Showing 63001 words to 66000 words out of 281271 words
ya bude ido zuciyarsa har gargada take numfashinsa na sarkewa. Waira sai kuche kushen ta subuce a hannun Ummi take ta sake rikeshi ganin take kamar maza sun fi mata yi mata kirki da kyautata. Tasss ya wanke mata fuska da mugun mari har sai da ta ji wata kara a kunnenta ganinta yayi batan wucin gadi, kwatankwacin tsayin da yayi a dazun da ta rumgume shi irinsa ta yi jini ya cika bakinta idonta ya cika da hawaye ya sauko mata...
AMEER POV.
10:24pm O'clock
Abincin ya masa dadi fiye da na kullum har cikin kwakwalwa kansa yake jin yadda abincin yake kai masa. Ba karyar Step Mother dinsa ta iya girki musamman na yau da ya zama na dabam.
“Da alama dai yau gaba daya zaka cinye jalof”
Ameer ya tsayar da cin abincin da yake yayi murmushi tare da daukar cup din ruwa ya sha.
“Sis don't fake it ke ma fa kin ji dadin abincin nan”
Sister ta yi murmushi tana cigaba da cin abincin. Wayar dake kam teburin ya dauka ya shiga Instagram dinsa ya the first thing da ya fara dubawa shi ne account din Nimra, sai kuma yayi sa'a ta amsa masa bukatarsa ta son following dinta.
“Good Girl, i like you”
Ya furta yana jin kamar wani target dinsa ya kama hanya.
“Is she the one?”
Ta tambaya duk kuwa da bata san abun da yake kallo a wayar ba, sai ya dago ya kalleta.
“Who?”
“Girlfriend”
Yayi wani miskilin murmushi
“Tun da kike a rayuwarki kin taba jin na yi maganar budurwa?”
“Noo amman na san kana da ita”
“No Fiyya ni bana boye komai ai, idan akwai ta definitely zaku sani, more especially you, kin san you're my favorite, so ni bana da budurwa?”
Ya maida hankalinsa gurin wayar yana tunanin irin sakon da zai tura mata.
“Amman miyasa? Ni Wallahi ban taba maka magana ba ne kawai amman na dauka kana da girlfriend”
“Idan har zan yi budurwa zan zabo mai tsada ce, kuma har yanzu ban taba cin karo da wanda ta yi daidai da ra'ayi na ba, idan har zan so mace dole sai mai matukar tsabta wanda bata taba sanin miye kazanta ba a rayuwarta, wacce ke wanka da tsabta kamar yadda nake, who can cook delicious food, mai yawan kamshi wacce idan an rabe ta babu abun da zan ji sai Kamshi, mai matukar kyau fara sosai yar gidan masu kudi, mai ji da kanta, kuma wacce idan na ce ta aske gashin kanta zata aske yi kamar dai Angel, sannan kuma Virgin”
“Wacece kuma Angel”
“Wata Ahlil Kitab ce, kin san su babu ruwansu da barin gashi, kuma tana da tsabta irin yadda nake so a jikin mace”
“Tab za a samu duk mai abun da ka lisaffa amman ban da yawan tsabtarka da kuma aske gashin kai, sai idan ka samu wacce bata ta gashin daman”
“Za a samu wata rana, duk da na san dukan abun da na lissafa abu ne mai wahala a yanzu ba musamman ma virgin din, domin yan mata yanzu tun a waje suke siyar da mutuncinsu da kudi ko da sunan soyayya, ke kanki bana iya shaidarki a yanzu”
Ta zaro ido tana kallonsa da mugun mamaki har tana nuna kanta.
“Ni.... Na yarda na bada mutuncin ne ai sai Momy ta ci Ubana”
“Lokacin da za ku yi ai babu wanda zai sani, ita kanta Momyn ba zaki bari ta gane ba, ku yaran zamani ne kun fi iyayenku wayo”
Ya fada kamar ba da shi ba, ya mike tsaye yaja kujerar baya.
“Good Night”
Ya fice daga gurin yana taba wayar, fiyya ta bishi da kallon mamaki har fice daga falon gaba daya.
“Kasan yan matan da ka lalata kenan shiyasa kake fadar haka”
Ta fada bayan ya fice.
Motarsa ya nufa ya sai jingina yana jin nan ne safe place da zai samu damar aikata abun da yake son yi.
“After all abun da kika Hada kai da dan'uwanki kika min be wadatar ba sai kin sake cutar da ni da cewar na dauko wata yarinya a motar? Why Nimra? Me na tare muku ne? Miyasa ba ku son ganin farincikina?. Ban tsammanci kalar wannan rayuwar daga gareki ba, a farkon ganin da na yi miki na aminta da ke shiyasa zuviyata ta natsu da ke, ashe akwai abun da kike shirya min, kin kyauta Nimra kuma na gode”
Ya tura mata bayan ya gama rubutawa, so yake ya kalailaye zuciyarta ya siye da kalaman dauraya ya yaudare ya karye mata guiwa kamar yadda ta yi masa.
“By the way, akwai sarewata a cikin motar, ki aiko min da ita a inda muka saba haduwa dake”
Ya sake aikawa, daman sarewar na daga dalilin da ya saka ya nemi handling dinta a IG. after ya gama tura mata ya dago jikin motar ya dawo cikin gidan, yana tunanin yadda sakon zai riske ta, yana misalta irin amsar da zata ba shi Idan har yayi nasarar karya mata zuciyar.
Yana shiga dakinsa amsar sakon da ya tura ya fara dawo masa tun yana karantawa a tsaye har ya kai ga zaunawa.
“Dukan abun da kake zargin na aikata saboda na cutar da kai ban aikata ba Ameer Allah shi ne shaidata, Maleek ma ba shi da wani buri ko kudiri na cutar da kai, sai dai kuskuren fahimta da kuka samu, kuma ni ban san ka bar motar a can ba balle har na saka a aikata maka abun da kake zargina da shi, mi zai saka na saka wata a motar dan kawai na cutar da kai, miye ribata idan na yi haka? Ka fada min garin da ka tafi? Balle na aika wani yayi maka haka? Ka aminta da ni Ameer, ina cikin damuwar abubuwan da suka faru, mahaifina baya magana da ni saboda abun da na aikata na baka mota da kudi da wayata da na yi, har aka samu wata yarinya a motar ka”
Yana yi yana tsayawa har ya gama karantawa, yanayin yadda ta turo masa sakon zube a lokaci daya ya tabbatar masa da cewar ya fara yin nasarar karya lagonta, duk kuwa ba be san abun da take shirya masa a boye ba. Har yanzu be ji ya yarda da ita cewar ba da hadin bakin yayanta ta bashi motar ba.
“Sarewar kuma ban duba motar ba, balle na san abun da yake ciki saboda yau aka kawo motar tare da yarinyar a gidanmu, amman bayan komai ya lafa zan duba motar na dauko maka sarewar idan tana ciki, kuma ba zamu hadu a inda muka saba haduwa ba sai dai a gurin da muka taba zuwa da kai wajen Abuja, shi ma kuma idan har na samu sarewar domin ban san iya abun da zai faru idan mahaifina ko Maleek ya gan ni tare da kai ba”
“Really”
Ya fada bayan ya gama karanta sakon na biyu, sannan ya jefar da wayar saman gado ya cire rigarsa yana tunanin wata kila kuma ita ce take shirya masa wani zagon kasa kamin ya gama saka tasa gadar saren.....
DR SHURAIM POV.
“Wato ana yi ma mutun kallon mai hankali sai ka tarar babu hankali a tare da shi, ko kuma tunani zan ce?”
Hajiya Hajara ta fada tana masa kallon bacin rai.
“Yanzu ina yarinyar take?”
Cewar Mahaifinsa. Shuraim ya kalli mahaifiyarsa domin damuwarta ce ta fi daga masa hankali ya san mahaifinsa mai fahimta ne zai iya fahimtarsa amman Hajiya kam sai yayi da gaske.
“Ita yarinyar tana hannun Police na kai musu ita, ni kuma ina lafiya”
“Ina kwana? Kuma na kira wayarka baka daga ba daga baya kuma ka kashe wayar”
“Hajiya yarinyar bata yarda ta bar ni ba, a dole a can muka kwana ni da ita CID din, sai da safen nan da suka kama hanya sannan ta hakura, kuma kin san mace ce be kamata na barta ta kwana a can ba saboda mace ce, kuma na san idan idan na fada miki ba zaki bari na kwana a can ba ko dan yanayin jinin dake zuba a idonta ya kamata ace na tsaya a gurin gudun kar sai na dawo wani abun ya faru su ce ni na cutar da ita, shiyasa ban amsa kiranki”
“Aifa duk yadda zaka yi ka kare kanka ka sani, ku kullum ana nuna muku yadda za ku tsira sai son jefa kai a halaka kuke”
Fada ta yi masa sosai a washen garin ranar da ya koma gida, sa'arsa daya mahaifinsa ya masa uzuri har ma ya tare masa fada a gurin mahaifiyata. Sai da ta gama masa fadan tsab sannan ya fita daga falon ya shiga domin bangarensa yana wajen falon ne, ya shiga dakinsa cikin rashin jindadin rayuwa da Waira, har lokacin ya kasa natsuwa da inda za aje da ita, tunawa da yadda ta tsaya tana kallonsa ba ta yi kuka ba ya kara tausayinta a cikin ransa.
“Allah sarki Allah yasa tsare ki Waira Waira”
Ya maimaita sunan a karo na farko bayan idonta, ya kalli inda ta cije shi a hannu har ya fasa yana murmushi zuciyarsa sam bata masa dadi, ya san abu ne mai wahala kamin ya manta da lamarinta ba nan kusa ba.
“I hope zaki samu gurin da zaki aminta da kowa, Allah ya hana masu niyar cutar da ke su cutar da ke”
Kamar marar lafiya haka ya wuni a ranar saboda rabuwa da Waira, wata kila da sun dade a tare da ba zai ma iya sabuwa da ita ba saboda shakuwa. Musamman da ya je asibitin suna da zancenta wasu kuma na tambayar abun da ya faru bayan barin asibiti.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: *W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
22
Ummi ta yi saurin shiga tsakiyar su tana kallon Maleek dake huci abun da ba halinsa ba.
“Bata san komai akanka ba, ba ta yi hakan da ganganci ba, bakuwa ce miyasa baka yi wannan tunanin ba?”
Ya dauke kai ba tare da yace komai ba ya shige dakinsa, gaba daya manta yayi abun da ya kawo shi dakin har sai da ya zauna na tsawon lokaci sannan ya mike tsaye, sai ya ji kansa na mugun sarawa irin jikinsa jikinsa yayi weak sosai a take zazzabi ya karyo masa, daker yayi alwala a dole dakin yayi sallah Magariba yana gamawa ko addu'a be tsaya yi ba ya hau gado ya kwanta ya lulluba saboda sanyin da yake ji. Ummi ta kama hannun Waira ta koma da ita cikin dakin tana fada da Nimra wacce ta biyota a guje.
“Ummi na shigo na samu bata kan gadon, i just want to check on her ashe ta boya bayan curtains sai da na daga na ganta ina mata magana na rika ta sai ta fisge ta fito a guje”
“Gashi ai kin tsoratata, kuma kin ja mata ta sha mari ji yadda bakinta yake jini”
Bandaki Ummi ta shiga da ita ta kunna tap ta tara cup ta tara ruwa ta kai mata a baki, kamar wata tsumma haka Waira ta zama hawaye kawai ke zubo mata, duk inda aka yi da ita sai ta bi, ta kuskure baki kamar yadda Ummi ta nuna mata sai ta zubar da ruwan tare da jini, haka tai ta yi har sai da jinin ya fita sannan Ummi ta tafi dakinta ta dauko brush ta saka man goge baki ta mika mata.
“Zaki iya wanke bakin ko kadan ne? Saboda akwai ciwo a bakin”
“Ummi zafi zata ji fa, saboda brush ne kara dai a kyaleta sai gobe ko jibi sai ta wanke”
“Okay”
Ta hada mata ruwan wanka da kanta sannan ta juyo zata fito sai Waira ta biyo bayanta har lokacin hawaye take, yanzu kam ba kuka rashin marin da Maleek ya mata take ba, kukan barin garinsu da rayuwarta take, yanzu kam ta gane ta yi kuskure mai girma, ta baro mutanen da ta sani kuma take iya rayuwa a cikinsu ta dawo a inda bata san kowa ba, kuma kowa be santa yarensu da addininsu ba daya ba, abincinsu ma ba daya ba.
“Wanka zaki yi”
Ummi ta nuna mata ruwa, sai ta juya ta kalli ruwan ta juyo ta kalli Ummi ta fashe da kuka, a nan hankali Ummi yayi matukar tashin tausayinta ya kara kamata domin ta san bata jin yarenta kamar yadda police din suka fada tun kan a kawo ta, gashi ta samu mari daga Maleek ga kuma rashin sabo da su da bata yi ba, domin farkowa kenan ta ganta a dakin akan gado sai sanyin ac, hakan ya saka ta tashi ta boya a bayan lalulen dakin har sai da Nimra ta shigo ta ganta, a kokarinta na gujewa Nimra ne ta fito dakin a guje saboda barin kofar dakin a bude da Nimra ta yi.
“Wani abu na miki ciwo ne?”
Ummi ta taba hannunta sannan ta taba shafin fuskarta a inda Maleek ya mareta gurin har ya kumburo yayi mata ja kasancewar fara irin farin nan da ko sauro ya cijeta sai jikinta ya bayyana.
“Yi hakuri, hakan ba zata sake faruwa ba na miki alkawari”
Ita dai kallon Ummi kawai take ba dan tana jin yarenta ba, ita ma Ummin tana kokarin fahimtar da ita abun da take fada ta hanyar amfani da hannu, sannan ta saka duka hannayen ta goge mata hawayen.
“Ki yi wanka sai a kawo miki abinci”
Da kallo ta bi Ummi har ta fice daga bathroom din tare da Nimra suka ja mata kofar, ba su bata son wanka ba ita kuma bata san yadda zata fada musu cewar bata son wankan ba, tsoro take kar wani ya sake dukanta bata son ta sake yi ma kowa musu a yanzu. Dukawa ta yi a gurin ta rumgume kanta tana hawaye, gaba daya rayuwar da suke da Eid sai ta dawo mata sabuwa, yadda take hawan itace ya tsallaka tsauni, Eid yayi mata busa ta yi rawa sai ta ji tana marmari hakan.
A hankali ta daga kanta tana kallon bathroom din ya ci uban wanda ta shiga a gidansu Dr Shuraim, sulalewa ta yi kasa ta zauna ta kai hannunta mai lafiya ta taba gefen fuskarta, tun da take a rayuwarta ba a taba marin fuskarta haka ba, bata san wani abu zafin dukan ba sai a yanzu da ta farka ta sami kanta a gidansu Maleek, tana sauke hannunta ta tuna da takardar da Dr Shuraim ya bata da kuma tufafinta sai ta kalli hannun ta ga babu komai, a take ta fashe da kuka marar sauti tsoron take kar su ji kukanta ku ce za su daketa, a iya fahimtarta ba kowa yake da tausayi a wannan duniyar data samu kanta ba, saboda farko maciji ya cijeta tana ta neman dauki Ameer be taimake ta ba har ta suma, ta farko ta ganta a wani gurin da bata sani ba, wato asibiti suma sun tsikata mata karfen allura a jiki kamar yadda suka saka mata wani karfen na drip a hannu, kuma suka daure mata hannun da macijin ya tsareta, Dr Shuraim ne kawai ta san ya tausaya mata, kanwarsa da mahaifiyarsa ma sun yi mata wanka da karfin tsiya suka gyara mata gashin kanta yana zafi babu ko tausayi, sannan suka yi ma Dr Fada har sai da ya kai ta gurin mutanen nan masu bakin tufafin, a can aka sake soka mata karfe a jiki ta yi bachi bata farka ba sai yanzu a wani gidan na dabam, gashi kuma ta fara cin karo da mari da ya saka jini fita a bakinta, yanzu kuma sun saka ta a nan sun rufe gani take kamar cilasta mata suke sai ta yi wanka, abun da bata kauna kuma bata saba ba, ko ma zata ta yi wanka ba a irin wannan gurin take yi ba.
Kusan awa daya ta bata a bandakin tana zaune a inda Ummi ta barta, banbanci dazun da yanzu dazun a tsaye ta barta yanzu kuma tana zaune ta saka kanta cikin kafafuwa tana hawaye.
“Baki yi wanka ba”
Ta dago da sauri ta kalli Ummi ta girgiza mata kai, ta mike tsaye da sauri tana taba zuben sarkar da Dr ya saka mata a wuya.
“Fito ki ci abincin idan ba zaki yi wankan ba”
Ummi ta yi mata alama da ta zo, sai kuma ta tafi din suka fice daga bathroom din, Ummi ta nuna mata gado alamar ta zauna, sai ta girgiza kai ta zauna kasa ta matse guri daya ta maida idonta kasa, fita dakin Ummi ta yi bata dade ba ta dawo dauke da plate din fruit da ta yanka sai cup din zallar madara marar hadi, madarar ta fara ajewa sannan ta zauna ta aje plate din a tsakaninta da Waira wato tsakiyarsu, ta kai hannunta ta dago kan Waira ta sakar mata murmushi sannan ta dauki watermelon ta fara kai mata a baki da fork, Waira ta bude bakin ta karba tana taunawa a hankali, saboda halin Ummi na karamci da son kyautatawa ko madarar bata bari Waira ta sha da kanta ba, ita ta bata da hannunta, bayan sun gama ta kwashe kayan ta fita da su ta sake dawowa da ruwa a cup ta rika kanta ta bata ruwan ta sha. Sannan ta daga ta mike tsaye ta zaunar da ita saman gado ta nuna mata abun lullubi ta kuma nuna mata bandaki.
“Idan zaki yi fitsari ga guri can, idan kuma zaki rufa ga abun lullubi nan”
Waira ta sauko daga kan gadon ta zauna kasa, ta fi jin natsuwar kwantawa a kasan domin Bedsheets din da blanket ba irin wanda ta saba da shi ba ne, ga gadon da yayi mata kato sosai kamar na gidan sarautar garinsu.
“Ba ki yi wanka ba balle na baki tufafi ki canja”
Ita dai kallon Ummi kawai take, kamin ta kalli gurin da hannun Ummi ya nufa ta dauki takardar data gani saman gadon tare da tufafin fata, sai Waira ta yi saurin mika mata hannu alamar ta bata, Ummi bata zafafa sai ta bude ta ga abun da yake cikin takardar ba, sai ta mika mata, waira ta saka hannu ta dauki kayanta ta rike. Ummi ta mata Murmushi ta juya ta