Showing 162001 words to 165000 words out of 281271 words

Chapter 55 - Wani Gari Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1234

yana kallon harabar gurin.

“Wata yarinya ce mai kyau fuska da kyakkyawar zuciya, ta iya kyautata lafazi, gata da jan hankali, abar tausayi ce kuma abar so, abar kulawa full-option ta hada komai, and someone has never been in her heart”

“I'm sorry Ameer. It since like ka yi saurin warkewa daga abun da ka yi ma Nimra. With due respect Ameer baka canja ba”

Ya matso kusa da ita.

“I canja Humairah kuma zan canja, shiyasa nake son na kyautatawa mata i won't break her heart, ba zan bari wani ya cutar da ita ba, she's the kind of girl I'm looking for, not just her zan kyautatawa kowa gwargwadon ikona, domin na fahimci ni ma alfarma nake ci”

Ta sauke ajiyar zuciya tana jin wani abu marar dadi ya tsaya mata a makoshi.

“Who's knows who my family is? Wace kalar rayuwa suke? Su waye su? Mutanen kirki ne ko na banza wace kalar rayuwa mahaifina yayi ban zani ba, kamar yadda Waira ma bata san waye mahaifinta ba, banbancinta da ni, ni ina da Daddy da Ummi a yanzu, ita kuma bata da kowa”

“if you want to change you should start from within.... Ina fata kuma ina kyautata zaton mahaifinka mutumen kirki ne wish you all the best”

Ta karasa tana murmushin karfin hali.

“Thank you”

Ya amsa sannan ya saka key din ya bude motar ya shiga. Tana tsaye a gurin har ya bar asibitin. A hanya ya tsaya yayi sallah sannan ya kama hanyar gida. Yana isa ya cire jakar Waira ya saka a wata motar ya mikawa mai kula da motocin gidan key motar da ya dawo da ita.

“Ka wanke ta da kyau akwai jini a ciki, na kade wata mata ne muka kaita asibiti”

Jiki na rawa mutumen ya saka hannu biyu ya karba, yana mamakin yadda Ameer yake masa bayanin abun da ya faru, abun da be saba ba, ko da mutum zai bude ya gani a motar ba zai fada masa ga abun da ya aikata ba, shi a gidan babu mai jindadinsa dukansu suna zaune ne kawai saboda Mr Bashir yana kyautata musu kuma yana musu albashi mai tsoka. Ya shiga cikin falon cikin wani yanayi mai wuyar fassara, Mummy dake tsaye rike da remote ta kalleshi.

“Ameer ka dawo”

Ya kalleta, a lokacin da yake ďan iskan gari bata isa ta yi magana ya amsa mata ba sai ya ga dama, har ganin yake kamar sa'ido take masa tana masa munafurci a gurin Daddy, amman yanzu wannan duk ta kau.

“Eh”

Ya wuce sai kuma ya juya.

“Na kade wata mata by mistake amman na kaita asibiti, please ina son ki saka masu aikin gidan nan su zuba mata abinci, zan yi ma musa text din inda take da kudin da za a bata sai yaje ya kai musu”

“Subhanallahi amman dai baka ji ciwo ba ko?”

Ya amsa mata da kai.

“Matar da sauki?”

“Da sauki ina tunanin karaya ce”

“Allah ya sauwake, ya tsare gaba please Ameer ya kamata ka rika kula idan kana tuki, kuma ka rika sassautawa zuciyarka”

Sai da yayi kamar ya tsaya yi mata bayanin ba da gangan ya kade ya ba, it's not his fault sai kuma ya juya kawai ya nufi stairs.
[7/17, 6:21 PM] My S Line: 53

Around 9:11pm Waira tana zaune kan carpet tare da pen dinta, liffatinta na lessons na gabanta ta dora jakar a kan kujera. Baby rabbit dinta ta dora kan littafin tana zanawa kamar an sakata.
Namra na zaune kam 3 seater tana lasar wayarta. Maleek kuma na zaune a dayan side din falon rike da mug hannunsa daya kuma rike da wayarsa, sai ko kadan hankalinsa ba shi a gurin wayar ya tafi gurin abokiyar fadansa Waira dake zane, ba ya iya hangen zanen da take, but he found himself looking at her, ko wane motsi da nata yana kan idonsa. If ba dan kar na yi karya ba da sai na ce har yadda yake fita da shigar numfashinta yana kallon yake yana kan idonsa. If wani zai tambaye me yasa yake kallonta ba zai iya fada ba, maybe ko dan ita ce mace ta farko data fara bude masa ido har yake son kallonta ko zama kusa da yan'uwanta, zai kuma fi yarda idan aka ce saboda kyaunta ne domin tana da kyau daidai yadda ko ita ta tsara kanta iyakar abun da zata yi kenan. Everything about her is unique her hair, dress, her talk the shagwaba part and even her talk yana jin fadi muryarta when she's talking about something. Yana ganin Ummi ta fito daga kitchen sai yayi saurin dauke idonsa daga barin kallonta ya maida dubansa kan wayarsa. Ummi ta dire mata copy tea

“Wai haka aka ce ku yi a makaranta? Kina wahalar da wannan zomon ace sai an dora shi kan takardar sannan a zana waya ce ku zana zomo”

Waira ta kalleta with her cute laugh ta ce.

“Babu wanda ya ce na yi Ummi, kawai ina son na zana ne”

“Kin sa miyasa mai lessons dinki be zo ba yau?”

“Aa be ce komai ba da zai tafi”

“Ko maybe ba shi da lafiya ne?”

Waira ta bude baki zata yi magana kenan aka murda kofar falon, Ummi ta juyo ta kalli kofar Maleek kuma ya dago kansa ya kalli kofar, Waira ta maida dubanta a inda suke kallo. Ameer ne ya shigo cikin shiga ta kananan kaya sai kamshi yake kamar sabon ango, hannunsa rike da school bag din Waira. Mamakin zuwansa ya hana Ummi amsa sallamar da yayi, Maleek kam daman shi ba zai amsa masa ba, balle kuma Namra da sai a lokacin ta dago ta kalleshi. Waira ta washe hakora kamar bakauye ya zo birni, Hanne ce kawai ta amsa masa sallama domin bata wayance shi da kyau ba. Maleek ma mamakin zuwansa yake duk kuwa da yana kallon dalilinsa na zuwa wato jakar Waira dake rike a hannunsa, sai dai abun da ya fi daure masa kai shi ne yadda Ameer yake kokarin kula Waira yarinyar da ko a mafarki aka ce masa Ameer zai yi haka ba zai yarda ba.

“Ba a maraba da zuwana ne?”

Ya fada ganin yadda kowa yayi tsaye yana kallonsa kamar sun samu tv. Sai a lokacin Ummi ta dawo hayyacinta tunaninta ya dawo jikinta.

“Of course you're welcome, kai da gidan mahaifiyarka Ameer”

Ta fada idonta na cika da hawaye even though ta san ba zuwansa ne ya kawo ta amman a haka murna take ďanta ya shigo gidanta, sallamar da yayi kawai ta isa ta saka ta fahimtar da lalama ya shigo gidan nan.

“Please dan Allah ka zauna”

Kujerar da ta nuna masa dabam kujerar da ya zauna dabam, ta nuna masa dayar kujerar dake kusa da inda Waira ta dora jakarta, shi kuma sai ya zauna a kujerar da ke kusa da Waira. Da sauri Waira ta saki abun da take ta tashi tsaye ta zauna kusa da shi kamar zata shige jikinsa.

“Jakata ka kawo?”

Ya daga mata kai try to smile, kallonta kawai yake kana gani kasan ta gama dauke masa hankali, domin ko kadan be lura da sauran mutanen da suke falon ba, balle har ya san da zamansu.



After two weeks later...

Yana tafe Fiyya na bayansa rike da basket din da Mummy ta zuba masa kulolin abincin da za a kawo asibitin. Shi ya fara tura kofar ya shiga ya rike mata kofar ta shiga sannan ya rufe. Fiyya ce ta fara karasawa gurin gadon ta aje musu abincin tana yi ma Tsohuwar ya jiki tare da isar musu da gaisuwar Mummy, domin ita bayan kwana biyu take zuwa ta duba su, kanensa kuma time time idan zai so ko direba zai kawo abinci, Ameer kan kullum idan zai je aiki ko ya dawo sai ya shigo asibitin duba tsohuwar, domin jin yake kamar nauyinta a yanzu yana kansa.

“Ya jikin?”

Ya tambaya yana kallon Tsohuwar dake rike da ayaba tana ci.

“Jiki Alhamdulillah ďan nan, Allah yayi albarka kana ta fama da dawainiya”

Humaira ta mike tsaye ta bashi kujera, sai dai ta san ba zai zauna ba, domin ba gwada zama a dakin ba duk zuwan da yake.

“Kullum zai kin kin ba ni kujera, kuma kin san ba zama nake ba”

Ta yi murmushi.

“Ina jin ba dadi ne ace ina zaune kana tsaye”

“Kuma kullum sai na tararda ke a nan ke kike jinyarta bayan ga mahaifiyarki, ba kasafai nake tararda ita, Allah yass dai kina zuwa aiki”

“Duk lokacin da zaka zo kana sa'a da ina nan ne shiyasa, aiki kuma na daina zuwa ai tun a wacan lokacin”

Ya daga mata kai.

“You got lucky na canja if da yanzu na koreki”

Dariya Fiyya ta yi kamar yadda Humaira ma ta yi dariyar.

“Baka bukatar ka koreni ai, ni na kore kaina?”

“Why?”

Ta daga kafadunta.

“Kawai dai”

Be sace cewa komai ba, ya kalli agogon hannunsa.

“Kuna bukatar wani abu?”

“Aa bama bukatar komai a yanzu”

Shigowar da Dr yayi ne ya katse hanzarinsa daga yi musu sallama ya fice. Likitan dake cikin shiga ta kayan likitoci ya iso gurin ya mikawa Ameer hannu suka gaisa.

“An fada maka sakona”

Ameer ya kalli Humaira wadda ta dago tana kallon Likitan.

“Yanzu nake kokarin yi masa bayani”

Likitan yayi murmushi.

“Kin manta kenan?”

“Aa na tuna yanzu da na ganka”

Ta fuskanci Ameer dake jiran abun da zata fada masa.

“Yace gobe za a kwance daurin da aka yi mata, a duba, idan yayi haka ake so, idan kuma be yi ba sai an sake wani”

Tana fadar idonta na cika da kwalla.

“Sarkin kuka daga magana sai hawaye, haka jiya kika min fa”

Likitan ya fada yana kallonta.

“Bana son tashin hankali, ba mu da yawa a dangi kusa, bana son na sake rasa kowa”

“Ba saki rasata ba, aiki ne kawai kuma ni ba cinye ta zan yi ba, I'm not zombie”

Ta yi murmushi tana share hawayen idonta.

“Ni ban ce ba”

“Da dai yafi”

Duk abun da ake Ameer be ce uffan ba, sai kallon tsohuwar dake cin ayarba hankali kwace yake kamar ba ita ake fadar za a sakewa aiki ba.

“Ita hankalinta a kwance ma yake naki ne a tashe”

Likitan ya fada yana kallon Humairah

“Toh abun da Allah ya kawo ba sai hakuri ba, gwagwarmaya wace kala ce ba mu gani ba?”

Ameer yayi murmushi yana kallonta, karfin halinta da imani ya burge shi.

“Allah ya kara lafiya”

Ya fada sannan yayi ma Fiyya alama da su tafi da ido, Fiyya ta yi musu sallama suka fice. Likitan ya juya ya kalli Ameer har sai da ya fice sannan ya maida dubansa gurin Humairah.

“Am ya sunanki ma?”

“Humairah..”

“Haka ashe na rike sunan”

Ta yi murmushi tare da sauke kai kasa, sai ya dauki file din da ya shigo dashi bayan ya gama duba Tsohuwar ya fice. Zaunawa Humairah ta yi tana fadin.

“Yau Mama bata zo da wuri ba, gashi ina son na shiga makaranta kar na yi latti”

“Ki zuba min abinci da aka kawo sai ki tafi, ai zata zo wata kila ta tsaya wanke tsumman da tafi da su jiya ne”

“Maybe”

Ta dauki plate din ta bude coolar jalof din shimkafa ce da aka yi mata ado da doya ta sha kayan kamshi da vegetables ga kuma mai har yayi yawa. Rabin plate ta zuba mata ta dora mata a saman gadon ta matsa mata da ruwa kusa.

“Ba zaki ci abincin ba?”

“Sai na dawo zan ci”

“Toh Allah ya kiyaye hanya, yau ba su bada kudin da suka saba fadawa ba”

“Yau da gobe ai sai Allah Hajiya, wata kila sun fara gajiya ne ko kuma sun manta”

“Ba dai gajiya ba, sai dai ko mantuwa amman dan dan abun da suke ba mu ai be taka kara ya karya ba a dukiyarsu. Ni ba dan ba a son kaddara ba ai da na ce kara da aka yi haka, dubi ki ga kullum sai an kawo abinci, ga kudin nan, kuma sun dauke duk wata hidima ta asibitin nan, gaskiya suna da kirki, ko da can ke ce da masifar ki kike ganin kamar ba shi da kirki, kullum fa sai ya zo, mamansa ma kullum tana hanya”

“Hmmm Hajiya, ke dai kin ganshi kawai amman da can ba haka yake ba, yanzu ne ya canja”

“Ke ma ai na san halinki fitina ta miki yawa”

Ta yi dariya ta nufi gefen gadon Hajiya ta dauki jakarta ta goya, sannan ta yi mata sallama ta fice, tana tafiya harabar asibitin ta ji an kira sunanta.

“Humairah”

Ta dan juyo kadan sai ta yi arba da Likitan dazun, murmushi.

“Doctor”

“Na'am fita zaki yi?”

“Eh makaranta zan je”

“Wace makaranta? Ina kike karatu”

Ya jera da ita suna tafiya.

“Sky King University”

“Ah makarantar manyan mutane kenan, wane course?”

“Microbiology”

“Wow, ke babba ce”

“Kune manya ai”

“Kika ce ba, muje na sauke ki”

“No akwai inda zan biya kamin na wuce”

“Karki damu duk zan iya sama direbanki, kin ga wata rana zan yi alfahari na ce na taba daukar Humairah yar Microbiology a motata, zan ce ta yi min alfama ta shiga motata”

Murmushi ta sake yi ta girgiza kai.

“Bana son zolaya, Likita za'ayi ma alfama?”

“Eh mana ke baki san babba ce ba?”

Bata son jan zancen da tsawo dan haka ta yi shiru bata sake cewa komai ba har suka isa gurin motae yar yayi mai matukar kyau, kana ganinta kasan sabuwar mota ce, sai da ya saka key sannan ta bude front seat ya shiga ta zauna.



AMEER POV.

A Area 2 ya sauke Fiyya gidan wata kawarta da zata yi birthday, sannan yayi driving kansa zuwa gida, tun a harabar gidan yake kallon bakuwar motar da ke fake a compound din. Domin ba ta yi kama da motocin gidansu ba, yanayin yadda akai parking din ma ya fahimtar da ba direbobin gidansu ba ne. Yana wasa da key hannunsa ya shiga falon, sai ya samu Mummy da Ummi zaune, Daddynsa yana kan dayar kujerar fuskarsa dauke da murmushi. Ummi na ganinsa ta mike tsaye kamar karamin ma'aikaci ya ga boss dinsa.

“Ameer ka dawo”

Daddy ya fada, sai ya nufi inda Daddy yake ya zauna yana yi ma Ummi kallon tsanaki, ta yi rama sosai farinta ya wuce na ainahin fatarta wani fari ne mai sheƙar da fata, fatan idonta ta yi fari kana kallonta ka san lafiya bata isheta ba.

“Baka gaishe da Mamanka ba, tun fitarku take nan tana jiranka”

Mummy ta fada tana murmushi, still be ce komai ba, sai kallonta kawai yake. Hakan ya saka Ummi jin wani iri sai ta ji kamar ta tsargu, domin ganin take komai ta yi ma Ameer a yanzu ba zata burge shi ba.

“Na zo ne kawai na ganka, Daddyka ya fada min abin da ya faru, ina addu'a Allah ya tsare gaba, kuma idan ka ba ni dama ina son ni ma naje na dubata for the sake of you”

Ta karasa maganar muryarta na rawa kamar mai tsoron abun da zai fito daga bakinsa. Ya dauke kai sannan ya mike tsaye.

“Lemme drop her home”

Fadar sai sauke ta a gida, abun mamaki ne a gurin Mummy da kuma Mahaifinsa Daddy ya san da be son ganinta ba zai sauketa gida ba, ba ma zai zauna a falon ba, sai dai Daddy be san manufarsa ta yin haka ba, hakan ya saka shi mikewa tsaye tare da kai hannu ya dafa kafadarsa.

“Karka fada mata magana marar dadi please”

Cikin wata siga mai kamar rada ya fada masa haka, Ameer ya girgiza kai.

“Ba abun da kake tunani ba ne”

Yana bashi amsa ya wuce yayi gaba, Ummi ta dauki jakarta zuciyarta na raya mata maybe Ameer zai yi amfani da wannan damar ne ya fada mata karta sake zuwa gidan duba shi. Mummy ta rakota har gurin motar ta tuko kanta, hakan ya saka Ameer barin jikin motarsa ya iso gurinta ya mika mata hannunsa.

“Key”

Ta ciro key a jakarta ta mika masa, ya nufi motar ya bude mata backseat, ta ji kamar ya karramata yayi mata alfarma a cikin daruruwan mutane.

“Hajiya na gode sai anjima”

“Toh Allah ya kiyaye hanya, ni ma zan shigo wani lokacin In Shaa Allah”

“Allah ya nufa”

Ummi ta fada sannan ta nufi motar ta shiga, Ameer ya rufe motar ya zagaya ya shiga mazaunin direba yayi ma motar key. Yana tukin Ummi na hawaye ko da ace ba a cikin dadin rai Ameer zai tukata ya kaita gida ba, ita abun farinciki ne a gurinta.

“Karki sake zuwa duba ni, idan kina son ganina ki min waya zan zo”

Ya fada yana tukin a hankali.

“Ba lallai idan na ce ina son ganinka ka zo ba”

“Saboda me?”

“Saboda ban kyautata maka ba, a lokacin da kake bukatata, na san kana kallona da wannan abun a kullum”

Yayi shiru na tsawon lokaci kamin ya sake fadar.

“Me yasa to kika yi?”

Hannu ta saka ta share hawayen idonta.

“A lokacin ina tsoron rasa rayuwar mahaifinka ne, saboda likitoci sun tabbatar min, idan ba a yi masa aikin ba, zai iya mutuwa, mun siyar da gidan gadonmu da kayan dakin Yayata Maryam mun hada duk be wadatarwa na bi yan'uwana da abokan mahaifina, kowa be taimaka min ba, ina cikin wannan halin ne Dr Hamid ya kawo min mafitar cewar akwai wacce take son siyen ciki, idona a rufe na aminta aka siyar, sai bayan da aka yi aikin mahaifinka sai kuma rayuwa ta yi bankwana, babu yadda ban yi ba saboda na gudu da cikinka amman ban samu dama ba, saboda ina da talaka ba ni da ikon komai, a cikin yarjejeniyar da aka yi da Hajiya Jamila ance idan har na karya alkawari zan biya kudi mai yawa, kuma ba ni da su...”

Ta yi shiru saboda hawaye dake mata zuba suna son su ci karfinta su zame mata kuka.

“Su waye yan'uwa mahaifina? Ban san su ba”

“Idan kana son sani, zan fada maka su, zan tafi da kai har Kano ka gansu”

“Sun san abun da kika aikata?”

“aa ba su sani ba, duniya tana kallon ďan da na haifa da Deen a matsayin mataccen”

Hawaye sun saukowa Ameer, sai ya kara rage gudun motar ya faka gefen titi ya jinginar da kansa jikin kujera.

“I'm sorry, na san baka kaunata na san a gareka ban cika uwa ba, na san ba zan taba kima a idonka ba, amman please don't leave me, i want you here with me, na san ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login