Showing 120001 words to 123000 words out of 281271 words
sonta ba ko dan tana kanwata, sai dai yayi amfani da ita ya cin ma wata manufa”
Abiey yaja dogon tsaki ya bude motar ya fita ya nufi sashensa. Maleek ya juya gafensa da zimmar bude gambun motar ya hango Waira dake tsaye nesa da motar rike da dan zomonta tana kallon motarsu, jiran take waye zai fito mazaunin direban ko Ummi ce, domin ita kadai take son gani. Samun kansa yayi da tsayawa kallonsa kasancewar bakin gilashi ne na waje baya iya ganin na ciki, sai dai na ciki ya ga na waje, idonta yayi sumtum kamar an dafa shi saboda kukan da ta ci na tafiyar Shuraim. Ganin kamar ba za a fito ya saka ta laraso gurin motar ta saka hannunta daya ta dafa zata leka ciki sai ya sauke gilashin motar, ta kalleshi ya kalleta ido cikin ido, ba tare da tace komai ba ta juya.
“Waira”
Ya kira sunanta da tattausan lafazi, ta juyo tana kallonsa sai ta fashe da kuka.
“Toh me na ce miki kuma na kuka?”
“Ka ce Waira”
Ta fada tana kuka hawaye na mata zuba kamar bata san zafinsu ba. Hannu ya mika ya ciro tissue a motar Abiey ya mika mata bata tare da ya ce komai ba, sai ta saka hannu ta karba ta share hawayen, sannan ta juya ta koma gurin da ake mata lessons dinta. Sai a sannan ya bude mota ya sauko ya shiga cikin gidan. A kujerarta ta zauna tana share hawayenta har lokacin. Dattijon dake mata darasin ya ce.
“Kin tafi ki gani ko Ummi ce?”
“Ta daga kai”
“Ummi tana can asibiti gurin Nimra”
“Me ya same ta?”
Ta tambaya cike da son sani, domin ita dai tun da Maleek yayi mata tsawa dazun saboda tafiyar su Shuraim sai ta boya a kitchen tana kuka duk abun da ya faru bata sani ba.
“Saboda rabata da aka yi da wanda take so”
“Amman miyasa Ummi ba zata bari ta aureshi ba”
“Baki san Ummi ta haife shi?”
“Na sani”
“Na gani ai”
“Ta ina?”
Sai ta yi shiru bata son ta fada masa yadda aka yi ta sani saboda kar ya mata fahimta dabam, domin ta lura nan ba kamar garinsu ba ne da suke girmama tsafi. Dariya yayi ya matso kusa da ita
“A addininsu idan mace da namiji suka sha Nono daya ba a aure, ko da kuwa uwar su daban daban”
“Amman miyasa addininsu yake da zafi? Kai ma ai addininsu kake yi”
Ta tambaya domin ita dai bata ga illar haka ba, saboda sun sha nono daya ace ba za ayi musu aure ba bayan ba uwa daya ta haife su ba. Ya daga mata kai yana murmushi.
“Addininmu daya mana, amman ina fatar ba zaki jefar da na ki addinin ba ki dauki na mu, kuma ki daina kuka har idonki ya kumbura haka”
Kallonsa take kamar mai tunani ko mai son gano wani abu. Ganin hakan ya saka shiikewa tsaye ya isa gurin blackboard din suke rubuta ya cigaba da yi mata darasi.
AMEER POV.
Sai da suka yi nisa sosai sannan ya rage gudun da yake ya kalli Humaira dake gafen motar tana kukan da babu hawaye.
“Sai ki fada min gudun me nake wai?”
“Toh ba kamani za su yi ba, yarinyar nan na ganta a fito da ita da alama ma mutuwa ta yi, ai na san ina tsayawa za su kamani kashina ya bushe, Ameer ka ci amanar yarinyar nan kuma nima ka ci amanata, yanzu sun rike fuskata ko a wani gurin suka gan ni za su gane ni”
“Amman ke kin raina wayon mutane saboda wannan kika saka na taka mota ina da gudu kamar mun yi sata? Fitar min a mota Malama”
“Wallahi ba zan fita ba sai ka kai ni gidanmu, kuma ba zan yafe maka halin da ka jefa ni ba, kai dai haduwa da kai masifa ne babu alheri sam”
“Kuma rabuwa da ni bala'i ba, ina wayar?”
“Tana can na saki mana har da takardar na bar su a can, ni ba ta raina nake ba, Kuma Wallahi yarinyar nan tana cikin mawuyacin hali kila ma ta mutu, ni ba ruwana da alakarku amman yanzu ka dauke ni ka saka ni cikin masifa, gashi iyayena talakawa babu ruwansu ka ja min matsala”
“Me aka ce ya samu yarinyar?”
“Ni ina zan sani wai, kaddara ce kawai ta hada ni da kai, gashi ka zame min kaya, Allah kadai ya san iya abun da ka yi ma wannan yarinyar ita ba, bakin mugu”
Ya taka turki yayo slow down ya faka ya fita ya zafaya ya bude gambun motarta.
“Fita, ba zaki zauna min a mota kuma ki zage ni ba”
“Ba zan fita nan ba Wallahi ban san abun da zai sake samuna ba, Ameer ka sakawa kanka imani ta tausayi haba, sai ka rika treating mutane kamar su basa da zuciya da jini kamar kai”
Wannan karon hawaye ne ya zubo mata.
“Ina kallo kana rubutawa mata cewar fake love kake mata fa, haka ake yi kwanan baya a gabana ka saka iyayenta kuka kuma ka saka tana zuwa nan kana taba ta ashe ma kai ba da gaske kake sonta ba, ina ta mata hannunka mai sanda ta gane amman bata gane ba”
“Gaskiya na fada mata ai, miye laifina a haka?”
“Bayan ka gama cutar da ita, ni Wallahi da ace mahaifiyarka ce sai na maka dan banzan duka, kuma sai na kai kararka gurin police na nuna min wukar da ka yi”
“Ko yanzu ai zaki iya marar kunyar yarinya”
“Marar kunyar yara dai”
Ta rama tare da kai hannu ta jango gambun motar ta rufe ta bar shi nan tsaye. Shi har mamakin yadda ta iya rashin kunya kuma take iya tsayawa ta fada masa magana son ranta yake. Zagaya ya shiga side din direba yaja motar har suka isa inda yake kyautata zaton unguwarsu ce domin ya ganta a gurin sau biyu kuma ta jadada masa a lokacin da ta kai shi cikin gidansu. Ya faka be ce mata komai ba ita ma bata ce masa ba. Bude motar ta yi ta fita sai da ta yi nisa sannan ta juyo cikin daga murya ta ce.
“Allah ya isa, mugun kawai, bakin mugu”
Gudun kar ya biyota da mota ya saka ta cire talkamimta ta ranta a ana kare. Ta gishin gaban motar yake kallonta har ta shige kwanar sannan ya ja motar ya juya kanta yana fadin.
“Wannan ta fi tunanina, idonta a tsaye suke bata tsoron kowa”
Yaja motarsa ya fice daga unguwar, sai dai har ya isa gida tunanin halin da Nimra take ciki yake, babu abun da yayi masa dadi kamar rashin tarar da mahaifinsa a gidan da yayi saboda ya san zai masa maganar wukar da aka ce ya dauka dazun. Tunani kala kala ne a ransa na yadda zai yi ya san halin da Nimra take ciki, sai yayi kamar ya kira number data kira shi da ita sai ya ji ba zai iya ba domin ba san wayar a hannun waye take ba. Cam dabara ta fado masa ya kira abokinsa Abdull, Abdull na dauka ya gabatar masa da bukatar ta son sanin inda Nimra take.
“Ni ban ma san abun da ke faruwa ba ai”
“Na dauka ko Maleek din ne yake dubata ai”
“I don't think so kasan Maleek baya duba mata ai, ko da kuwa yan gidansu ne”
“Dan Allah bincika min lafiyarta da inda aka kwantar da ita yanzu please”
“Hope dai ba wani abun zaka yi ba”
“Wai Abdull kun mai da dan ta'addane ko minene?”
Abdull yayi dariya ya kashe wayar. Ameer ya jefar da wayar saman gadonsa ya cire rigarsa ya wandon ba tare da tunanin ko gudun kar wani ya shigo dakin nasa ba ya nufi bandakin haihuwar uwarshi ya shiga ya sakarwa kansa shower ya rufe ido ya bude hannayensa ruwan na tsasa shi. Sai da ya ji ya gamsu da hakan sannan yayi wanka ya fito ya dauki tawul a dress room ya daura. In less then 20min ya shirya cikin korean trouser da farar T-shirt ya saka snipers masu kyau da tsada sannan ya nufi wayarsa ya dauka ya duba sakon da Abdull ya turo masa na asibitin da aka kwantar da Nimra.
“Good My Guy”
Ya nufi inda keys dinsa suke ya dauki na wata motar dabam ya fito dakin. Da sassafa ya saukk Stairs Mummy ta kalleshi ta ce.
“Daddy ya dade yana jiranka, wani uzurin ne ya taso masa shiyasa ya tafi, da ka jira ya dawo kamin ka fita”
Kallonta kawai yayi ya dauke kai ya fice kamar ba da shi take magana. Yana isa gurin motar da key ta ke hannunsa ya bude ya shiga, masu tsaron gidan suka bude masa gate ya fita ya fara shimfida gudu a titi kamar shi ma na ubansa ne.
A lokacin da ya isa asbitin sai ya samu guri ya faka yana ta kalle kalle, can kuma ya fito yana tunanin ta ina zai fara, domin sunan asibitin kawai Abdull ya turo masa amman be fada masa inda take ba, sai dai tunaninshi na ba shi ba zata wuce Emergency ba, sai dai idan ya shiga ya gane dakin yayi me? Bayan ya fada mata gaskiya kuma abun kunya Maleek ya ganshi ya zo gurin ma, wata zuciyar ta katsi hanzarinsa. Sai kawai ya fasa yin abun da zai yi a asibitin ya juya da zimmar tafiya sai ya ji an kira shi da wata bakuwar murya.
“Ameer”
Ya juyo sai yayi arba da Ummi dake rike da coolar Mahmood na gefenta rike da key mota, da alama su ma kusa da inda ya aje motarsa suka aje ta su ko kuma sun hangoshi. Hannayensa ya saka aljihu yana kallonta sai wani sham kamshi yake.
“Me ka zo yi nan?”
Ya kalli Mahmood sannan ya amsawa Ummi.
“Na zo ganin likita na ne, ya jikin yarki ance bata jin dadi”
“Magana kake hankali kwance kamar baka aikata komai ba, kalli idona tun da muka kawo Nimra asibitin nake kuka har yanzu, bata iya numfashi sai da Oxygen, bugun zuciyarta ya kasa daidaituwa, ta kasa bachi kuma Likitoci suna tsoron su yi mata allurar bachi saboda kar ta ki farkawa, kasan abun da ya fi min ciwo? Da ta fada min cewar ka fada mata soyayyar da kake mata ta karya ce, idan yau Nimra ta mutu wannan furucin naka ne ya kasheta, Ameer yar'uwarka kake son ka kashe..... Nimra kamar yar'uwa take a gareka saboda Nono na ta sha bayan kai ka saki, na gaji da ajiyar kayan da ba zai kai ni ko'ina ba, lokaci yayi da ya kamata kowa ya san gaskiya”
“Excuse me kamar baki cikin hayyacinki”
Ya fada yana daga kafadunsa, a take Mahmood ya ware hannu zai kai masa mari sai Ameer yayi karaf ya rike.
“Kai yaro Maleek ma yayi kadan balle kai kanensa, bakin rijiya ba gurin wasan makaho ba ne”
Ya jefar da hannunsa ya juya sai Ummi ta saka hannu ta juyo da shi da karfi.
“Weather you believe me or not, mutumen da kake attacking dan'uwanka ne, saboda ďana ne ni na haife shi kamar yadda na tsuguna na haife ka, uwar da ake fada maka ta mutu ni ce, Alhaji Bashir ba mahaifinka ba ne, ka je ka tambayi Hajiya Jamila idan tana raye, Ameer kai ďana ne jininka yau idan aka tsaga sai anga nawa a ciki, ba dan nono ďaya da kuka sha da Nimra ba, babu abun da zai hana na cilasta maka aurenta saboda ina son rayuwarta da farincikinta....”
Cikin wani yanayin mai kama da fada Ummi take fadin haka hawaye na mata zuba.
Baya baya Ameer yayi yana jin wani jim akansa.
“And Now kuma you're not making any sense...”
Ya nufi motarsa ya bude da sauri ya shiga yaja ta ya bar gurin. Jinginawa ta yi jikin wata motar dake kusa da ita ta fashe da kuka tana jin kamar ba ta yi abun da ya dace ba, sai dai ba zata iya cigaba da aje abun a zuciyarta ba, domin ba san iya abun da zai biyon duk wadannan abubuwan da suka faru ba. Mahmood kam mutuwar tsaye yayi yana kallon mahaifiyarsa ya kasa cewa komai, shi ma dai ganin yake kamar ta zauce ba a hayyacinta ta fadi duk abun da ya fito bakinta ba.
___________
Masu karatu na ce ana wata ga wata me kuke tunanin zai faru a gaba?
Anya Ameer zai yarda?
Abiey zai karbi Ameer matsayin step son dinsa kuwa bayan duk abun da ya faru?
Ya kuke tunanin rayuwar Nimra zata kasance?
Ni fa ban yarda da Malamin nan na Waira ta ba ku fa kun yarda da shi?
Anya Maleek be fara fadawa ba?
Abiey zai yarda Namra ta auri Shuraim kuwa?
Wai ina labarin Eid?
#Team Maleek
#Team Ameer
Ni dai ina Team Shuraim da Humairah, kun san na fi son masu zafi zafin lol.
[6/21, 10:22 PM] My S Line: *Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
40
Tukin motar yake zuciyarsa na raya masa cewar, mahaifiyar Nimra ta fita daga hayyacinta ne, wata kila kuma ta yi haka ne saboda ta haddasa masa fitina saboda abun da yayi ma ďanta da yarsa. Ya girgiza kai yana tabe baki domin sam maganarta bata kama kanshi ba, kuma ba zata kama ba. Da tunanin ya isa gida sai ya bude motarsa zai fita sannan wani furucinta ya fado masa a rai na cewar ya tambaye Hajiya Jamila idan tana raye, how comes ta san Hajiya Jamila? Bayan ba a Abuja take ba a Kano, kuma shi be taba yin maganarta da Nimra ba balle yace ita ta fada mata, then taya ta san Hajiya Jamila, to him Hajiya Jamila is just he's father's ex wacce take matukar nuna masa kauna da soyayya.
Fitowa yayi motar ya fara dialing number Ammynsa wato Hajiya Jamila, tunanin me zan tambayeta ko ya fada mata and taya zai fara mata kwatancen mahaifiyar Nimra da ko sunanta be sani ba bayan Ummi da yaji Nimra na kiranta, tana daf da dauka ya yanke kiran ya nufi hanyar falonsu. Daman kofar a bude take dan haka ya saka kai ciki, i think this is the first time da be tsaya canja talkamin shiga falo ba ya haura sama da su har dakinsa, domin hankalinsa ba a nan yake ba, sai da ya shiga kuma sai ya fara tunanin me zai kawo shi dakin? Me zai yi a dakin? Ya juyo ya fito yana jin ransa kamar ya dan bace, but why ransa zai bace? A take ya tuna daga hannu da Mahmood yayi zai mareshi, wai kamar shi Mahmood zai daga ma hannu da sunan mari, and then mahaifiyarsa ta fara fada masa magana anyhow.
“Revenge take son dauka, ita ma dai bata da banbanci da yayanta”
A falon ya zauna, sam sam maganar Ummi bata sake shiga kansa ba, shi kawai mamakin yadda take shiga lamarin yayanta yake, ta wani bangaren kuma baya ganin laifinta saboda ita macece akwai rauni a tare da ita, kuma shi ne mai laifi da ya sake bibiyar rayuwar yarsu. Be wuce awa daya da yawowa gidan ba Daddy ya shigo gidan kamin ya isa part dinsa ya kira Ameer a waya domin hankalinsa ya tashe da zancen wukar da aka ce masa ya dauka.
“Na ce ka same ni gida ko?”
“Ina gidan fa Daddy, tun dazun nake jiranka”
“Alright”
Daddy ya fada sai ya fasa shiga bangarensa ya jufo apartment dinsu yana sanye da jallabiyarsa yar Egypt mai tsada, sai shining take kamar an shafa mata mai, hannunsa rike da counter.
Ameer na ganin shigowarsa ya mike tsaye domin baya son yayi masa magana a gaban Mummu wato Step mother dinsa shi a kullum kallon makiyiyyarsa yake mata.
“Daddy yanzu zan tafi part din ka ba”
“Toh gani ni na zo ai, zauna”
Daddy ya nuna masa kujerar da ya tashi sannan shi ma ya zauna, Ameer be zauna ba kamar yadda mahaifinsa ya bukata sai ya cigaba da tsayuwar yana juyawa ya kalli stairs.
“Daddy can't we talk private”
Daddy ya karewa falon da babu kowa a ciki kallo sannan ya kalleshi.
“Akwai wani a nan ne?”
“Wani dai zai iya shigowa”
“Wani abu ka aikata”
Ya zauna yana fadin.
“Come on Daddy na girma a wannan babin kuma”
“Toh ka yi da wukar? Da bakinka kake fada min cewar wata ka tsorata fa, wata wa? Sannan an fada min akwai yarinyar da kake treating badly why? Kai yaushe zaka canja ne Ameer?”
“Daddy ka taimake ni dan girman Allah ka fada min waya fada maka wannan maganar?”
“Ba zan fada ba, shi ma kaje ka karta masa rashin mutuncin ko? Zauna ka fada min me ka aikata, kuma karka kuskura yi min karya”
Ya zauna ba dan ransa ya so ba.
“Yadda labarin yake, ita yarinyar nan tun da ta gan ni ta bi ta tsane ni, yadda kasa ni na hana ta arziki, shiyasa idan na dan shigo sai na yi mata barazana, and daddy bata Tsorona sam kai tsaye idan na yi mata abu take ramawa kuma bata shakkar fada min magana any how i hate her, kuma kar kace wata babba ce karamar yarinya ce fa yanzu ma take jami'a”
Daddy ya samu kansa da murmushi domin ya lura da yanayin da yadda yake bashi labari ba irin na kullum ba ne, har wani yamutsa fuska yake yana son gwada yadda take masa tsiwa ba tare da ya san yana yi ba.
“Toh me ka yi mata da wukar?”
Ya juyo ya kalli Daddy.
“Sako nake so ta kai min wani guri shiyasa na yi mata barazana na san idan ban mata haka ba, ba zata ji magana ba, dan bata Tsorona kuma bata jin maganata”
“Do we need to fired her?”
“No no no no no no”
Ya furta hakan kusan sau biyar, daman da biyu Daddy ya tambaye shi ba dan ya sallame ta ba ko da ya bukata.
“A barta ta zauna, ai son nake na azabtar da ita har sai ta yarda na fita zafin kai”
“Baka ba ni labarin inda ta kai maka sakon ba kuma sakon me ne?”
“Haba Daddy karka min haka mana, na fa girma sai ka rika daukata karamin yaro”
“Ba yaro nake daukarka ba, ina maka kallon abokina ne da zai fada min sirrinsa