Showing 165001 words to 168000 words out of 281271 words
abu ne mai sauki ba, kuma ban cancanci ko wace kalar alfarma a gareka ba”
“Idan kina bukatata a kusa da ke, you can make a room for me, sai na dawo gidanki na zauna, i need to know who you are, me kike so miye baki so, ya rayuwarki take. It tear me up when you turn me down, ina son na ji ɗumin uwa how it's? To get to know you”
Yana fada yana kuka kamar karamin yaro. Ta girgiza kai.
“I don't want to force you”
Bude motar yayi ya fita ya rufe ya dawo back ya bude ita dai binsa kawai take da ido har ya shigo.
“You didn't force me, ni nake neman wannan alfarmar, ni dai kawai ina bukatar uwa ne, ko da wata uwarce ba ke ba zata tsaya a gabana tace ita ta haife ni, zan karbeta you leave a empty place here in my heart, i want you to fix it, that's little boy you left is still inside me, and he need a mother, i want to make a motherhood memory now”
Kuka yake Ummi ma kukan take jikinta na rawa tana son ta taba shi ta kasa, wannan karon ba tsoro ne ya rufe ba kunya ce irin na uwar data kasa bawa ďanta kulawa har sai da ya bukata. Ya saka rigarsa ya share hawayensa sannan ya fita daga back seat din ya rufe mata motar, jinginawa yayi motar ya na dan lokaci kana ya bude ya shiga ya cigaba da tuki, a gabansa dazun wata ke tsoron rasa nata iyalin shi kuma kari ma ya samu dan haka ba zai iya barin wannan damar ta wuce ba, ko dan ciwon da Waira ta fada masa Ummi tana yi. Kalaman da ya furta mata a yanzu sun yi effecting dinta, ji take kamar wani dafi ya saukar mata a jiki, kalmominta sun tsare jikinsa she couldn't hold her tears har suka isa gidan. Ya faka motar harabar ya ciro tissue da ya gani ya mika mata.
“I'm sorry please stop crying, a yanzu bana son kowa ya zubar da hawaye a kaina, ni ma ban kyauta miki ba ni ne silar mutuwar yarki Nimra wacce kanwa ce a gurina”
“No Nono daya kuka sha, she and her sister they are my step-daughters, kuma ba kai ne sila ba kawai Allah ya kawo ne, karka haka a ranka, idan ma laifi ne ni ce mai laifi ni ce silar komai”
Ta karba ta share hawayenta sannan ta bude gefenta ta fita, shi ma fita yayi ya jingina da motar yana kallonta.
“Waira tana ciki?”
“Kana son ka ganta ne?”
“I always wanted to see her, zata raka ni na dauko wasu abubuwan ne a gida, kamin mu dawo make sure my room is clean”
Ummi ta kara dubansa da kyau.
“Da gaske kake Ameer?”
“I need you by my side, ya zan yi?”
Hannu ta saka ta dafe kirjinta idonta ya sake cika da hawaye.
“Thank you so much for this opportunity, na gode da ka zabi zama da ni, thank you for everything Ameer Allah ya maka albarka, Waira zata zo yanzu. Thank you”
Ta furta sannan ta nufi hanyar falon tana jin wani kukan da bata san na minene ba ya sakota gaba, farincikin Ameer zai zauna da ita ne? Ko kuma na kuskuren da ta aikata a baya ne? Ko kuma na rayuwar da take tunanin ba za'a bata aro ta dade tare da ďanta ba ne? Barin jikin motar yayi yana fara zagaya harabar gidan yana kallon yadda tsarin gidan yake. Ba laifi su ma sun zubar da dukiya a ginin gidan kamar yadda aka zubar a gina na su, domin komai yayi tsarin ginin kadan ya banbanta da na Daddynsa. Yana tsaye Waira ta nufo inda yake da gudu tana murna, doguwar rigar material ce sanye a jikinta sai bakin talkami da karamar safa da ta rufe kafafuwanta kanta babu dankwali gashin kanta ya kwanta da kyau kana gani ka san ya sha gyara, sai kamshi take zubawa irin na manyan larabawa.
“Welcome”
A take dadin muryarta da shaukin ganinta ya wanzar da murmushi a fuskarsa.
“Thank you”
Ya amsa yana kallon yadda ta bude masa hakoranta ita kawai muryar yace zai zauna a gidan take. Ya kalli kanta.
“Ke miyasa baki son ďankwali? Baki rufe kanki? Kin ga gidan nan akwai maza da yawa kuma za a iya cewa yayi kyau ko ki burge wani”
“Su waye mutane?”
Ya wara ido yana kalle-kalle sannan ya kalli abun da ya fi daukar masa hankali a fuskarta wato idonsa.
“Masu aiki aljannu, ranar ma da wani saurayi na ganki a mota ga kuma Maleek da Mahmood”
Ya karasa yana rage murya kamar baya son a aji.
“Ni bana son komai a kaina, a garinmu ba a rufe kai, bana son rufe kai na”
“Mu kuma a nan ana rufewa ai, kin ga ko hulace ya kamata ae kina sakawa, idan a garenku ba ayi a nan ai ana yi, ko baki san kin girma ba? You're not that small child”
“Na sani, ni kawai bana son rufe kai ne”
“Sai idan zaki yi Sallah kawai kike rufewa?”
“Ni bana sallah ai”
Ya matso kusa da ita da mamaki.
“Ba ki sallah kamar yaya? Baki ga mutanen gidan suna sallah ba?”
“Na gani?”
“Uhmm?”
Ta motsa kafada.
“Bana yin irin addinku”
“Ohh too bad, Babe you missed alot, akwai wani irin natsuwa, da imani da kusanci da aminci da rahma da tsaro a cikin ganawa da Ubangiji, shiyasa bana yarda ko da raka'a daya na rasa balle kuma jam'i, kin bar dadi yarinya”
“Bana son na bar addinina, ko malamin dake mana lessons ya ce kar na kuskure na sake aikata laifi biyu kar na bar addinina”
“Christian ne?”
“Aa irin addininku yake”
“Kuma yake son hana ki, yana son karki kwashi rahma da lada ne kawai, ke baki ga yadda Ummi take yi ba? Be burgeki ba?”
“Ya burge ni, amman dai bana son na bar addinina”
“No one will force you, sai dai na miki alkawari matukar ina gidan nan sai rayuwarki ta haskaka zuciyarki ta bude ki karbi gaskiya”
Zancen zama a gidan da yayi ya tuna mata da abun da Ummi ta fada mata, cikin zumudi ta ce.
“Ummi tace zaka zauna a nan da gaske ne? Wai na raka ka zaka dauko kayanka?”
“Yes for, for her. Happy?”
Ta yi tsalle.
“Yes, can I hug you?”
“Da can da kike rumgumata izini kike nema?”
“Toh ai Ya Maleek ne ya ce ba kyau, wai harame ne”
Ta fada a shagwabe tana dan turo baki gaba, kalmar Haram ta kira da Harame domin haka kalmar ta zauna a kanta. Ya sakarwa fuskarta ido babu ko kyaftawa.
“Ke ai yanzu baki san banbancin Haram da Halal ba, hukuncin be hau kanki ba”
Ya rage tsawo tare da mika bakinsa ya sumbanci karan hancinta, yana dagowa motar Maleek na kunno kai cikin gidan, sai da ya kalli motar sannan ya sake maida bakinss ya sumbanci saman fatar idonta dake rufe tun a lokacin da ta ji numfashinsa na kokarin kwaurawa da nata. Jin karar motar ya saka ta bude idon da sauri ta juyo tana kallon motar dake fake saitinsu sai dai nesa da su, hakan kuma be hana ta yi ido hudu da Maleek ba, da ya kasa fitowa motar sai kallonsu yake, yaƙin duniya na uku na shirin haduwa a kirjinsa, yan sojojin zuciyarsa sai kawo makamai suke, jinin dake circulating a a jikinsa yana jefo masa da bomabamai.
[7/17, 6:22 PM] My S Line: 54
After two weeks later...
Yana tafe Fiyya na bayansa rike da basket din da Mummy ta zuba masa kulolin abincin da za a kawo asibitin. Shi ya fara tura kofar ya shiga ya rike mata kofar ta shiga sannan ya rufe. Fiyya ce ta fara karasawa gurin gadon ta aje musu abincin tana yi ma Tsohuwar ya jiki tare da isar musu da gaisuwar Mummy, domin ita bayan kwana biyu take zuwa ta duba su, kanensa kuma time time idan zai so ko direba zai kawo abinci, Ameer kan kullum idan zai je aiki ko ya dawo sai ya shigo asibitin duba tsohuwar, domin jin yake kamar nauyinta a yanzu yana kansa.
“Ya jikin?”
Ya tambaya yana kallon Tsohuwar dake rike da ayaba tana ci.
“Jiki Alhamdulillah ďan nan, Allah yayi albarka kana ta fama da dawainiya”
Humaira ta mike tsaye ta bashi kujera, sai dai ta san ba zai zauna ba, domin ba gwada zama a dakin ba duk zuwan da yake.
“Kullum zai kin kin ba ni kujera, kuma kin san ba zama nake ba”
Ta yi murmushi.
“Ina jin ba dadi ne ace ina zaune kana tsaye”
“Kuma kullum sai na tararda ke a nan ke kike jinyarta bayan ga mahaifiyarki, ba kasafai nake tararda ita, Allah yass dai kina zuwa aiki”
“Duk lokacin da zaka zo kana sa'a da ina nan ne shiyasa, aiki kuma na daina zuwa ai tun a wacan lokacin”
Ya daga mata kai.
“You got lucky na canja if da yanzu na koreki”
Dariya Fiyya ta yi kamar yadda Humaira ma ta yi dariyar.
“Baka bukatar ka koreni ai, ni na kore kaina?”
“Why?”
Ta daga kafadunta.
“Kawai dai”
Be sace cewa komai ba, ya kalli agogon hannunsa.
“Kuna bukatar wani abu?”
“Aa bama bukatar komai a yanzu”
Shigowar da Dr yayi ne ya katse hanzarinsa daga yi musu sallama ya fice. Likitan dake cikin shiga ta kayan likitoci ya iso gurin ya mikawa Ameer hannu suka gaisa.
“An fada maka sakona”
Ameer ya kalli Humaira wadda ta dago tana kallon Likitan.
“Yanzu nake kokarin yi masa bayani”
Likitan yayi murmushi.
“Kin manta kenan?”
“Aa na tuna yanzu da na ganka”
Ta fuskanci Ameer dake jiran abun da zata fada masa.
“Yace gobe za a kwance daurin da aka yi mata, a duba, idan yayi haka ake so, idan kuma be yi ba sai an sake wani”
Tana fadar idonta na cika da kwalla.
“Sarkin kuka daga magana sai hawaye, haka jiya kika min fa”
Likitan ya fada yana kallonta.
“Bana son tashin hankali, ba mu da yawa a dangi kusa, bana son na sake rasa kowa”
“Ba saki rasata ba, aiki ne kawai kuma ni ba cinye ta zan yi ba, I'm not zombie”
Ta yi murmushi tana share hawayen idonta.
“Ni ban ce ba”
“Da dai yafi”
Duk abun da ake Ameer be ce uffan ba, sai kallon tsohuwar dake cin ayarba hankali kwace yake kamar ba ita ake fadar za a sakewa aiki ba.
“Ita hankalinta a kwance ma yake naki ne a tashe”
Likitan ya fada yana kallon Humairah
“Toh abun da Allah ya kawo ba sai hakuri ba, gwagwarmaya wace kala ce ba mu gani ba?”
Ameer yayi murmushi yana kallonta, karfin halinta da imani ya burge shi.
“Allah ya kara lafiya”
Ya fada sannan yayi ma Fiyya alama da su tafi da ido, Fiyya ta yi musu sallama suka fice. Likitan ya juya ya kalli Ameer har sai da ya fice sannan ya maida dubansa gurin Humairah.
“Am ya sunanki ma?”
“Humairah..”
“Haka ashe na rike sunan”
Ta yi murmushi tare da sauke kai kasa, sai ya dauki file din da ya shigo dashi bayan ya gama duba Tsohuwar ya fice. Zaunawa Humairah ta yi tana fadin.
“Yau Mama bata zo da wuri ba, gashi ina son na shiga makaranta kar na yi latti”
“Ki zuba min abinci da aka kawo sai ki tafi, ai zata zo wata kila ta tsaya wanke tsumman da tafi da su jiya ne”
“Maybe”
Ta dauki plate din ta bude coolar jalof din shimkafa ce da aka yi mata ado da doya ta sha kayan kamshi da vegetables ga kuma mai har yayi yawa. Rabin plate ta zuba mata ta dora mata a saman gadon ta matsa mata da ruwa kusa.
“Ba zaki ci abincin ba?”
“Sai na dawo zan ci”
“Toh Allah ya kiyaye hanya, yau ba su bada kudin da suka saba fadawa ba”
“Yau da gobe ai sai Allah Hajiya, wata kila sun fara gajiya ne ko kuma sun manta”
“Ba dai gajiya ba, sai dai ko mantuwa amman dan dan abun da suke ba mu ai be taka kara ya karya ba a dukiyarsu. Ni ba dan ba a son kaddara ba ai da na ce kara da aka yi haka, dubi ki ga kullum sai an kawo abinci, ga kudin nan, kuma sun dauke duk wata hidima ta asibitin nan, gaskiya suna da kirki, ko da can ke ce da masifar ki kike ganin kamar ba shi da kirki, kullum fa sai ya zo, mamansa ma kullum tana hanya”
“Hmmm Hajiya, ke dai kin ganshi kawai amman da can ba haka yake ba, yanzu ne ya canja”
“Ke ma ai na san halinki fitina ta miki yawa”
Ta yi dariya ta nufi gefen gadon Hajiya ta dauki jakarta ta goya, sannan ta yi mata sallama ta fice, tana tafiya harabar asibitin ta ji an kira sunanta.
“Humairah”
Ta dan juyo kadan sai ta yi arba da Likitan dazun, murmushi.
“Doctor”
“Na'am fita zaki yi?”
“Eh makaranta zan je”
“Wace makaranta? Ina kike karatu”
Ya jera da ita suna tafiya.
“Sky King University”
“Ah makarantar manyan mutane kenan, wane course?”
“Microbiology”
“Wow, ke babba ce”
“Kune manya ai”
“Kika ce ba, muje na sauke ki”
“No akwai inda zan biya kamin na wuce”
“Karki damu duk zan iya sama direbanki, kin ga wata rana zan yi alfahari na ce na taba daukar Humairah yar Microbiology a motata, zan ce ta yi min alfama ta shiga motata”
Murmushi ta sake yi ta girgiza kai.
“Bana son zolaya, Likita za'ayi ma alfama?”
“Eh mana ke baki san babba ce ba?”
Bata son jan zancen da tsawo dan haka ta yi shiru bata sake cewa komai ba har suka isa gurin motae yar yayi mai matukar kyau, kana ganinta kasan sabuwar mota ce, sai da ya saka key sannan ta bude front seat ya shiga ta zauna.
AMEER POV.
A Area 2 ya sauke Fiyya gidan wata kawarta da zata yi birthday, sannan yayi driving kansa zuwa gida, tun a harabar gidan yake kallon bakuwar motar da ke fake a compound din. Domin ba ta yi kama da motocin gidansu ba, yanayin yadda akai parking din ma ya fahimtar da ba direbobin gidansu ba ne. Yana wasa da key hannunsa ya shiga falon, sai ya samu Mummy da Ummi zaune, Daddynsa yana kan dayar kujerar fuskarsa dauke da murmushi. Ummi na ganinsa ta mike tsaye kamar karamin ma'aikaci ya ga boss dinsa.
“Ameer ka dawo”
Daddy ya fada, sai ya nufi inda Daddy yake ya zauna yana yi ma Ummi kallon tsanaki, ta yi rama sosai farinta ya wuce na ainahin fatarta wani fari ne mai sheƙar da fata, fatan idonta ta yi fari kana kallonta ka san lafiya bata isheta ba.
“Baka gaishe da Mamanka ba, tun fitarku take nan tana jiranka”
Mummy ta fada tana murmushi, still be ce komai ba, sai kallonta kawai yake. Hakan ya saka Ummi jin wani iri sai ta ji kamar ta tsargu, domin ganin take komai ta yi ma Ameer a yanzu ba zata burge shi ba.
“Na zo ne kawai na ganka, Daddyka ya fada min abin da ya faru, ina addu'a Allah ya tsare gaba, kuma idan ka ba ni dama ina son ni ma naje na dubata for the sake of you”
Ta karasa maganar muryarta na rawa kamar mai tsoron abun da zai fito daga bakinsa. Ya dauke kai sannan ya mike tsaye.
“Lemme drop her home”
Fadar sai sauke ta a gida, abun mamaki ne a gurin Mummy da kuma Mahaifinsa Daddy ya san da be son ganinta ba zai sauketa gida ba, ba ma zai zauna a falon ba, sai dai Daddy be san manufarsa ta yin haka ba, hakan ya saka shi mikewa tsaye tare da kai hannu ya dafa kafadarsa.
“Karka fada mata magana marar dadi please”
Cikin wata siga mai kamar rada ya fada masa haka, Ameer ya girgiza kai.
“Ba abun da kake tunani ba ne”
Yana bashi amsa ya wuce yayi gaba, Ummi ta dauki jakarta zuciyarta na raya mata maybe Ameer zai yi amfani da wannan damar ne ya fada mata karta sake zuwa gidan duba shi. Mummy ta rakota har gurin motar ta tuko kanta, hakan ya saka Ameer barin jikin motarsa ya iso gurinta ya mika mata hannunsa.
“Key”
Ta ciro key a jakarta ta mika masa, ya nufi motar ya bude mata backseat, ta ji kamar ya karramata yayi mata alfarma a cikin daruruwan mutane.
“Hajiya na gode sai anjima”
“Toh Allah ya kiyaye hanya, ni ma zan shigo wani lokacin In Shaa Allah”
“Allah ya nufa”
Ummi ta fada sannan ta nufi motar ta shiga, Ameer ya rufe motar ya zagaya ya shiga mazaunin direba yayi ma motar key. Yana tukin Ummi na hawaye ko da ace ba a cikin dadin rai Ameer zai tukata ya kaita gida ba, ita abun farinciki ne a gurinta.
“Karki sake zuwa duba ni, idan kina son ganina ki min waya zan zo”
Ya fada yana tukin a hankali.
“Ba lallai idan na ce ina son ganinka ka zo ba”
“Saboda me?”
“Saboda ban kyautata maka ba, a lokacin da kake bukatata, na san kana kallona da wannan abun a kullum”
Yayi shiru na tsawon lokaci kamin ya sake fadar.
“Me yasa to kika yi?”
Hannu ta saka ta share hawayen idonta.
“A lokacin ina tsoron rasa rayuwar mahaifinka ne, saboda likitoci sun tabbatar min, idan ba a yi masa aikin ba, zai iya mutuwa, mun siyar da gidan gadonmu da kayan dakin Yayata Maryam mun hada duk be wadatarwa na bi yan'uwana da abokan mahaifina, kowa be taimaka min ba, ina cikin wannan halin ne Dr Hamid ya kawo min mafitar cewar akwai wacce take son siyen ciki, idona a rufe na aminta aka siyar, sai bayan da aka yi aikin mahaifinka sai kuma rayuwa ta yi bankwana, babu yadda ban yi ba saboda na gudu da cikinka amman ban samu dama ba, saboda ina da talaka ba ni da ikon komai, a cikin yarjejeniyar da aka yi da Hajiya Jamila ance idan har na karya alkawari zan biya kudi mai yawa, kuma ba ni da su...”
Ta yi shiru saboda hawaye dake mata zuba suna son su ci karfinta su zame mata kuka.
“Su waye yan'uwa mahaifina? Ban san su ba”
“Idan kana son sani, zan fada maka su, zan tafi da kai har Kano ka gansu”
“Sun san abun da kika aikata?”
“aa ba su sani ba, duniya tana kallon ďan da na haifa da Deen a matsayin mataccen”
Hawaye sun saukowa Ameer, sai ya kara rage gudun motar ya faka gefen titi ya