Showing 177001 words to 180000 words out of 281271 words

Chapter 60 - Wani Gari Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1268

ba, if not she will talk ta fada masa bata so. Ganin damuwa a fuskarta har idonta ya fara tara kwalla ya saka ya rika hannunta ya sumbanci hannu ya shafa goshinta zuwa saman kanta sannan ya sauka saman gadon ya fice daga dakin, mamakin abun da yayi mata ya hanata bachi har karfe 4am na asuba, sai 4:30 ta sake komawa bachi, bata farka ba sai da Ummi ta shigo ta tasheta, sannan ta tashi ta yi shirin makaranta ta sauko tana sanye da uniform dinta tana rike da jakarta ta makaranta. Idonta na kan Maleek dake shan ruwan sanyi tun da farar safiya har ta sauko ta isa dinning.

“You didn't greet him”

Waira ta daga kai tana masa wani irin kallo da ita kadai ta san manufarsa ta gaisheshi. Kamar kar ya amsa mata sai kuma zuciyarsa da baki suka ki bashi hadin kai har sai da ya amsa din. Ummi ta aje mata komai na karyawa sannan ta aje mata lunch box dinta a gefen kujerar dake fuskantar wadda Maleek yake zauna.

“Baki gaishe da Namra ba”

Ummi ta fada, sai a lokacin ta lura da wata Namra a gurin, domin tuni tunaninta ya tafi akan abun da ya faru a tsakar daren jiya.

“Ina kwana Yaya Namra”

“Lafiya Kalau”

Ta amsa sannan ta dauki kofin tea ta ta bar dinning din domin ta gama bata karin, a nan Waira tace waye tv na ba Maleek, kallonsa take kamar zafa fada cikin idonsa, duk dagowar da zai yi da wani motsi yana kan idonta ta ma kasa taba komai a abin karyawarwa da Ummi ta aje mata, tun be kula da kallon ba har jikinsa ya bashi cewar kallonsa take, dan haka ya dago idonta da nashi suka yi tarayya da juna, a madadin ta dauke idonsa sai ta cigaba da kallonsa. Zuciyarsa ce ta fara raya masa kallon da take masa ba na Allah da Annabi ba ne, dan haka ya sake kallonta.

“What?”

Ya tambaya da wata murya can ciki, sai ta dauke idonta domin bata da amsar bashi. Kadan ta sha tea ta mike tsaye tana duba agogo dakin dake nuna 7:30am.

“Ummi zamu wuce makaranta, Ameer be tashi ba?”

Maleek ya hade tea dake bakinsa da karfi, yana jin kamar an daka masa wani mashi a zuciya, why ma ya zauna yana karyawa at this early morning abun da ba halinsa, mikewa yayi tsaye yaja kujera baya ya fice daga dinning din.

“Be farka ba, ni kuma na kyale shi yayi bachinsa ne saboda shi ne first bachinsa a gidan nan, kuma idan ma ya farka this time around me zai yi? Ai kara yayi ta bachinsa, idan ya farka zamu tafi tare anjima na duba matar nan da ta yi accident, shiyasa na hada komai tun a yanzu kuma ina son kamin ya farka na gama shirya masa komai na karyawa even though ban san favorite dinsa ba”

Ummi ta fada tana dire flask din ruwan zafi daya banbanta da sauran Flask din da suke gurin. “Zan tafi na san school bus ta iso a yanzu”

Ummi ta zagayo bangare da Waira take tsaye ta sumbanci goshinta.

“Allah ya miki albarka a dawo lafiya, ki dauki lunch box dinki, na ga baki ci komai ba ma”

“Okay”

Ta amsa sannan ta dauko lunch box din, kiss din da Ummi ta yi mata yana tuna mata da irin kiss din da Maleek yayi mata a daren jiya. Ummi kuma ta yi tsaye tana kallon Waira fuskarta da murmushi har ta fice, ta juya zata koma kitchen sai ta ji jiri ya kwasheta, ko wane gaba na jikinta ya fara rasa kamar ana dukan kashinta, da sauri ta dafa dinning din ta zauna a hankali har sai da abun ya sake ta sannan ta mike tsaye cike da karfin hali ta nufi kitchen din domin karasa abubuwan da take son shiryawa Ameer.



****** ******** ******* *******

Ummi bata samu zuwa duba matar da Ameer ya fada mata tana asibiti da safe ba, sakamakon kiran da Mummy ta yi masa ta sanar masa ta yi aika musu da breakfast, shi kuma ya sanar da Ummi a lokacin da ya sauko kasa domin yin breakfast. Ganin Mahmood a dinning make him feel uncomfortable, but ga mamakinsa sai Mahmood ya mika masa hannu suka gaisa sannan ya tashi daga dinning din yana fadin.

“Bari na baka guri ka karya kamin ka saba da mu”

Ameer dai be ce masa uffan ba, ya cigaba da kallon kalolin breakfast din da Ummi ta shirya masa tare da taimakon Hanne.

“Ban san favorite dinka ba, shiyasa na girka wadannan ina fatar za su maka dadi”

Ya mika hannu ya dauki plate sai ta rigashi ta dauka tana tambayar abun da yake so. Da haka ta yi feeding din yaronsa cikin farinciki da jindadi da ya kasa boya a zuciyarta har sai da ta zauna ta saka shi a gaba da kallo har ya gama cin abinci.
Dakin da zai iya kira da shi ya shiga ya yi wanka ya shirya sannan ya fito falon jiran Ummi, a kokarinsana rage zaman banza ya saka shi tashi ya fara zagayawa a falon yana duba kofafin da suke falon da kuma ta inda suke bullewa, ya leka Kitchen da kofar baya, tsakar gidan dake gefen hanyar dinning ma sai da ya duba sannan ya fito compound yana kallon tsarin gidan. Shi dai ya san zai daurewa kansa ne kawai ya koyawa zuciyarsa a zaman inda bata sani ba har ta saba, domin rayuwa a inda baka tashi ba, da kallon mutanen da baka sani ba a matsayin iyayenka abu ne da sai an jure. Isarsa gurin expensive car dinsa yayi daidai da fitowar Ummi ciki shiga ta alfarma. Kamin ta karaso gurin ya kawa motar key ya bude mata back seat yana jiran isowarta. A take murmushin ya fadada fuskarta wannan ne second joy dake samu a gurin Ameer bayan cin abincinta driving dinta ma wani abu ne mai muhimmanci a gurinta. Ta shiga motar ta zauna ya rufe ya bude side dinsa ya shiga yayi ma motar key.

“Mu tsaya a wani gurin ina son na siye musu wani abu”

“Karki damu suna da komai a asibitin”

Ya amsa mata daga haka bata sake magana ba, shi ma be sake yi ba, yana son ya tambayeta wani abu game da Waira kuma ya kasa. Tafiyar 40min ta iso da su Hikima Hospital, kamin ta bude ta fito ya bude mata sai ta sauko tana jin wani honour, bayan ta fito ya rufe motar ya wuce gaba tana binsa a abaya har suka shiga cikin asibitin. Shi ya fara tura kofar dakin da Tsohuwar take ya shiga sannan ya rikewa Ummi kofar ta shigo, ya maida kofar ya rufe a hankali sannan ya taka ya isa gurin gadon da tsohuwar take Humaira ta mike tsaye kamar yadda ta saba idan ya shigo bata zama balle kuma yau da ya zo da bakuwar fuska.

“Sannunku da zuwa”

Ta fada cikin girmamawa, Ameer ya amsa mata da hannu yana yi ma tsohuwar ya jiki, sai ta amsa masa hankalinta na tafiya gurin Ummi da ita ma kallon tsohuwar take tana kallon Humairah with shock and surprised. Akwai tsufa da sauyin yanayi na rayuwa a jikin tsohuwar da bata saka ran tana raye ba idan har ta tabbata ita din ce. Sai dai kammanin Bahijjah da Deen da suke a fuskar Humairah suna kokarin karfafa mata tunanin kwakwalwarta. Hannu ta kai ta rike karfen gadon dake gurin kafafuwan Tsohuwar ta runtse idonta gam. Tsohuwar ma kallonta take baki sake tana kokarin tantance abun da idanuwanta suke nuna mata madafar tunaninta take tariyo mata, Ameer ya dan karkarta kadan ya kalli Ummi ya kalli tsohuwar sannan ya kalli Humairah da ita ma kallon rashin fahimta take masa, domin sun rasa gane dalilin Ummi ya rike karfen gadon da karfi ta runtse ido, tausayin tsohuwar ne? Ko kuma na rasa saka ran ciwon ya kai haka ne? Duk ba su canki ko daya ba.
[7/20, 10:33 PM] My S Line: 58

“Ummi are you okay?”

Ameer ya tambaya yana kallonta, kamar wadda ta tsorata haka ta bude idon da sauri, hawayen dake makale a idanuwanta suka samu damar saukowa saman fuskarta.

“Bismillah zauna a nan Hajiya”

Hunairah ta fada tana kallonta domin ta fahimci ita ce matar da Ameer ke bata labarin tana ikirarin ita uwarsa cw ta hanyar sunan da ta ji ya ambata kuma ta ganta a lokacin da suka zo tafiya da Nimra. Ummi ta cira kafa ta taka sai jiri ya dibeta ta yi baya kamar zata fadi har sai da Ameer yayi hanzarin rikata.

“Are you okay”

Ta dan kallesa jin wani abu mai kamar yana a ido ya sska ta ganinsa dishe dishe-dishe.

“Taimaka min na zauna Ameer”

“Okay”

Ya rikata da kyau, Humairah ta dauko kujerar da sauri ta aje mata, Ameer ya taimaka mata ta zauna.

“Ummi lafiya? Ko ciwon ne ya tashi?”

Ta kalleshi a cikin halin da yake

“Waya fada maka ba ni da lafiya?”

“Waira ta fada min komai”

Ummi ta bude baki da dan mamaki sannan ta rufe ido ta bude ta kalli Tsohuwa ta karata da sunan da zai kara tabbatar mata idan ita din ce.

“Hajiya ina Bahijjah?”

Wacce aka kira da Hajiyar ta yi ma Ummi kallon neman sani da fahimta, ita dai ta ga kamar ta san Ummi sai dai kammanin ya canja gaba daya, sai dai mamakin tambayarta ta san Bahijja ya gagara boyuwa a fuskarta.

“Bahijja tana hanya bata karaso ba, amman tana nan zuwa ga yarta nan dai Humairah, Hajiya sai na ga kamar na san ki amman fuskar ta canja”

Humairah da aka nuna ta sakarwa Ummi ido jin an ambaci sunan mahaifiyarta, ga hawaye sai saukowa yake a idon Ummi kamar ba gobe.

“Kin san ni mana Hajiya...”

Kuka ya ci karfin Ummi ta kasa karashe maganar, Hajiya ma ta sake yi mata duba na tsanaki.

“Ko dai Zahra ce Zahra matar Abiey tsohuwar matar Zaharardeen? Na ga fuska amman tsufa ya kai kar na fadi ba daidai ba, shekara ashirin da biyar rabona da ganinta, wata kila ma har da doriya, tun akwai sauran kurciya”

Ummi ta saka hannu ta dafe fuskar tana mamakin yadda Ubangiji yake tsara al'amurransa, ya hadata da kowa ta inda bata yi tsammani ba, tun daga kan Ameer ga kuma Shuraim yanzu kuma ga Hajiya. Cikin kuka Ummi ta ce.

“Ni ce Hajiya, idonki be fada miki karya ba, shekaru sun ja na sani, tun yarana suna tasawa gashi yanzu har sun girma”

“Allahu Akbar ashe Allah zai sake sada fuskokinmu Allah da girma kake”

Fadar Hajiya tana girmama Ubangiji, Humairah da Ameer kam kallo kallo kawai suke domin ba su fahimci komai a cikin abun da Ummi da Hajiyar suke tattaunawa ba. Cikin kuka Ummi ta ce

“Yaushe kika bar Kano Hajiya?”

Hajiyar ta sauke ajiyar zuciya tana murmushin takaici.

“Labari ne mai tsowa Hajiya Zahra, rayuwa ta yi mana wahalar zama a kano, tun bayan rasuwar Malam, sai na zama bani da kowa na kusa ai dangi da yan'uwa, kuma ba abun ka dauko ďan wani ya zauna tare da kai ba, saboda kai talaka ne ba kowa ke son zama kusada talaka ba, ina tunanin ai kin san auren Bahijja”

Ummi ta daga kai tana kuka sosai.

“Toh sai ya zama, jarabawa ta shiga, dan kasuwanci da yake abun be karbe shi, har ta kai ya bar garin Kano ya dawo Abuja da zama saboda ya biyo abokinsa nan suna sana'ar siyar da Nama, kuma a nan sai Allah ya amsa masa ya samu bude sosai har ma ya kama haya ya dawo da Bahijja a nan, kuma ita ma sai ta zama kamar ni haihuwar ba mai yawa ba ce, shi kuma mijin Allah be mishi tsawon rayuwa ba, yana zuwa kano duba iyaye da yan'uwa yana zaune a Abuja yana dan tana kasuwancinsa, sai gashi ya hadu da hatsarin mota lokaci yayi, a madadin ita Bahijja ta koma gida da zama sai Iyeyen mijin suka ce me zai hana na zo na zauna tare da ita tun da bata da kowa a nan zata ji sanyi, saboda an fi son mace ta yi takaba dakinta, ni kuma daman haya nake a Kano, tun bayan rasuwar Malam yan'uwansa suka siyar da komai har dan gidan da kika siya mana, aka raba gado aka ba ni na wanka na, kin san ba ni da namiji, tun da Margayi Zaharardeen ya rigashi Ratsuwar dole za su ci gadon dan'uwansu, ni da Bahijja abun be yi mana auki ba, daman gado ba shi da albarka sai wanda ya dauki bakin wuta”

Hajiya taja numfashi ta sauke sannan ta cigaba tana fadin.

“Shiyasa ban musa musu ba da suka ce dawo, sai na hada yan komatsaina na dawo, bayan ta gama wanka kuma sai muka cigaba da zama nan, kin san yadda zaman yadda zaman gidan wani yake idan ba gidanka ba, ko kuma gida mai wadata ba dadi kake ji, kuma da ma ace a cikin yaya akwai wani a can dole na kwasheta mu koma, ita kuma ta dan sabada nan din shiyasa tafi son zama a nan, saboda tana dan kasuwsncinta kamin abu ya zama yadda ya zama a yanzu, ga kuma karatun yara, kin ji yadda aka yi muka dawo nan da zama, amman ke ai na san tun da kika je mana bankwana nan da zama ko?”

Kai kawai Ummi ta iya dagawa sai kuka take kamar wata criminal. With confused and tunanin ta wani bangaren Ameer ya dubi mahaifiyarsa ya ce.

“Why are you crying?”

“Dole ta yi kuka, aba yau ba ne wata kila ta tuna baya”

Hajiya ta amsa masa itama nata idon na cika da hawaye. Sai Ummi ta tari numfashinta.

“Ba baya nake yi ma kuka ba Hajiya, kukan na yanzu ne, abun da na aikata nake tsoron yadda za ku kalli abun, nake tunanin yadda za ku karbi abun”

Hajiya da bata fahimci komai ba ta ce.

“Baki mana komai ba sai alheri Zahra, in ma bake ba wace matar ce zata siyawa iyayen tsohon mijinta gidan ta kai Ubansa makka ta bawa uwarsa jari? Ba ďa ba jika? Aikin mana ya ni ba abun da kika min Wallahi kin g....”

Zuwan wani tunanin ya tsayar da halshen Hajiya daga sarrafa kalmar da zata fito daga bakinta, sai ta yanke maganar tana kallon Ameer da yayi baya ya jingina da kofa, shi ma kallon Hajiyar yake cikin wani yanayi na tashin hankali. Ummi ta juya ta kalli Ameer da Hajiya ke kallo sannan ta juyo ta kalli Hajiya, sai wani sabon kuka ya kwankwaso mata kofa hawaye suka ce mata salamatu alaiki. Hajiya kam kallon Ameer kawai take babu dauke ido, surarta da zubin halittarsa suke tuna mata da ďanta Deen, yayinda wani bangare na zuciyarta ke raya mata abun da hankali da tunani ba zai dauka ba, balle har ta yarda. Ssi da Ummi ta yi da gaske sannan ta iya tsayar da kukanta, ta mikewa tsaye tana fadin.

“Hajiya Allah ya kara lafiya, zamu tafi daman na ce ya kawo ni ne na duba ki kawai”

“Ummi zauna”

Kamar saukar aradu haka ta ji maganar da Ameer yayi mata ta dira a kunnenta ta yi cikin kanta. Bata da kuzarin musa mass duk da kasancewar shi ne ďa ita kuma uwa, sai ta koma ta zauna gabanta ns bugawa da karfi, idonta kuma ta kafe shi gurin Ameer.

“Akwai abun da ya kamata ki warware ko ba haka ba? Zuciyata na hararon min wani abu, ni da Hajiyar da Humairah duk kin saka mana shakku. Warware maganar dake cikinki, fada min wani abun da ban sani ba, ba ni labarin yadda kika san tsohuwar nan”

Ummi na fargaba da tunanin kalmomin da zata hada ta fadi maganar ta sigar da Ameer da kuma Hajiya za su fahimceta. Ta tsinkayo Hajiya na karanta masa alakarsu.

“Ni uwar mijinta ce ta farko, mutumen da ta aura kamin ta auri mahaifinka, ni ce na haife shi, Bahijja da ka ji tana ambata ita ce kanwarsa, su biyu kawai Allah ya ba ni, sai kuma yanzu da na samu yan jikoki, wannan Humairah da ka sani yar Bahijja ce matar da ka ji tana tambaya, ita mahaifiyarka har ta haihu da Deen amman Allah be kawo abun da ta haifa da rai ba, shi ya tafi kuma shi ma abun da ta haifa ya tafi, ba dan ma mace ta haifa ba, Wallahi da na ce kai ďansa ne domin kamar ta yi yawa har ta bace, duk na kalleka sai na tuna da ďana...”

Ta kai karshe maganar, su kuma hawaye suka fara gudana a idon Ameer. Ummi na ganin haka ta mike tsaye da sauri tana kiran sunanshi.

“Ameer”

Sai ta sauke kansa kasa, duk yadda ya so gushewa ganin laifin Ummi ko daga mata kafa yayi mata uzuri a wannan babin sai abun ya gagara.

“Hajiya, ni ne ďan da kike zaton ya mutu, ba mace ba ce namiji ne, kuma ban mutu ba ina raye ni jikanki ne, ni ďan da aka haifawa ďanki ne”

Wani abu mai kama da mafarki kamar zahiri ne ya baibaiye Hajiya, ba dan hankalinta da yake tare da ita ba, da kuma kaifin tunani da Allah ya bata na gane komai ba tare da rikicewa ba, tabbas da babu abun da zai hana ba zata rikice a lokacin ba. Sai dai duk da haka sai ta ji kamar ba daidai ta ji abun da Ameer yake fada ba, dan haka ta sake fadar.

“Kasan abun da kake fadi ďan nan? Wacan jika da aka haifa min mace ce kuma bata zo da rai ba, kuma kuma an ba mu gawarta mu muka rufeta da kanmu, ko dai baka gane bayanin ba?”

“Ke ce dai abun zai miki wahalar fahimta a yanzu, wata gaskiya ce da zaki ganta kamar karya, wata kalar gaskiya ce mai wuyar karba, Ummi kin cutar da mu, ina jin kamar abun da kika fada be isa ya saka ki aikata abun da kika aikata ba, why Ummi why”

Wannan karon da kuka Ameer yake tambayarta, sannan ya karasa gurin Hajiya ya kai hannunsa ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login