Showing 144001 words to 147000 words out of 281271 words
ba, amman idan har ya bukata zata fada masa domin tana kallonka a matsayin wani wanda ya samu farinciki da kyautar ďa silarta amman ya kasa zama da ita, ya ki yarda ta bawa wannan yaron kulawa a karkashinsa, kai ma baka yi mata adalci ba, domin saboda kai ta aikata haka sai gashi kuma ka rabu da ita.... ”
Mommy na aje ayar zancen Daddy ya rufe da fada, domin ji yake a yanzu ba shi makiyiya a rayuwarsa kamar Zahra da Jamila, ba ma kamar Jamilar da ita ce silar komai.
“Toh zama zan yi da ita? Bayan ta yaudare ni? Ta jefa a matsala ta aikata kuskure da addinin musulunci ma be yarda da shi ba, sannan yanzu ki kalli idona ki ce wai na kyale ta? Haukace ne ni da zan zauna da ita? Ko kuma neman haihuwa hauka ne? An isa ayi ma Allah wayo ne? Yanzu da ya tashi ba ni yayan ba ya ba ni ba? Taya za zauna da macen da bata da tawallaki da imani a zuciyarta? Idan har zata iya aikata hakan me kike tunanin gaba? Da ace ban gane gaskiya ba haka zamu yi ta zama ina kallonta a matar kirki? Ashe ke ma dai baki da hankali, ina ganinki mai ilmin ashe na banza ne”
“Allah ya huci zuciyarka, ban ce ka zauna da ita ba, kawai ina fadar abun da na fahimta ne”
“Fahimtar banza fahimtar wofi, mai daki ai shi ya san inda yake masa yoyo, karki fada min maganar banza, ina neman abun da zai zame min mafita ni da ďana sai kuma ki fara fada min wata maganar banza akan Jamila Malama tashi ki fice daga daki”
“Ka yi hakuri dan Allah... ”
“Ki tashi ki fice na ce”
Ta mike tsaye cike da nadamar maganar da ta yi ta fice daga dakin ta bar shi sai huci yake, abun da ba halinsa ba domin mawuyacin abu ne ta ga bacin rai a fuskarsa idan ma ransa ya bace yakan yi kokarin boye abun ya barshi a ransa.
AMEER POV.
Ji yake kamar shi kadai ya rage a duniyar nan he's feeling so lonely. Wani irin tarin bakinciki da damuwa ne a cikin ransa, ya dade a cikin motar kwance idonsa a rufe sannan ya bude motar ya fito ya shiga ciki, sai da ya fara bude fridge ya dauki gorar ruwa ya sha sannan ya dawo falonsa ya zauna yana sauke ajiyar zuciya. Be yi bachi ba kuma be tashi daga falon ba har kusan 11pm, tunani yake wani abun yana zuwa masa baibaiwa wani a daidai, wani tunanin kuma idan ya fadada sai ya ji kamar ya fashe da kuka. Sha daya na dare da yan mintuna kiran Abdull ya shigo wayarsa, yana ganin sunan mai kiran gabansa ya fadi zuciyarsa ta raya masa cewar Maleek ya labarta abokansa abun da yake faruwa shiyasa Abdull ya kira shi by this time. Amsa kiran yayi ya saka wayar a speaker yana tunanin kalar amsar da zai bawa Abdull idan ya tambaye shi.
“Hello”
Ameer ya fada cikin rashin kuzari murya can kasa. Kai tsaye Abdull ya fada masa dalilin kiran.
“Ameer ka ji kanwar Maleek ta rasu”
Jin an fada masa abun da ya sha gaba komai wato mutuwa ya saka shi zabura ya gyara zama da sauri.
“W-w-w what? Wace wace wace please wace?”
“Nimra, ta rasu da daren nan asibiti”
Ameer ya aje wayar akan center table dake kusa da shi ya dora hannunsa saman kai ya gurfana a kasa kamar mai neman gafara.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un Allah ya Abdull how? Why?”
“Why? Mutuwa ai bata da magani, ba kai ka fada min an kaita asibiti ba? Maybe ciwon be barta ba”
Ya girgiza kai ya rufe bakinsa yana kuka.
“Na kasheta Abdull ni ne... Ni ne silar mutuwarta.. Na rabata da duniya... Oh my God yanzu ya zan yi da hakkinta?”
“Ameer lafiya kake kasan me kake fada?”
“I break her heart, na yi ne kawai saboda na bakantawa Maleek, and ba son gaskiya nake mata ba, kuma na fada mata and.... Shi ne silar sumanta har aka kaita asibiti now you're telling me ta mutu, Me yasa abubuwan nan za su zo min a yanzu Abdull I'm such bad person i didn't deserve anything good at all, ina zan roki yafiyarta? Yanzu ya zan yi da hakkinta”
Dauke wuta Abdull domin shi dai ya kira ne kawai ya sanar masa kamar yadda abokinsu Dawood ya sanar musu so that su taru su tafi gurin abokinsu domin jajanta masa kuma ayi komai da su, kamar yadda suna gudanar da al'amurransu a can da, duk kuwa da kasancewar babu wanda ya taba rasa rai a cikinsu sai a yanzu da Maleek ya rasa, sai dai duk abun da ya samu suna taruwa su jajanta ma juna, ba dan ma matsalar da Ameer ya samu da Maleek ba da a kullum tare suke rayuwa.
“Ameer... Kasan me kake fada kuwa? Amman Ameer ya sani? All this fadan da kuka yi har abun ya kai su gurin police iyaye suka shiga abun be tsaya iya nan sai da zuciyarka ta raya maka ka aikata ma yarinyar nan wani abu? Yanzu miye amfanin aikatawar da ka yi? Gashi ka zama silar mutuwarta, innocent live, da ma ace kana sonta da gaske sai abun ya zo da sauki amman kasan baka sonta ka aikata hakan saboda kawai ka cutar da ita? Kana da matsalar rayuwa Ameer, idan ka dauki gaba da mutum kai ala dole sai ka ga bayansa, burinka ka wulakanta kowa cikin har da mu da muke abokanka, kuma babu wanda zai fada maka ta ji wannan ba rayuwa ba ce mun sha nuna maka amman baka ji ba, yanzu kana tunanin hakkin yarinyar nan zai barka? Idan iyayenta suka yi kararka ma za a iya kwatar musu hakkin yarsu, bayan haka kuma ka karawa kanka kiyayyar kanka a gurin Maleek da iyayensa.. Sannan.... ”
Yanke wayar yayi fahimtar Abdull ba zai gaba zuba masa kalaman da suke kona masa rai ba.
“Nimra...”
Ya furta yana hawaye, wayarsa ta sake ringing wannan karon Dawoo ne ya kira shi, wata kila shi ma zai sanar masa an yi mutuwar ne, sai ya ki daga wayar sai hawaye kawai yake, wani rauni da nadama suka mamayeshi. Sai a yanzu yake ganin be kyauta ba, be aikata daidai ba, be dace yayi haka ba, me yasa ya cutar da Nimra? Son zuciya ne ya kai shi ga aikata hakan ko kuma rauninta? Wa gari ya waya yanzu? Gashi Ummi ta fada masa kanwarsa ce, that's mean Ummi ta haife ta kenan? If wani ya aikata wa kanwarsa haka ya zai ji balle kuma ace shi da kanss ya aikata? Ya mike tsaye ya fara safa da marwa a falon, dariyarta ce ta fara fado masa a rai yana tuna yadda take nishadi idan ta zo gidan, saboda tana tunanin son gaskiya ya nuna mata, yadda ta rike hannunsa tana rokon ya rike ta amana ya tsaya mata a duk lokacin da za su tsinci kansu a cikin mawuyacin hali, yadda take yawan fada masa tana kaunarsa ga kuma irin marin da Abiey yayi mata a lokacin da suka zo daukarta restaurant ya tsaya masa a rai, kiran da ta yi masa a waya na karshe har ya fada mata cewar shi baya kaunarta ya hana shi sukuni. Sai da ya kai tsakiyar falon ya fadi durkushe ya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya, sosai yake kukan da ace gidan ba babban gida ba ne da makota ma za su iya jiyo muryarsa.
“Nimra ki yafe min.... Ki yafe min Nimra.... Na shiga uku, i hurt this innocent girl, i hurt her hakkinki ba zai bar ni ba, me yasa na aikata? Akan me zan dauki dansa akanta? Meyasa na zama wawa? Why ido zai rufe na kasa ganin abun da zai biyo baya?”
Fada yake da kansa kamin ya daga hannunsa ya dauke fuskarsa mari, ya daga hannayensa ya buga kasa, be taba jin ya cutar da wani cutar da ta kai makura ba irin wannan, sam be dorawa Nimra mutuwa a yanzu ba, shi be ma zaton son da take masa ya kai har haka ba.
“I'm such a bad person”
Ya fada yana jin kamar akwai abun da zai iya yi ya dawo da rayuwar Nimra ya roki gafararta. Tunanin yadda take rayuwa da shi a gidan ya dawo masa komai nata gani yake kamar lokacin yake faruwa, dariyarta ta cika kunnensa. Da sauri ya dauki key din motarsa da wayarsa ya fice daga gidan, sai da yayi kamar ya tafi gida kuma ya ji ba gidan yake bukata ba, kai tsaye gidansu Nimra ya nufa sai ya faka nesa da gidan yana kallon gidan, yadda motoci suke shiga da fita ya tabbatar masa da yarinyar da ya cutar ta bar duniya. Sai da dare yayi sosai ya juyo ya dawo gidan, ban da Mommy babu wanda ya san dawowarsa domin ya dawo a wani yanayi kamar ba shi ba. Dakinsa ya kulle ya rasa abun da zai yi, yadda gidansu Nimra ba a runtsa ba shi ma be yi bachin ba har garin Allah ya waye, washe gari yayi wanka ya shirya tun da wuri ya saka mask da bakin tabarau ya fice daga gidan. Gidansu Nimra ya sake komawa ya tsaya nesa da gidan yana kallon motocin dake shiga da fita, yana a gurin har aka fito da gawarta aka wuce da ita zuwa makabarta domin a cikin gidan aka yi mata Sallah sai da motocin suka yi nisa sannan ya bi bayansu har makabarta ya shiga ya tsaya can wani gefe domin ya san be isa ya taka karasa gurin, gawar Nimra ce first gawar da ya taba rakiya zuwa kabari, shi tun da yake a rayuwarsa be taba zuwa makabarta ba, sai dai ya gani a hoto ko video. Be taba sanin dan'adam ba a bakin komai yake ba sai a yau. Bayan kowa ya tafi sannan ya shiga motarsa ya dawo gida, kamar wanda yayi sata aka kamashi haka ya shigo falon jiki ba kwari zuciya a raunace, ido a kumbure baki a bushe.
“Ameer ga abun karyawarka, kuma mahaifinka ya damu da fitar da ka yi da safe baku ga juna ba, gashi baka dawo gida ba jiya sai da dare ya raba sosai”
Dagowa kawai yayi ya kalleta sai ta ga idonsa na zubar da hawaye ya kasa ce mata komai ya juyar dakansa ya hau stairs ya shige dakinsa. Kwantawa yayi ruf da ciki a take zazzabi ya rufe ciwon kai mai tsanani, yana jin wayarsa na ruru alamar kira amman ya kasa dagawa ya duba mai kiran ma balle har ya amsa.
UMMI's POV.
Ranar da aka yi sadakar ukun Nimra zuciyarta ta kwadaitu da son ganin danta, fiye da yadda jikinta ke son ganin likita. Bata son daga hankali kowa dan haka ta bar duk wani abu da take ji a ciki ranta tun daga ciwon jiki har zuwa son ganin Ameer da kuma son sanin halin da yake ciki, domin Maleek ya gabatar mata da duka abokansa da suke tare da suka zo masa gaisuwa har ma da iyayensu van da Ameer, ban da iyayensa da ba su san ma abun da yake wakana ba. Ta san idan tace tana son ganin Ameer ko sanin halin da yake ciki, yayanta da mijinta za su fahimta ba, ita kadai ta san yadda take ji kuma ta san halin da take ciki. Domin sosai mutuwar Nimra ta taba ba, bata iya cin komai a yanzu sai ka mata magana sau uku sannan ta amsa maka daya, irin wadanda tunaninsu yayi nisa damuwa ta sako gaba haka Ummi ta zama, musamman tana jin ita ma kamar nata mutuwar yana kusa da ita. Misalin 2pm aka yi addu'ar uku, wadanda suke kusa suka koma gidajensu na nesan ma da yamma wasu suka kama hanya, domin gaisuwar ta samu halartar mutane da daga daga abokai da dangi, Shuraim ma da ke ta shirya shiryen komawa Katsina a dole ya fasa saboda rasuwar, daman daga samuwar rai wato haihuwa sai kuma rasa shi mutuwa kenan ake yi ma irin wannan taron, ba ma kamar mutuwa.
Washe garin ranar da aka yi sadakan ukun Nimra da yamma lis guraren biyar da rabi, Ummi ta fadawa Maleek tana son ya kaita asibiti ta ga likitanta wanda ya saba duba ta. Duk yadda ta so ta fita ita kadai sai Maleek hakan be samu ba domin Waira tana jikinta tsawon kwanakin nan duk wani motsi na Ummi ta san da shi, ta kara takura matuka saboda taron da aka yi, da kuma rasa Nimra da ta yi sai take jin cewar tana ta rasa mutanen da take so take sabo da su, hakan ya saka ta shakuwarta da Ummi ya karu, Maleek kuma ya fi sassauta mata da tausayinta a yanzu fiye da can baya. Dan karamin mayafi Ummi ta saka ta yafa ta rufe kanta sannan suka shiga motar Abiey ma be so an barta ta tafi daga ita sai Waira sai Maleek ba, sai dai nuna masa cewar ta fi son zuwan ita kadai ya saka dole ya kyaleta.
Sai da suka yi nisa a tafiya ta gyara hannunta dake rike da carbi ta ce.
“Maleek ba asibiti zamu je ba”
Ya rage tafiyar motar.
“Ina zamu je?”
Ta sauke ajiyar zuciya kusan sau hudu sai a na biyar ta iya furta.
“So nake ka kai ni na ga Ameer, na san Mahmood be san gidan ba, ni ma kuma ban sani ba, mahaifinku kuma ko ya sani ba zai kai ni ba”
Maleek ya jiyo ya kalleta.
“Ummi Ameer fa kika ce?”
Ta shiru na wani lokaci sannan ta daga masa kai idonta na tara hawaye. Ganin zata zubar da hawaye ya saka Maleek saurin juyawa ya fuskancin gabansa.
“Why?”
“Ina son na san halin da yake ciki, buri na kyautatawa kowa na bawa kowa hakkinsa”
“Kina kallo amman Ummi ko gaisuwar nan be zo ba, bana son ganin fuskarsa ko kadan”
“Karka zarge shi da abun da ya faru duk laifina ne, da ban aikata abun da na aikata ba da duk haka be faru ba, shi ma baka san halin da yake ciki ba”
“Wane hali yake ciki Ummi? Halin da yake ciki ya kai wanda mu muke ciki? He's the reason da muka rasa Nimra? I will never forget that, saboda bakar zuciya da son kai irin nasa, and i will never forgive him”
“Ka kai je ka aje ni kofar gidan dan Allah sai ka yi tafiyarka”
“How comes ma za ace ke kika haife shi Ummi taya? Taya zaki haifi wannan ďan iskan wawan mahaukaci da babu komai a zuciyarsa sai sheri”
Ummi ta kai hannu ta dafe zuciyarta hawaye na sauko mata, ji take kamar ita Maleek yake zagi, domin ita ce silar komai a yanzu.
“Ya Maleek please”
Waira ta fada itama tana hawaye ganin uwar dakinta na kuka. Ta madubin gaban mota ya kalleta da hawayen da take ita ma ta kalleshi, be sake cewa komai ba ja motar. Be tsaya ko'ina ba sai a bakin gate din gidansu Ameer ba zai iya shiga ciki ba dan haka ya faka motar a waje. Ya fito ya budewa Ummi ta fito tana gyara hijabinta mai 3 in 1, Waira ta bude side dinta ta fito ita da Ummi suka doshi gate din gidan. Masu gadin na ganinsu ya mike tsaye ya bude musu gate ana musu sannu da zuwa, Maleek binsu yayi da kallo har suka shige sannan ya koma cikin motar wani irin zafin zuciya na dibarsa. Suna shiga harabar gidan Waira ta jiyo busar sarewar irin wacce Eid yake mata a garinsu, busar da babu wanda iya ta sai Eid busar da aka kirkira da tsafi, wanda wani be isa ya kwaikwaya ba, balle har ya iya. A firgice ta saki hannun Ummi ta falla da gudu sai kuma ta ja ta tsaya tana kallon gabas da yamma ta juyo ta kalli nan ta kalli can ta rasa ta ina busar take fitowa. Kara matsawa ta yi compound din sai ta jiyo sautin na fita ta wani gurin da take kyautata zaton Garden ne, da gudu ta nufi gurin tana jefar da mayafin kanta tana kuka marar sauti hawaye sharrr kamar an sako teku...
[7/5, 9:39 PM] My S Line: 48
Ummi har ta yi kamar ta bi bayan Waira sai kuma wata zuciyarta tace mata focus on abun da ya kawo ki gidan nan, dan haka bata damu ta bi bayan Waira ko kuma ta san abun da take yi ma gudu ba, sai ta nufi kofar shiga cikin gidan domin yin abun da ya kawota. Door bell din ta fara danna tare da gyara tsayuwarta, gabanta faduwa yake sosai domin bata taba risking aikata wani abu kamar wannan ba. Wata matashiyar yarinya ce ta bude mata kofar sai ta tsaya tana kallonta ganin bakuwar fuska.
“Mahaifiyarki tana ciki? Ko Ameer”
“Duka suna nan shigo”
Ta kauce daga jikin kofar Ummi tayi taking deep breaths sannan ta saka kafarta cikin falon. Katon hoton Ameer da aka zana da art ya fara mata maraba da zuwa, bata bukatar izinin zama dan haka ta zauna a daya daga cikin kujerun da suka fi kusa da ita. One after the other ta bi hotunan da suke falon da kallo cikin har da wanda Mr Bashir ya dauka tare da Ameer da kuma wanda suka yi a matsayin iyali daya da Mommy da yaranta.
“Bakuwa muka yi?”
Mommy ta fada tana saukowa a yayinda take yi ma Ummi kallon rashin sani. Ummi ta juyo ta kalli stairs fuskarta cike da damuwa.
“Eh Sannu Hajiya”
“Yauwa sannu da zuwa”
Mommy ta amsa sannan ta sauko gaba daya ta zauna a kujerar dake fuskantar wadda Ummi ta zauna.
“Sai dai ban wayance ki ba”
“Ba lallai ki san ni ba, Sunana Zahra, na zo gurin Ameer ne, ko yana ciki?”
Mommy ta kara kallonta da kyau domin tantancewa.
“Eh toh amman ba zaki iya magana da shi kai tsaye ba, ya kamata ki fara neman izini gurin mahaifinsa tukuna”
Ummi ta yi shiru tana tsoron kar a hana ta ganin ďanta.
“Na zo ganinsa ne kawai ba wani