Showing 150001 words to 153000 words out of 281271 words
komawa gidansu Ameer, ko kuma ya kaita ya barta a can har sai ta gama abun da take sannan ya daukota. A nan ya daka mata tsawa daman ransa a ɓacen yake.
“Ba zan koma ba, babu wanda zai koma gidan nan, ko sunansa na sake ji a bakinki sai na miki dukan tsiya, Ummi that's enough ba zaki sake zuwa ganin yaron nan ba, ko da ba ni zan kai ki ba zaki sake saka kafa da sunan ganin Ameer ba, ba zan jire yadda yake amsa miki magana son ransa ba i won't tolerate that”
Ummi ta yi murmushi cikin tattausan lafazi ta ce.
“Shi ma ďana ne, banbancin ka da shi kai Aliyu ne ya haifeka, Shi kuma Zaharadeen, kai sunanka Maleek shi kuma Ameer, amman a cikin uwa ďaya kuka fito, a mahaifa ďaya kuka zauna, a yanzu ya fika bukatata, domin ban samu rayuwa da shi a lokacin da yafi bukatata ba, kai ma lokacin da kake kyamata ma jure zama da kai, da duk wani abu da kake yi min har zuwa yau da komai ya yaye maka, miyasa shi ba zamu ba shi damar yin fushi har ya fahimci manufata ya sauka ba?”
“Ummi yaron nan ba shi da tarbiya idan ba haka ba, ai ko wace uwa a bar girmamawa ce a gurin ko wane ďan halak, amman daman can shi ne matar kirki a cikin abokanmu, kalli abun da yayi ma Nimra”
“Mutuwa ma tana kunyar idon mahaifiya, ya kamata ka tausasa kalamanka kuma maganar Nimra! Ni ya kamata ka dorawa laifin, ba wanda be san komai ba. Ya fahimci Ameer ďan uwanka ne na jini”
“That's the most painful part”
Ya fada ya rufe motar ta karfi ya nufi cikin gidan da wani irin fushi da Ummi bata saba ganin Maleek a cikinsa ba.
“Idan aka samu rashin hadin kai a tsakaninku, wani sabon ciwo ne a gareni, Allah ka hada min kan ƴaƴana”
Ta kama hannu Waira suka shiga ciki. A falo Ummi ta samu Dr Zaune zaune Namra na cinyarta kwance daga ita har Namra sharar kwalla suke. Namra na ganin Ummi ta tashi zaune
“Ummi ya jikin na ki?”
“Jiki Alhamdulillah”
“Me likita ya ce”
Ummi ta kalli yayar mijinta wato Dr Zainab sannan ta kalli Namra ta ce.
“Ya ce jiki da sauki babu wata matsala”
“Ummi Allah ya baki lafiya, dan Allah ki yarda da maganar Abiey ya ce zai fitar da ke waje a duba lafiyarki”
Ummi ta saki hannu Waira ta zauna tana kallonsu.
“Daga ina kuma wannan ya fito?”
“Ummi ba zaki iya boye mana komai ba a yanzu, Dr ta fada min Abiey be dade da tashi anan ba, ya fada mana komai”
Namra na fada tana nufar inda take, sai ta rumgumeta tana kuka. Ummi ta shafa bayanta.
“Da sauko fa karki daga hankalinki, babu abun da zai faru, komai ai sai Allah ya kaddara yake faruwa”
“Allah ya barki cikin zuri'arki Zahra”
Dr Zainab ta roka tana jin tausayin Ummi, sai dai karfin hali irin na uwa dake kokarin kwantar da hankalin kowa ya hana Ummi zubar da kwalla ko daya, sai murmushin da take.
Bayan sallah la'asar Waira ta sauko rike da jakarta ta nufi dinning sai da ta kauce duk abu da zai takura mata a kam dinning table din sannan ta dora jakarta ta cire littafanta tare da abun rubutu ta aje ta fara bude textbook dinta tana kallo.
“Yau kuma nan ake karatun Waira? Ba akwai dakin karatu ba? Kuma a dakin ki ma an saka miki kujerar zama da teburin karatu ko?”
Cewar Ummi tana dire flask din ruwan zafi a dinning din.
“Na tafi can?”
Ummi ta yi murmushi ta shafa kanta, sai idonta ya cika da hawaye tana tunawa da Nimra.
“Aa zauna a nan, amman dai kar wani yayi miki wani abu ki ce an miki ba daidai ba, nan gurin cin abinci ne ba gurin karatu ba”
Da kai Waira ta amsa mata ta cigaba abun da take har sai da ta ga Ummi ta bar falon ta koma kitchen saboda shigowar Hanne. Sannan ta tashi da kamar sanda ta nufi upstairs ta hau, bangaren da dakinta yake ta nufa kamar zata shiga sai kuma ta wuce dakinta ta tsaya bakin kofar dakin Maleek, har yanzu zuciyarta da kwadayin son zuwa gurin Ameer dan haka take jin kamar idan ta yi ma Maleek magiya zai yarda ya kaita. A hankali ta murda kofar dakin ta bude ta leka, sai ta hango shi zaune kan kujera yana fuskanta windows din dakinsa dake bude, bata san abun da yake ba domin kansa a kasa yake yana ta rare karatun Al'qur'ane, baya ta yi kadan ta yadda ba zai hango ta ta tsaya rike da kofar tana sauraren yadda muryarsa take da dadin gurin karatun, yadda yake jan aya ya direta ya dauki wata ya tafibda tunaninta, zakin muryarsa da kuma dadin abun da yake karantawarta ya saka ta tsayuwa jikin kofar har ta kai zaune ta tsanu tana jin ayayoyin da bata san akan me suke magana ba, wani yare ne mai dadin sauraro da saukar da natsuwa,ba wannan ne karon karfo da ta ji karatun a gidan ba, sai dai bata taba maida hankali ta saurara da natsuwa ba irin yau, kuma wani be tana karatu da murya mai zaki ba irin ta Maleek, wannan ne karon farko da taba jin Maleek yana karatun, a yanzu kam ta tabbatar wannan yaren ya fi nata da na su Ummi da kuma wanda aka koya mata wato turanci dadi nesa ba kusa ba. Shi yake karatun ita tsigar jikinta yake tashi ji take bata taba jin wani abu mai dadi saurarowa irin wannan!
Dan juyowa yayi kadan sai ya lura da kofar dakin dake bude kadan, ga kuma inuwar mutum a zaune, be tabbatar ba amman zuciyarsa ta raya masa cewar Waira, domin ita kadai zata yi masa haka, Namra ya san idan tana bukatar wani abu zata iya masa magana, balle ma dakinsa ba gurin shigowarta ba ne tun a lokacin baya hakan ya saka sai suka dauke kafarsu daga dakinsa gaba daya, Ummi ma dake shigowa ba zata masa labe ba. Yana kawai a karshe aya, ya rufe qur'ane ta aje ya tashi ya nufi kofar ya bude tana ganinsa sai ta mike tsaye da sauri ta daga kai tana kallonsa ta manta da hawaye a idonta har sai da ta ga yana kallon fuskarta.
“Cry???”
Ta saka hannu ta sauri ta share.
“Abun da kake yi ne?”
Ta fada a shagwabe, sai ya tsaya tunani domin be san wani abu da yake ba.
“Oh karatu?”
Ya tambaya tunawa da yayi. Sai ta daga kai masa.
“Shi me yasa baka koya min ba?”
“Shi ak karatu ne, wani bangare ne na ibadar mu, ke kuma ba Musulma ba ce”
“Ke ma ba kuna da ibadar ku ba?”
“Yes amman wannan karatun yana da dadi, na ji wani iri karatun akwai dadi”
He's not in the mood if not da sai yayi mata murmushi ko kwararran bayani, sai dai shi ma yana cikin bacin rai na abun da Ameer yayi da kuma bakinciki rashin kanwarsa Nimra, wannan ne silar karatun al'qur'anen da yake da yamman nan domin samun walwala.
“Why are you here?”
Bata san tana da wayon iya roko ba sai a lokacin, kamar wata almajira haka ta zube kasa ta hade hannayenta ta daga kai, daman sai da daga kai kam tana tsaye ma ta daga kai ta kalleshi balle ta zube kasa. Marairaice murya ta yi ta fara masa magiya.
“Please Ya Maleek i know you hate me, but please ka kai ni gurin Ameer, ina son magana da shi, please”
Da hannu yayi mata nuni da ta tashi ta fice domin ya lura bacin rai kawai take son kara masa. Sululu a tashi ta juya ta fara tafiya tana yi tana waigensa shi kuma yana tsaye bakin kofar yana kallonta har sai ta sauka. Dinning ta dawo ta zauna tana kuka domin jin busar sarewar da ta ji Ameer yana yi tana son ta sake jin irinsa kuma tana son ta yi masa tambayoyi akai idan ma bata masa tambaya ba zata so rumgumarsa ta san komai. Tana tsaka da matsar kwalla mai goge mata uniform ya danna door bell din kofar, sai ta gwada yin karanbanin budewa domin bata taba mata gwada budewa wani kofa ba, ko da yi knocked din kofar sai dai ta yi ta kallo ko ta fadawa wani an taba kofa a zo a bude amman ita ba zata bude ba. Sai dai yau yadda ta ga Ummi na yi idan zata bude kofar haka ta yi har ta bude.
“Hajiya Waira yau ke ce da bude kofa?”
Cewar Haruna yana rike da uniform dinta da ya goge hannunsa. Kallonsa kawai take kamar wata marar wayo bata ce masa komai ba, sai yayi murmushi ya mike mata kayan.
“Gashi an goge, kuma malaminki ya iso tun dazun yana jiranki”
Da zumudi ta karbi kayan bata ko iya kaisu dakinta ba ta aje su akan kujera ta nufi dinning ta dauki jakarta da kayan karatunta ta fice da sauri. Kamin ta isa inda yake har da hadawa da gudu, sai dai yanayin yadda ta yi arba da fuskarsa ya katse duk wani hanzarinta. Zaunawa tai tana kallon yanayinsa da alama dai kam yau ransa a bace yake matuka.
“Good Evening”
Ta fada tana kallonsa sai ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba, a ka'ida idan zai mata darasi na gaba sai ya yi mata tambayoyi akan darasin da aka yi na baya, sai dai be yi mata tambaya ko daya ba ya cigaba da dora mata daga inda ya tsaya a kwana ukun da suka wuce. Sakancewarta mai fahimta ta maida hankali sosai akan darasin har aka yi aka gama. Yana kokarin maida kayan da yayi mata karatu da su a jakarsa ta kalleshi.
“Wani ya bata maka rai yau ko Uncle”
Ba tare da ya kalleta ba ya amsa mata.
“Baki marmarin gidanku ne? Baki kewar garinki da mutanenki ne? Akwai abun da yake burgeki a nan?”
Ta sauke kai kasa tana taba littafin dake gabanta.
“Ina yi, amman....”
Ta kasa karasawa bata son ta fada masa cewar tsoron komawa take. Sai kawai ta saka hannu ta share hawayen da suka cika idonta.
“Abubuwa da yawa suna burge ni a nan”
Ta dago ta kalleshi.
“Kamar rayuwarsu, yadda suke mu'amala ababen hawansu, yadda uwa take kula da yayanta, yadda suke rayuwa a gidan nan, yarensu, da kuma yadda zuciyarsu take da son mutane da nuna kauna ga kowa, ni ba jininsu ba, ba yar garin ba amman Ummi ta nuna min kulawa da soyayya, kamar a garinmu idan ba jininmu basa son kowa basa barin kowa ya zauna, basa maraba da kowa, basa yarda su koyawa kowa yarensu”
Ya tsayar da abun da yake ya kalleta.
“Ashe kenan a garinku wani be isa ya auri jininku ba? Haka ne?”
Ta daga mishi kai.
“Toh sai ki kiyaye dokokinku, ina kara jaddada miki, karki kuskure watsarda al'adarki da addininki saboda na wasu, su ma suna nunawa mutum kauna ne kawai idan be shiga a cikin addininsu ba, da zarar kin jefar da addininki kin shiga na su, a nan za su canja miki har sai kin tsorata da lamarinsu”
“Kai ba addininsu kake yi ba?”
Ya kalli kansa domin shigar musulunci ce kuma shigar bahaushe a jikinsa kamar yadda fuskarsa take da gemu da tsaje.
“Addini mu daya da su, shiyasa nake baki labarin abun da baki sani ba, saboda ina tausayinki, mu muna boye hallayarmu ne har sai idan mutum ya bar addininsa ya shiga da mu. Ke wai baki tunanin komawa garinku ne?”
Ta girgiza kai alamar aa bata so.
“Wata kila zuwa yanzu, sun shiryar karbarki sun shirya yafe abun da kika yi”
Ta mike tsaye tana kallonsa.
“Ya aka yi kasan sun shirya karbata? Waya fada maka guduwa na yi?”
Yayi yar siririyar dariyar da zata batar da tunaninta.
“Waira, ni fa ba yaro ba ne ina fahimtar komai, ko da baki fada min ba na fahimci hakan ne ta yanayin maganarki da kuma fuskarki kana da mu'alamarki, ni mai matukar kaunar farincikinki ne ƴata”
Ta kasa natsuwa da kalamansa, ta san gaskiya ya fada yayi yata da bakwai da ita, amman yadda ya fadi wasu abubuwan akanta a yanzu ya saka ta tunani.
“Me yasa baka zo jiya ba”
“An yi mutuwa ai”
“Waya fada maka?”
“Na zo na tararda gidan a cike da mutane, na tambaya sai aka fada min mutuwa aka yi”
Ta saka littafanta a muhalinsu ta dauki jakarta ta juya ba tare da tace komai ba. Sai ya kirata
“Waira”
Ta juyo ta kalleshi.
“Karki da al'ummarki, karki yada al'adarki, karki manta da mutanen da suke ta fafuka akanki, memory ki na kurciya ya zauna a kanki, rayuwar da kike a garinku tana da dadi fiye da nan”
Kasa ce masa komai ta yi ban da ido data sakar masa har ya dauki jakarsa ta karatun ya nufi gate yana dingishi kamar gurgu.
9:23pm
Ummi ta aje kofin shayi biyu a gaban Abiey, ma farkon ta fara dauka ta mikawa Abiey sannan ta dauki dayan ta mikawa Dr Zainab dake zaune a falonsa.
“Aa ku sha tea ai sai ku, ni idan kin ga na sha tea safiya ce zan yi breakfast”
Ummi ta zauna rike da kofin tana kallon Abiey da ke bata umarni babu wasa a maganarsa haka ma a fuskarsa.
“Wannan ya zama na karshe da zaki sake dafa min wani abu, na san aiki zai yi ma Hanne yawa dan haka na yanke shawarar zan karo wasu masu aiki”
“Ciwona ba zai hana ni yin komai ba ranka ya dade, dan abun da nake dafa maka ai ba wani abun wahalar ba ne”
“Ba shawararki nake nema ba, hukunci ne da na riga na yanke, kuma idan abubuwa sun dan laba zamu fita waje a duba ki a can hankali zai fi kwanciya kuma zan fi samun gamsuwa idan a can ne, saboda suna da kayan aiki masu kyau”
Dr Zainab ta tari numfashinsa.
“Yanzu ma yake min maganar rage wasu ayukan ma office, saboda ya samu time din zama a gida kuma na yaba da hakan, daman ina tunanin lokaci yayi da ya kamata ace ya sauwake kansa wasu abubuwa ya huta”
“Duk saboda ni? Haba dan Allah karku sauya rayuwarku saboda wannan, ba abun mamaki ba ne Allah ya bani lafiya mai daurewa, wata kila ma sai duk kun rigani mutuwa”
Dr ta yi murmushi tana zolayar Ummi.
“Ban ji bakinki gashi ina son na tafi Kano jibi idan Allah ya kai mu”
“Jibi kuma?”
“Eh tun da na zo ina nan Abuja, ai ya kamata na leka gida na ga yan'uwa da iyaye, jibi idan Allah ya kai mu zan tafi Kano, Jabir ma na ji yana zancen tafiyar gobe ban sani ba ko ya fasa”
“Zaku kara mana kewa Auntie”
“Toh ya za'ayi abun da ya zama dole ai dole ayi shi, daman bayan taro sai raguwa, amman dai ina bada shawarar ku sake bincika yan'uwan yarinyar Waira take ko Wara? Saboda akwai rai akwai mutuwa”
Abiey ya kurba tea ya aje ya dauko wani zancen domin baya son maganar da Dr Zainab ta yi ta Waira.
“Sauban ma yace min gobe zai koma, amman kamin ya tafi zai sake dawowa”
“Yayi kokari ai sosai Allah dai ya bar zumunci, kun zama yan'uwan kai da shi”
Cewar Dr Zainab kamin ta kalli Ummi dake fadin.
“Waira tana son zama da mu Auntie, kuma ta fada mana matsalarta, ko ba komai tana rage min kewar Nimra, idan aka dauketa zan yi kewa sosai kuma ita ma ba asan halin da zata fada ba”
“Zamu yi wannan maganar daga baya, for now yarinyar tana tare da ke, karki saka damuwa a ranki”
Yadda Abiey ya mika hannu ya dafa kafadar Ummi yana bata magana ya matukar burge Dr Zainab, hakan ha tabbatar mata har yanzu kanenta yana bawa matarsa kulawa. Ummi ta mike tsaye rike da tea
“Bari na baku guri”
“Okay”
Abiey ya amsa yana binta da kallo ransa na ƙuna,a yanzu ta fi zame masa tashi hankali fiye da mutuwar Nimra domin ita dai ya san ta tafi kenan, tsabanin Ummi da ciwo ke tare da ita. Waira na ganin Ummi ta mike tsaye ta nufi Ummi tana fadin.
“Ummi zaki kira min Sulem ko Ameer please?”
“Ba ni da number Shuraim, Namra ce mai number sa, Ameer kuma idan na kira na san ba zai daga ba”
“Zai daga Ummi please ki kirashi”
“Toh kai wannan Kitchen sai ki dawo na kira shi”
Ta karbi tea ta nufi hanyar kitchen, tana shiga ta samu Maleek tsaye yana sakawa kansa kankara. Kallo daya ta yi masa ta dauke kai ta nufi kusa da inda hake ta aje ta dauki abu ya rufe sannan ta juyo. Samun kansa yayi da binta da kallo, ya sani da a da ne sai ta fada masa abun da ya kawo ta kitchen din sannan ta yi dakon jiran umarnisa kamin ta aje. Sai dai a yanzu bata yi ko ďaya ba, hakan kuma sai ya ji kamar dan dame shi, fushi take da shi? Or ranta ne a bace? Be raba ďayan biyu ba aje kankarar ya fito daga kitchen din, yana daf da ficewa falon ya ji Ummi na fadin.
“Shiga ďakina ki dauko wayar sai a kira shi”
[7/8, 5:19 PM] My S Line: 50
Yana rike da wani littafi na turanci yana dubawa kanwarsa Fiyya ta turo kofar dakin a hankali ta shigo.
“Ya Ameer”
“Favorite”
Ta fada ba tareda ya dago ya kalleta ba. Sai ta zauna kusa da shi tana leka abun da yake dubawa, a lokacin ya kalleta.
“Wani abu kike so?”
“Ya Ameer duk ka canja, kusan three days kullum kana daki”
“Fiyya baki san abun da ya faru ba ne?”
“Na sani, amman faruwar wani abu zai canja alakata da kai ne? Zai tashi matsayinka na yayana ne? Ko kuma zai canja ka a matsayin ďan Daddy? Har abada kai yayana ne, fitowar wannan abun ke kara mana komai ba sai kaunarka, Mommy tace kar mu kuskura mu tattauna wannan maganar ko da yan'uwa balle kuma wani a waje ya ji, ta ce mu aje wannan maganar a cikinmu, dan Allah ka dawo da mu'alamarka yadda ka saba, wannan takura kanka da kake muma muna takura da shiga damuwa sosai”
Yayi murmushi.
“That's