
“Toh ai Sulem dina ne”
Ta fada tana kuka. Mahmood ta sauko gaba daya ta tsaya inda take.
“Wane Sulem”
“Sulem”
Ta nuna masa sarkar wuyanta.
“Oh na gane kai ta san shi fa, idan bata san shi ba ai ba zata je haka nan ta rumgume shi ba, ka gane Sulem din da take yawan magana, aiko ni ma zan so ganinsa ko dan na ji inda suka san juna tun da bata fada mana ba, waya sani ma ko ďan'uwanta ne”
“You miss the point ko yaya ne be kamatadaga ganin mutum an gayyato shi kije ki rumgume shi ba, wannan ai rashin tarbiya ne da sanin ciwon kai, she's so annoying sai ta rika yin abu kamar wata yar jaririya”
Mahmood ya zauna.
“Maybe daukin ganinsa take kuma ita ai ba musulma ba ce wata kila al'adarsu haka ake tarbon mutum”
Tsaki yayi ya nufi hanyar fita daga falon, Mahmood ya bishi da kallo baki saki, sai a yanzu shi ma yake mamakin sbun da Maleek yayi kamar ba shi ba, da can babu ruwansa da duk wani abun da ya shafi Waira, wata kila saboda kanennsa ba su taba rumgumar wani a gaban idonsa balle ace ya tsawata musu ita kuma ya ga ta yi dole yayi mata fada. Maleek be duba yiyuwar akwai alaka tsakaninsu ba, shi dai abun da idonsa ya gane masa ne be masa dadi ba, domin be ga dalilin rumgume mijin da kanwarsa zata aura Da Waira ta yi ba, yanayin yadda ya ga fuskar yar'uwarsa ta sauya baya tarin farincikin data wuce ta gabansa ta fita da shi ya sosa masa rai, wata kila yana taya yar'uwarsa kishi ne, ko kuma yana ganin rashin dacewar hakan da gaske. Bayan fitar Maleek Mahmood ya kalli Waira yayi murmushi
“Karki damu, haka yake takurawa kowa a gidan nan kin san halinsa ai ko?”
Ta daga kai.
“Ina son na tafi gurin Sulem”
“Yanzu ki bar shi ya huta tukuna, idan ya huta zamu tafi gaba daya har Ummi mu gaisa da shi sai ki sake ganinsa, yanzu zauna ki ba ni labarin i da kika san shi”
Ta zauna a kasa sai dai ta kasa labarta komai, sai tabin sarkar wuyanta take idan ta dago ta kalleshi sai ta yi murmushi kamar ba ita ce hawaye ya gama yi mata zuba ba.
“Toh shiga ki fadawa Ummi kin ga Sulem tun da ba zaki ba ni labari ba”
Ta mike tsaye da sauri daman abun da take nema kenan, da gudu ta hau stairs din kamar zata zame ta fado ta tura kofar dakin Ummi ta shiga sai ta samu bata cikin dakin, fitowa ta yi ta nufi dakin Nimra ta tura idan bata samu Ummi ba ai zata iya labarta Nimra sai dai tararda da ita da ta yi tana kuka ya saka jikinta yayi sanyi sai ta juyo ta fito ba tare da tace mata komai ba. Dakinta ta nufa tana shiga ta sami Ummi da Dr Zainab a dakin zaune Ummi tana hawaye. Take kwarin guiwar data shigo da shi ya mutu sai ta tsaya jikin kofar tana kallon Ummi.
“Waira kin san shi ne?”
Ummi ta tambaya cikin karfin hali domin bata manta dazun data fita daga dakinta tana fadin Sulem ba. Wannan ne karo na farko da Waira bata damu da tambayar ko son jin dalilin Ummi na kuka ba, ta karasa cikin zumudi ta fara fada mata abun da zata iya tunawa a game da Shuraim. Sannan ta nufi gurin data aje tsofin kayanta na fata na ainahin garinsu ta bude ta dauko takardar da yayi mata rubutu a jiki ta nunawa Ummi.
“Ya ba ni wannan da babaken mutane za su kawo ni Habuja”
Ummi ta karbi takardar ta bude.
‘Ban san iya inda tafiya zata dauki be, ban san iya inda kaddara zata tsaya da ke ba, ban san yaushe Allah zai sake gadamu ba, a duk inda zaki karance ina fatar guri ne mai aminci da natsuwa. Ya kai wanda zai ci karo da wannan sakon ka ji tsoron Allah karka cutar da ita, fruits ne abun da ta fi ci, kuma ta tsoro da rashin sabo da mutane da wuri, Allah ya tsare ki
Dr Shuraim...’
Ya rubuta daga karshe, Ummi ta mikawa Dr Zainab takardar ita ma ta karanta sannan Waira ta karba ta nade a hannunta ta tashi tsaye ta fito dakin, so take ta je ta nunawa Sulem bata jefar da takardar da ya bata ba, tana nufo Stairs ta fara saukowa dai ga Maleek ya fara haurowa sai ta juya da sauri ta koma. Mahmood dake zaune yana hangen abun da ke faruwa ya saka dariya yanayin yadda ta juya ta koma din da sauri ya nuna tsoron Maleek take. Bata shiga dakinta da Ummi take ciki ba sai ta shige bedroom din Ummi da babu kowa a ciki a zatonta Maleek zai yi magana da Ummi ne ko kuma dakinsa zai tafi. Tsayawa ta yi a dakin tana sauraren idan ya wuce sai ta fito, shi kuma hango Ummi da yayi a dakin Waira kasancewar kofar a bude take, sai yayi reverse ya dawo baya. Kamin ya tura kofar dakin Ummi sai Waira ta bude masa a zatonta ya wuce ita kuma ta fito, ita da shi duk suna rike da kofar ne, ita zata bude ta fita shi kuma zai tura ya shiga. Sakin kofar ta yi ta matsa baya shi kuma ya samu damar shigowa ya rufe kofar. Ba saboda ita ya shigo ba amman hakan be yana shi yi mata ishara data zauna da ido ba. Ta nufi gefen gadon Ummi ta zauna a kasa tana kallonsa da idanuwanta da ya fi tsana a yanzu domin haushi take ba shi, ta boye takardar hannunta a bayanta ta matse gadonta ta natsu sosai irin natsuwar nan ta tsoro. Yau wardrobe din Ummi ya nufa ya bude ya fara dubawa a hankali domin ita kadai ce be bincika na a kwana uku da ya kwashe yana bincikar ďakin a duk lokacin da ya samu sa'a Ummi bata ciki, yadda yake bin komai a sannu yana maida shi mazauninsa a yadda ya taba shi sai ka rantse da Allah criminal ne da ya kware a sata. Ita dai Waira kallonsa kawai take kamin ta mike tsaye ta nufi inda zomonta ya leko ta dauke abunta ta rike. A hankali ya rufe wardrobe din sannan ya juyo ya kalleta tana shafa zomon tana kallonsa. Ya bude dayan side din ya fara dubawa daga samna gaba daya akwati ne da Ummi ta saka a gurin. Hankali kwance ya bude akwatin yana saka yadda zai fadawa Ummi cewar Waira ce ta ce ya duba mata tufafinta a gurin, tufafi ne sabin da ba a dinka ba a ciki lace da atamfa kasan kayan kuma wata karamar jaka ce irin ta saka takaradu, sai da ya cire kayan sannan ya dauko jakar dake lake da karamin makulli, aje jakar yayi ya maida akwatin da ya rufe sannan ya rufe wardrobe din yana ta mamakin me ke ciki fatansa dai ace abun da yake nema ne, domin ya duba gun da Ummi ke aje takardunta be samu komai a gurin ba. Sai da ya gama ya dauki jakar ya nufi kofa sai kuma ya juyo ya kalli Waira.
“Sauran na ji kin ce na dauki wani abu, na cire miki ido”
Yana maganar yana zare mata ido, ita dai idon kawai ta sakar masa har ya fice, sai da ta ba shi mintunan da take kyautata zaton ya isa ya boya sannan ta nufi kofar ta bude ta fito tana sanda ta sauko kasa, sau daya ta kalli gurin da Mahmood yake zaune ta dauke kai bata ce masa komai ba, shi ma kuma be ce mata ba har ta fice. Harabar gidan ta fara kallo tana rabon ido bata san inda ya shiga ba balle ta bi shi, sai dai ta ga motar da ya shigo dan haka ta nufi gurin motar ta tsaya tana leka ciki ganin babu kowa ya saka ta zauna a gurin ta jingina da motar, a wayonta duk inda suka a cikin gidan dole idan suka fito za su tafi zata gansu ai idan tana gurin.
NAMRA POV.
Namra ta yi musu tarba irin wacce ta dace da mosoyi ita da Yesmin da Hanne suka jera musu abubuwan da aka shirya musu. Zaman minti talatin da ta yi a falon sai da ya fara bata labarin haduwarsa da Waira, a iyakar gaskiyarsa ya jidadin ganinta kuma ya kasa boye hakan, ita dai bata ce masa uffan ba akan Waira ba har ta fita ta ba su guri domin cin abinci.
“Dr zaka kufular da yarinyar nan fa, taya zaka rumgume wata budurwa a gabanta kuma ka zo kana ta bata labarin haduwarku?”
Dr Shuraim ya aje kofin lemun dake hannunsa.
“Haba karka min kuskuren fahimta mana, Namra ba yarinya ba ce ai tasan kanta ba zata ce kishi take akan haka ba, kuma ni ba son wannan yarinyar nake ba, kawai dai ta shiga raina ne sosai dan zaman da muka yi na kwana biyu daga asibiti zuwa gidanmu Allah ya sanya shakuwa a tsakaninmu, baka lura ita ta yi tsalle ta rumgume ni ba?”
“Eh amman mace bata son ko kwalliyar wata macen ka yaba a gaban wata fa, kai baka lura yanayinta ya canja ba, kuma ka zo kana ta son dole sai ka fada mata yadda kuka shaku”
Shuraim yayi murmushi.
“Kamal kana nufin kishi take? Ai dalili ake ma kishi da ace ganin ta yi nace jna sonta shi ne zata yi kishi”
“Ka dai kiyaye kar garin neman gira a rasa ido, kuma karka manta abun da ya kawo ka a gidan nan”
“Ba zan manta ba, ni da na dade ina jiran zuwan wannan ranar, kuma zan manta a yau? Kaima tunaninka ne ya baka wani abu amman babu abun da kake tunani a zuciyata”
Be sake cewa komai ba, ya bude fruit salad. Shuraim be ci komai ba bayan lemun da Namra ta zuba masa ya sha, Kamal ne kawai ya ci abinci shi ma kuma ba sosai ba.
[6/17, 10:57 PM] My S Line: *Littafin WANI GARI na kudi ne biya