Showing 189001 words to 192000 words out of 281271 words

Chapter 64 - Wani Gari Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1241

ma Humairah ta yi sallama ya sanar da Ummi abun da yake ransa, domin ba zai iya jira sai gobe ko jibi ba, kawai ba zai iya jinkiri da jira ba, ba kuma ba zai iya hakuri da abun da Maleek yake masa na shiga hanci da kududdufi ba, ta ya zai kula Waira abun da ba muruminsa ba. Daga Ummi har Humairah sun kula da yanayinsa ba ma kamar Ummi da idan ransaya bace ko ta ga damuwa a fuskarsa take jin kamar an cire mata duk wani jindadi na duniya.

Ummi ta saka Hanne ta kawo ma Humairah abinci sannan ta dauki wayarta ta kira Namra ta sauko suka gaisa, kana ta shiga dakinta ta yi mata goma na arzki daga kan perfume body spray da atamfa mai kyau, Namra kuma ta bata Veils har biyu saboda Ummi ta yi mata maganar ta bata wani abu a kokarin Ummi na ganin kowa ya kawar da abun da ke zuciyarsa. Ummi ta fito har balcony ta rakota tare da Namra da Ummi ta yi mata dole. Humairah ta bude mota ta shiga kamin ta rufe Ameer ya kalleta ya ce.

“Bari na kira Waira ku ga juna, ita ce kadai ba ku gaisa ba”

Namra ta taba baki kamar zata ja tsaki sai kuma ta juya ta shige ciki saboda gudun bata ran Ummi.

“Ummi muje ciki akwai maganar da nake son na yi da ke kamin na tafi, Maybe ba zan kwana a gidan nan ba yau saboda Daddy yace yana son na yi dinner a can shi ma yana da maganar da zai yi da ni”

Ummi ta amsa masa.

“Okay”

Sannan ta kalli Humairah ta ce.

“Allah ya kiyaye Humairah na gode sosai ki gaida gida”

“Gida zai ji Ummi, ni ce da godiya Allah ya saka miki da alheri ya yaye miki damuwarki”

Ameer da Ummi suka hada baki gurin amsawa da Ameen. Sannan Ummi ta juyo suka shigo cikin falon, ganin Hanne na zaune a falon ya saka Ummi ta zarce dakinta kai tsaye yana biye da ita har suka hau sama. Idonsa sai ya koma gurin dakin Waira zuciyarsa ta raya masa yanzu tana can tana kuka ko kuma tana jin haushinsa. After sun shiga dakin Ummi ta zauna shi ma ya zauna sai shiru ya biyi baya, ita tana sauraren abun da zai fito daga bakinsa shi kuma ya samu kansa da jin nauyin furta mata kurinsa kai tsaye, wannan ne karon farko da yake jin haka, bayan kuma ya shigo da zimmar furta mata komai kai tsaye. Wata kila saboda tana ita ne ko kuma saboda Waira ce da ta banbanta da sauran mata a gurinsa, ya'allah kuma saboda wannan ne karon farko da zai gabatar da wata mace a matsayin wacce yake so da aure, amman zai iya ikirarin kunya ko jin nauyi akan komai ba halinsa ba ne.

A dan zaman da yayi a gida da kuma experience irin na uwa mai ƴaƴa maza da mata ya saka Ummi fahimtar yana jin nauyi ko shakkar furta mata abun da yayi niya ne, lura da ta yi da yadda ya rike hannunsa yana matsawa kuma ya kasa daga kai ya kalleta. Hakan ya sakata tasowa daga inda take zaune ta dawo saman kujerar da yake ta zauna ta fuskance shi.

“Ameer maganar tana da nauyi ne ko hatsari? Ko kuma tana da kunya ne? Wani abu zaka bukata? Ko kuma wani abu zaka gabatar? Kar tunanin yadda zan karbi abun ya saka ka yin nauyi ko jin kunya gabatar da bukatarka, fada duk abun da kake so a duniyar nan matukar be tsabawa Allah ba, na maka alkawari zan maka shi, wannan duty na na uwa, wata kila da nan ma zaka yarda ina kaunarka sosai, ko wani ka kashe ko wani abu ka aikata karka ji nauyi ko tsoro fuskance ka fada min saboda ni Mahaifiyya ce, uwa kuma mai tausayin ƴaƴa ce kuma mai kaunarsu, balle kuma ni da nake da kai a matsayin ďa, dole zan sama maka mafita a duk inda take”

Kalamanta sun karfafa masa guiwa kuma sun masa dadi, ta haka ne ya dago ya dubeta duba na tsanaki yana murmushi.

“Ummi”

Sai kuma yayi shiru ya sake maida kansa kasa.

“Ummi... Daman...”

Ya kasa dago kai, ganin hakan ya saka ita ta kai hannu ta riko fuskarta ta dago ya kalleta

“Fada min me kake so Ameer duk abun da kake so zan maka shi a duniyar nan karka ji nauyin komai”

Ya rausayar da kai.

“Ummi akan Waira ne”

Ummi ta gyara zamanta irin na ina saurarenka.

“Ummi Daddy ya dade yana min maganar aure, ke kanki a yanzu na san abun da kike bukata ganin kenan, and my life has changed now ina son na zama cikaken namiji kuma na faka ku farinciki, maybe ma maganar da Daddy zai min yau ba zata wuce ta aure ba ina tunani wata kila kuma zai min magana ne akanki ko Hajiya, to cut the story short, ban taba duba maganar da Daddy yake min ba, saboda ban taba faduwa da yarinyar da nake ganin ta dace da ni ba, but when i lay my eyes on Waira, she has everything da nake so a mace, i can't breathe when she is not near, Ummi ina son Waira so na gaskiya so na tsakani da Allah son da ban taba yi ma wata mace ba... And i want to marry her....”

Kana duban murmushin dake fuskarta kasan daga cikin zuciyarta yake fitowa, baki yayi kadan ya bayyana yadda zuciyarta ta cika da farincikin farucin Ameer da kuma kudirinsa, yau ita Ameer ya kalla ya fada mata yana son yayi aure, kuma yarinyar data rika yake son ya aura, me ya fi wannan dadi a gurinta, hawayen farinciki dake fita a fuskarta ne suka bayyana masa farincikin ruhinta, kasa cewa komai ta yi, sai ta mika hannu ta riko ta dan kwanto ta rumgumeshi.

“You have no idea how happy i am, ka kaddara a ranka kamar ka auri Waira ne Ameer domin na tabbatar ita ma tana sonka, kuma na jidadi da na zama first person da ka fadawa wannan maganar Allah ya maka albarka farinciki da ma saka ni a yanzu nan Allah ya ninka maka haka a rayuwarka”

Da dan mamaki ya dago daga jikinta ya kalleta.

“Na dauka ba zaki yi farinciki ba?”

“Why? Ai na fi kowa son farincikinka Ameer, kuma karka manta Waira a hannuna take yanzu, ko da ace baka sonta na gabatar maka da ita ka amince ka aureta abun farinciki ne a gurina balle kuma kai da kanka ka furta cewar kana sonta....Wow Alhamdulillah Allah all my thoughts zaka gabatar min da Humairah ne”

“Humairah ia just my friend kuma cousin a yanzu”

Ummi ta shafa fuskarta tana jin wani irin farinciki marar misaltuwa. Ya mike tsaye yana dariya

“Bari na je kar na bar Humairah tana ta jira”

“Okay”

Ta fada cike da alfahari ta bishi da kallo har ya fice. Ba kasa ya sauka directly ba, sai da ya sake leka dakin Waira sai ya same ta kwance a kasa, babu jacket din a jikinta amman bata far'a idonta ma yana nuna ta yi kuka ne. Suna hada ido ya sakar mata murmushi sai ta juyar da fuska ita ala dole tana fushi ne, kara fadada murmushi yayi ya ja mata kofar ya sauko kasa yana jin ransa fes domin ya san a yanzu ya shata line tsakaninta da kowa kuma ta zama tashi shi kadai.
[7/24, 5:20 PM] My S Line: 62

MALEEK POV. 

Da sassarfa ya sauko kana ganinsa kasan sauri yake yi, domin kilif din rigarsa ma yanzu yake kokarin sakawa, sanye yake da sky blue shadda kansa babu hula sai dai royal shoes ne a kafarsa dark blue da suka karawa shaddar kyau.

“Yadda ka sha wankan nan kyauta ace zance zaka je, ina matukar son na ga aurenku”

Cewar Ummi tana tauna yayan itatuwa dake gabanta zube a plate. Maleek yayi murmushi not knowing what to say domin shi dai be san ranar da tunanin aure zai zo masa har yayi yunkurin yi, kawai dai yana fatar wata rana shi ma ya zama kamar ko wane namiji ko dan cika burin mahaifiyarsa.

“Ameer dai ya kama haya”

Maleek ya dan tabe baki.

“Good for him”

Ummi ta yi murmushi tana kallon agogon da Maleek ya ciro aljihunsa ta ce.

“And abun farincikin, kasan wa yake son ya aura Waira”

He don't know how when da agogon da yake kokarin daurawa ya subuce daga hannunsa ya fadi kasa, glass din dake jikin fuskar agogon ya fashe ya kalli Ummi da sauro jikinsa na shocking fuskarsa na nuna tsananin mamaki da kiyayya da abun da yake na farinciki ne a gurin Ummi.

“What Wai... Ra... How....? That can't be possible, yanzu kin fahimci abun da nake fada miki ko? Yana da wani manufa akan yarinyar nan, rayuwarta yake son lalatawa kamar yadda yayi ma Nimra, daman opportunity kawai yake nema”

Ummi ta aje grapes din hannunta ta mike tsaye.

“No ba yadda kake tunani ba ne, wannan karon da gaske yake, na ga hakan a cikin idonsa, kuma aurenta yace zai yi, ita ma kuma na san tana sonsa, domin shakuwarsu da yadda suke kula junansu ya isa ya fahimtar da duk wani mai ido haka”

He don't want to argue with her because he don't has that energy now, jikinsa rawa yake kamar yadda zuciyarsa ma take ra rawa gaba daya tunaninsa ya rikice kuma ba zai iya fadar dalili ba, kawai dai shi dai ya san baya son Ameer ya kusanci Waira balle kuma aure ya hada su. Kamar wadda aka daurewa baki haka yayi shiru ya nufi kofar fita falon, Ummi dake ta kafa masa hujjoji ta bishi da kallo ganin kamar hankalinsa baya gurinta, kamin ya shiga motarsa har gumi mai zafi ya jika shaddar jikinsa ya shiga ya zauna ba tare da ya tashi motar ba, duk wani hanzari da yake na fita daga gidan zuwa gurin da yake ta uzuri sai ya kau hausawa suka ce sawun giwa ya take na rakumi. Ya kusan minti talatin a cikin motar zaune kamar ruwa sannan ya rufe motar ya saka key din ya tashi motar. Tukin kawai yake ya manta inda zai je, titin ya bi ya kai karshensa ya dawo ya sake kaiwa karshen ya sake dawowa haka yayi ta wuce gidansu yana zagayo kamar wanda aka yi ma sihiri. Can kuma ya faka motarsa kusa da gidansu ya ciro wayarsa ya kira Abiey domin shi kadai ne mutumen da yake jin zai iya fadawa wannan maganar au tattauna kuma ya fahimce shi. Ringing biyu kamin ta yi na uku Abiey ya daga.

“Son”

“Abiey akwai matsala”

“Kamar ta me?”

“Wai Ameer yau ya fadawa Ummi yana son ya auri Waira imagine?”

“What? Bayan duk abun da yayi? Ita kanta yarinyar ya manta yadda ya barta a wulakance yanzu an dauke an gyarata ta yi kyau shi ne zai ce zai aureta”

Maleek ya tashi zaune da kyau yana jin yadda Daddy ya tabo masa inda yake masa kaikaiyi.

“Yauwa Abiey dadina da kai kana da sauri fahimta, ni abun ya bani mamaki kuma ya ba ji tsoro jikina shaking kawai yake gaba daya tunanina ya jagule bana son na ga abun da zai cutar da yarinyar nan ko kadan, amman Ummi bata ganewa sai fadar take wai ba yadda nake tunani ba ne, gaba daya na rikice Wallahi na ma rasa kalar tunanin da zan yi, amman gaskiya ba zan jure ganin Ameer tare da Waira ba innocent soul like her”

Daga dayan bangaren Abiey yayi murmushi domin yana iya fahimtar abun da ke zuciyar dansa ba tare da shi dan ya sani ba, Abiey ya dade da karantar abun da ke zuciyar Maleek ba dan shi Maleek din ya fahimci zuciyarsa ba.

“Idan kuma mahaifiyarka da gaske take fa? Ameer ba zai cutar da Waira ba? Kuma idan muka yi bincika muka tabbatar da haka zaka yarda mu aura masa ita?”

Kamar an kashe mutu haka Maleek yayi shiru a wayar ko numfashinsa ba aji Abiey kuma yana testing dinsa ne domin gane ko daidai a ma'aunin da ya dora ďansa Maleek. Rasa yayi me zai ce idan yace ko a haka be be dace da aurenta miye hujjarsa? Saboda ya wulakanta ta could be enough? Idan kuma babu hujja zai iya yiyu ace ya tsani Ameer din ne.

“Abiey yarinyar nan bata dace da aure a yanzu ba, ni da zaka dauki shawara kuma ka amince ka saka Ummi ta amince zan fitar da ita waje ta yi karatu mai kyau kamin ta dawo ta yi hankali ta san kanta then by that time tana da yancin zabar abokin rayuwa, amman a yanzu ko ba Ameer ba ni bana son ganin kowa a tare da ita, ita fa bata san wa take so ba, kalli yadda ta rika waken tana son Shuraim a baya sai ka dauka saurayinta ne, idan wani ya samu irin haka ai sai iya amfani da weakness dinta ya cutar da ita, bayan duk abubuwan da ta yi going through”

“Maleek”

Abiey ya kira sunansa a natse.

“Na'am”

“Umminka ta san ka kira ni?”

“Okay don't tell her, karka ma nuna mata mun yi waya, maganar Ameer da Waira kuma ka barta a hannuna Waira tana karkashin iko na ne a yanzu, that's mean nine jagoranta a yanzu, and na manta ma ban fada maka ba, tun kwana baya na saka a bincika min garinsu ko za a samu danginta”

“Okay”

Maleek ya fada sannan ya sauke wayar yana dan jin sassauci a ransa, dazun kan jin yake kamar ya cire zuciyar daga kirjinsa ya jefar tsabar bakinciki da rudani.




AMEER POV.

After yayi dropping Humairah ya nufi gurin friends dinsa he spends time with them sai bayan Sallah Isha'i ya nufi gidan Daddy. A al'adar da ya daukarwa kansa a yanzu yana shiga gidan fuska a not like can baya da yake musu yadda yake so. Teema ce kadai a falon

MALEEK POV. 

Da sassarfa ya sauko kana ganinsa kasan sauri yake yi, domin kilif din rigarsa ma yanzu yake kokarin sakawa, sanye yake da sky blue shadda kansa babu hula sai dai royal shoes ne a kafarsa dark blue da suka karawa shaddar kyau.

“Yadda ka sha wankan nan kyauta ace zance zaka je, ina matukar son na ga aurenku”

Cewar Ummi tana tauna yayan itatuwa dake gabanta zube a plate. Maleek yayi murmushi not knowing what to say domin shi dai be san ranar da tunanin aure zai zo masa har yayi yunkurin yi, kawai dai yana fatar wata rana shi ma ya zama kamar ko wane namiji ko dan cika burin mahaifiyarsa.

“Ameer dai ya kama haya”

Maleek ya dan tabe baki.

“Good for him”

Ummi ta yi murmushi tana kallon agogon da Maleek ya ciro aljihunsa ta ce.

“And abun farincikin, kasan wa yake son ya aura Waira”

He don't know how when da agogon da yake kokarin daurawa ya subuce daga hannunsa ya fadi kasa, glass din dake jikin fuskar agogon ya fashe ya kalli Ummi da sauro jikinsa na shocking fuskarsa na nuna tsananin mamaki da kiyayya da abun da yake na farinciki ne a gurin Ummi.

“What Wai... Ra... How....? That can't be possible, yanzu kin fahimci abun da nake fada miki ko? Yana da wani manufa akan yarinyar nan, rayuwarta yake son lalatawa kamar yadda yayi ma Nimra, daman opportunity kawai yake nema”

Ummi ta aje grapes din hannunta ta mike tsaye.

“No ba yadda kake tunani ba ne, wannan karon da gaske yake, na ga hakan a cikin idonsa, kuma aurenta yace zai yi, ita ma kuma na san tana sonsa, domin shakuwarsu da yadda suke kula junansu ya isa ya fahimtar da duk wani mai ido haka”

He don't want to argue with her because he don't has that energy now, jikinsa rawa yake kamar yadda zuciyarsa ma take ra rawa gaba daya tunaninsa ya rikice kuma ba zai iya fadar dalili ba, kawai dai shi dai ya san baya son Ameer ya kusanci Waira balle kuma aure ya hada su. Kamar wadda aka daurewa baki haka yayi shiru ya nufi kofar fita falon, Ummi dake ta kafa masa hujjoji ta bishi da kallo ganin kamar hankalinsa baya gurinta, kamin ya shiga motarsa har gumi mai zafi ya jika shaddar jikinsa ya shiga ya zauna ba tare da ya tashi motar ba, duk wani hanzari da yake na fita daga gidan zuwa gurin da yake ta uzuri sai ya kau hausawa suka ce sawun giwa ya take na rakumi. Ya kusan minti talatin a cikin motar zaune kamar ruwa sannan ya rufe motar ya saka key din ya tashi motar. Tukin kawai yake ya manta inda zai je, titin ya bi ya kai karshensa ya dawo ya sake kaiwa karshen ya sake dawowa haka yayi ta wuce gidansu yana zagayo kamar wanda aka yi ma sihiri. Can kuma ya faka motarsa kusa da gidansu ya ciro wayarsa ya kira Abiey domin shi kadai ne mutumen da yake jin zai iya fadawa wannan maganar au tattauna kuma ya fahimce shi. Ringing biyu kamin ta yi na uku Abiey ya daga.

“Son”

“Abiey akwai matsala”

“Kamar ta me?”

“Wai Ameer yau ya fadawa Ummi yana son ya auri Waira imagine?”

“What? Bayan duk abun da yayi? Ita kanta yarinyar ya manta yadda ya barta a wulakance yanzu an dauke an gyarata ta yi kyau shi ne zai ce zai aureta”

Maleek ya tashi zaune da kyau yana jin yadda Daddy ya tabo masa inda yake masa kaikaiyi.

“Yauwa Abiey dadina da kai kana da sauri fahimta, ni abun ya bani mamaki kuma ya ba ji tsoro jikina shaking kawai yake gaba daya tunanina ya jagule bana son na ga abun da zai cutar da yarinyar nan ko kadan, amman Ummi bata ganewa sai fadar take wai ba yadda nake tunani ba ne, gaba daya na rikice Wallahi na ma rasa kalar tunanin da zan yi, amman gaskiya ba zan jure ganin Ameer tare da Waira ba innocent soul like her”

Daga dayan bangaren Abiey yayi murmushi domin yana iya fahimtar abun da ke zuciyar dansa ba tare da shi dan ya sani ba, Abiey ya dade da karantar abun da ke zuciyar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login