Showing 90001 words to 93000 words out of 281271 words

Chapter 31 - Wani Gari Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1267

din kar karyar ta yi yawa”

Yayi wani shegen murmushi yana lila da kujerar office din.

“Alright gani nan zuwa”

Ya aje wayar ya mike tsaye ya dauki keys dinsa ya fice daga Office din, sa sassafar ya sauko ya fito waje da tafiyarsa irin ta zarumai da basa jin wahalar komai kamar yadda basa da nauyin kowa akansu. Motarsa ya shiga ya murza key ya fita daga Kamfanin tana tuki a hankali, ransa be bace ba sai da ya kai gurin traffic, wani guntun tsaki yaja ya danna horn da karfi yana jin kamar ace zai iya taka motocin dake gabansa ya wuce, traffic na ďaya daga cikin abun da ya tsana a hanya. Ta cikin bakin gilashin motarsa ya hango wata kyakkyawar yarinya take cikin School Bus, tana sanye da uniform ta rumgume jakarta ta Teddy kana ganinta kasan a tsorace take, ta yi parking din gashin kanta baya, fara ce sol bw tabbatar da hakan ba sai da ya sauke gilashin motarsa yana kallonta, ji yayi kamar ya santa ko kuma ya taba ganin wata mai kama da ita a wani gurin sai dai ba zai iya tunawa ba.

“Amman yarinyar nan kina da masifar kyau”

Ya fada yana shafa kansa kallonta yake sosai, ita kam bata ma san yana yi ba domin hankalinta yana gurin motocin dake gaban bus dinsu, sai da aka saki green light sannan yaja motarsa zuwa hanyar gidansa yana waigen School Bus din da ta ďauki wata hanyar dabam. Wayarsa ta yi ringing ya dago wayar ya duba.

“Hello”

“Ranka ya dade wata mata ce ta zo nemanka.... ”

Ta mamaki ya gama sauraren kiran sannan ya ce.

“Ka je ka fada mata ba zan dawo yanzu ba”

“Toh”

Mamaki ya cika shi, domin shi dai be yi da wani za a zo nemansa a gidan ba, gidan ma ba Nimra ba be taba kawo kowa a gidan ba, bw ya jin ko Daddy ya san yana zuwa gidan a yanzu balle kuma wani da be fadawa ba. Ya sake daukar wayarsa ya kira Nimra ya tambayeta ko akwai wanda take tsamanin zuwansa ko kuma ya biyo bayanta. Tana jin haka sai hankalinta ya tashi.

“Aa amman wa suka ce maka?”

“Ban tambaya ba, na ce ya fada mata ba zan dawo ba, zan tsaya daga nesa na ga ko wacece”

Nimra ta kashe wayar da sauri ta mike tsaye ta fita daga dakin da take kwance ta fito harabar gidan kamar mahaukaciya. Ta nufi gurin mai gadin tana masa tambayoyi.

“Dan Allah wacce ta zo ta fada maka wace ce ita?”

“Aa bata fada min ba”

“Dan Allah fita ka tambaya wacece ita kuma wa za a ce masa idan ya dawo”

Ba musu mai gadin ta fita ya leka waje har sai da ya hango inda Ummi ta aje motarta ya taka ya isa gurin yayi knocking din glass din motar ta bude masa idonta har ya kumbura tsabar kukan da take a motar, jiki ya mutu domin ta riga ta san mai afkuwa ta afku.

“Hajiya na kira shi yace ba yanzu zai dawo ba, amman wa za'a ce masa idan ya zo?”

“Zaka iya kiran min yarinyar da take cikin gidan nan?”

“Gaskiya ba zai yiyu ba”

“To dan Allah zaka iya ba ni aron wayarka? Saboda tawa wayar tana gida na manta”

Sai da ya dan dade yana tunani sannan ya ciro wayar ya mika mata, ta karba ta saka number Nimra, Nimra dake tsaye jikin gate tana jiran dawowar mai gadi wayarta ta fara ringing sai ta ki ta yi picking har kiran ya tsinke, sai da aka sake kira na biyu sannan ta daga.

“Hello”

“Nimra kina ina?”

Jin muryar Ummi ya haifar mata da sarawar kai, ta juya ta kalli gidan.

“Ina gurin Saloon Ummi”

“Saloon din kenan a cikin gidan wani? Yaushe kika lalata kanki Nimra? Me muka miki da zaki watsa mana kasa a ido? Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un ki fito yanzu nan ina jiranki a waje”

Kalaman da zata hada ta tari furucin Ummi sai ta rasa har Ummi ta yanke wayar, kuma ta kasa fita ta kasa komawa ta kasa yin komai sai gumi take tana hawaye kamin ya duka a gurin ta fara kuka...




©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 30

Ji ta yi kamar hanjinta za su fito a lokacin da wayarta ta sake yin ringing, wani irin rawa jikinta yake kamar mazari, sai dai ganin Number Ameer ya saka ta yi saurin dauka.

“Hello Ameer Ummi ce?”

“Wace Ummi? Na santa ne?”

“Mahaifiyarmu”

Ta sake fada cikin kuka.

“Oh Really wow i like it”

“What do you mean you like it?”

“Na kusa karaso bari na zo sai mu yi magana”

“No no no karka zo kar ta ganka tana waje tana jiran na fita”

Ya yanke wayar ba tare da ya sake ce mata komai ba, tana kokarin kiransa Mai gadin ya dawo min sai ta yi baya da sauri a zatonta Ummi ce ta shigo ciki.

“Ina take?”

“Ta wuce”

Ta juya baya tana dora hannunta a saman kai.

“Na shiga uku na lalace? Waya fada Ummi ina zuwa nan?”

“Toh Wallahi ban sani ba”

Ya amsa kamar da shi take magana, sai ta juyo ta daka matsa tsawa.

“Kai dan Allah ba da kai nake ba, ka rufe min shegen bakinka, ai duk laifinka ne”

Ya tabe baki ya koma gurin zamansa yana fadin

“Allah ya kara daman ina bakincikin abun da kuke aikatawa, zamani ya lalace yara sai fadarewa suke”

Da gudu ta shiga falon ta zauna saman kujera tana kiran wayar Ameer dake ta ringing ya ki ya daga.

“Ka daga Ameer ka daga”

Can kuma ta yanke kiran tunawa da ta yi da Ummi ta tafi, kusan tun da take a rayuwarta bata taba shiga tashin hankali irin wannan ba, bata saba yi na Ummi karya ba a lokacin da ta koyi yin karyar kuma ba ta yi zaton asirinta zai tonu ta wannan hanyar mafi muni ba. Shigowar Ameer ya saka ta mike tsaye da sauri ta nufi inda yake shi ma ya nufota.

“Ya aka yi haka ta faru?”

“Ban sani ba, wata kila wani ya fada ma mata ne, ko kuma ya kawo ta nan”

“Na so na tararda da ita da sai na yi mata bayani ko yanzu zamu tafi gidan tare zan fada mata komai”

“Wane irin bayani kuma? Ameer are you okay? Zan yi magana da ita tukuna”

Ya kama hannunta.

“Nimra ina fatar kin shiryawa wannan, daman soyayya dole akwai kalubale balle kuma irin ta mu da muka boye, amman ni I'm ever ready to marry you, ban san miyasa iyayenki suka tsane ni ba, but i trust you na san zaki iya shiga ko wane irin hali saboda ki ga soyayyarmu ta daure haka ne?”

Ta daga mishi kai.

“Good kamar yadda zan iya aikata komai akanki, and ina tunanin wannan dama ce a gareki da zaki bayyana musu wanda kike so, kuma ki fada musu cewar ba zaki auri kowa ba sai wanda zuciyarki take so, matukar suna kaunarki na tabbatar za su bar mu mu auri junanmu, kuma ki daina wannan kukan haka ba wani abun tashin hankali ba ne, zamani ya zo da an daina abubuwa da yawa, yanzu an waye ba kamar da ba ne zuwan dakin saurayi ba wani abun ba ne, kawai dai boyewar ne ina tunanin zai zama laifi a gurinsu, shi ma kuma laifinki ne domin tuntuni na yi ta neman ki ba ni damar bayyana kaina a matsayin masoyinki kika ki, i hope ba zasu ce za su raba ni da ke ba Nimra, saboda zan iya mutuwa idan iyayenki suka aikata haka, domin ni na dade da fadawa iyayena cewar ke nake so kuma sun goya min baya”

Ya rairaice mata yana ta saka mata maganganu a cikin kai kamar gaske, ita kam jikinta ya dauka kuma ta yarda har sonsa da tausayinsa sun karu a zuciyarta.

“Zan yi magana da Ummi zan fada mata gaskiya, kuma na san tana da fahimta zata fahimta amman Abiey...”

“Idan har uwa zata fahimta me zai hana uba ma fahimta matukar yana son farincikin yarsa? Ko dai ance na yi ma iyayenki wani abun da ban sani ba ne Nimra”

Ta girgiza kai.

“Aa bari na tafi”

Ta saki hannunsa ta nufi dakinsa ta dauko jakarta ta fito ta mayafinta ta saka talkaminta ta fito ta dauki wayarta dake kan kujerar falo ta sumbanci Ameer sannan ta fice. Binta yayi da kallo sai da ta fice sannan yayi murmushi.

“Now iyayenki za su ji zafin da mahaifina ya ji a lokacin da kuka yi sanadin da ya koreni, bari mu gani ke ma korarki za su yi, ko kuma za su ba ni dama na fito neman Aurenki ne? Not just them Maleek ma would feel the pain....”

Abun da ya faru a yau ba karamin faranta nasa rai yayi, ko ba komai ya samu dama ta biyu da zai kuntatawa iyayenta da ita Nimra da yake ganin an hada kai da ita an cutar da shi.



UMMI's POV.

Daker ta tuko motarta ta dawo gida, a harabar gidan ma ta dade zaune a motar sannan ta bude ta fito tana tafiya kamar marar lafiya ta shiga falonta. Hanne akwai ta samu a falo tana zaune tana kallon Plasma girkin data dora kuma yana Kitchen, Hanne ta mike tsaye da sauri tana yi ma Ummi sannu da zuwa hankalinta a tashe ganin hawaye a fuskar uwar ďakinta.

“Sannu da zuwa Hajiya, lafiya?”

Ummi bata iya amsa mata ba ta haura sama tana tafiya daker sai ka ce mai ciwon kafa, saman bed dinta ta fadi zaune. A yau kam sai ta ji tana kewar mahaifiyarta fiye da kullum, wasu kalamai da tarbiyar da mahaifiyar ta dage akansu take tunawa, ashe haka iyeyenta suka ji? Musamman ma mahaifiya domin ita ko da ta tashi bata san natan mahaifin ba, sai dai mahaifiyarta ta sha wahala akanta saboda ta yi rashin jin magana a lokacin da take da kurciya, kuma mahaifiyar na yawan fada mata cewar idan ta fita bata da kwanciyar hankali har sai ta dawo, ita kiriniya ce kawai take yi sai jan magana, wani abun ma ba ita take aikatawa ba faruwa yake yi saboda wautarta da shiririta, a wacan lokacin na su tashin akwai matukar kurciya da rashin wayo, kamar na yaran yanzu ba, da wasu suke fin iyayen ma wayo. Ita ba ďakin wani take zuwa ba, amman hankalin mahaifiyarta yana tashi ina ga ita data kama Nimra a gidan wani.

“Ashe haka kike ji Mama? Allah ya miki lullube kabarinki da rahma ya yafe miki”

Ta mike tsaye ta cire hijabinta ta nufi inda wayarta take ta dauka ta kira Abiey, ringing biyu ya yanke kiranta ya kira da kansa.

“Hiayatee....”

Sai ta yi shiru kamar ba zata amsa ba.

“Are you there?”

“Abiey... Wallahi a yau ina jin kewar mahaifiyata fiye ko yaushe, na san na girma amman ina jin kamar ace tana kusa da ni na raba jikinta na ji sanyi kuma na fada mata damuwata, duk girman mace tana bukatar uwa ko uba a kusa da ita, ko dan ta kallesu kawai ta ji sanyi a ranta, kuma ta kara kyautata musu”

“Hiayatee, yanzu aka kira ni daga makarantar su Waira wai ta yi fada da wata suna neman mahaifinta, amman zan kira Maleek ko Mahmood su tafi, gani nan zuwa gida yanzu nan”

Ya yanke wayar, kusan shi ne abokin shawararta a duk abun da ya shafe ta, idan bata fada masa damuwarta ba waye zata fadawa? Shi ne kadai mutumen da ya ke gane abun da take so tun kamin ta furta. Wayar dake hannunta ta fara ringing tana dubawa sai ta yi arba da number Yaya Maryam, yayarta the one and only sister she has, wacce suke uwa ďaya uba ďaya, yar'uwar da suka sha wahalarta a tare da Mama lokacin da kurciyata take cinta.

“Assalamu Alaikum”

“Wa'alaikissalam, Zahra Lafiya kike?”

“Ba kalau ba Yaya Maryam ina kewarku”

“Miya faru? Abiey ya kira ni yace na kira ki ko hankalinki zai kwanta kin kira kina masa maganar Mama, hankalinshi duk ya tashi”

“Yaya Maryam, yau na ďanďana wani ďaci da uwa take ji idan Yayanta suka mata karya, ina cikin wani irin bakin ciki na uwar da ta bawa yayanta tarbiya aka rusa, sai dai kuma a yanzu yanke shawara nake”

“Fada min abun da ya faru?”

Ummi na cikin labarta mata abun da ya faru ta ji an yi knocked a kofar dakinta Nimra na kiran sunanta..

“Ina zuwa”

Ta yanke wayar tana kallon Nimra data turo kofar ďakin ta shigo idonta a kasa domin tana jin kunyar hada ido da Ummi, ba dan fuskarta dake nuna alamar kuka ta yi ba, da ta rantsewa Ummi akan karya cewa gurin Saloon ta tafi albashi daga baya sai ta bayyanar mata da Ameer a matsayin wanda take so.

“Da ace kina da kunya kamar yadda nake gani a idonki, da Ubangijinki ya kamata ki fara kunya, kamin ki aikata abun da kika aikata, da kin ji kunyar yin karya da kuma shiga gidan wanda ba mijinki ba ki taba jikinsa ki sumbance shi ki cire tufafinki a gabansa ki bar shi ya aikata abun da yake so da ke”

A lokacin ďaya ta saki jakar hannunta da mayafinta da wayarta ta fadi kasa ta kama kafar Ummi.

“Aa Ummi na yarda na ina zuwa gidan, ina rika hannunsa ko taba jikinsa ko sumbantarsa amman Wallahi na rantse miki da sarkin da babu abun bautawa da gaskiya sai shi ban taba aikata zina ba, ban taba yarda wani namijin ya san yi a matsayin ƴa mace ba, Wallahi ban aikata ba Ummi”

A tsakanin yarda da yar'uwarta Ummi ta samu kanta, ba zata yi saurin yarda da maganar data fada mata a yanzu cewar bata aikata zina ba, domin a baya ta yarda da ita kuma ta same da wannan halin, kuma ba zata karyatata kai tsaye ba, domin ta yi mata rantsuwa da Allah.

“For how long kike tare da shi? Waye shi? Miya fada miki ya yaudare ki kika watsar da tarbiyarki? Miyasa ba zaki fito ki fada mana kina son aure ba? Akwai abun da muka rage ki da shi da kika tafi gurin wani ya baki?”

Ta girgiza kai tana kuka sosai.

“Ba ku rage ni da komai ba Ummi, idan na fadi haka na yi karya kuma na ci amanarku”

“A yanzu ma kin ci amanarmu Nimra miye rage? Kin yi komai kin daka kin tankade kin shanye”

“Ummi ki dubi girman Allah ki yafe min”

“Ki fada min wanene?”

Ummi ta daka mata tsawa sai ta jikinta ya dauki rawa domin bata taba mata fada haka ba.

“Idan baki fada min ba, shi Abiey idan ya zo sai ki fada masa”

Nimra ta matsa baya da sauri tana girgiza kai.

“Aa Ummi ba zaki fadawa Abiey wannan maganar ba, ba zaki fada masa abun da na aikata kai tsaye ba, wannan a tsakaninmu ne, ba zaki fadawa Abiey haka ba dan Allah Ummi”

“Toh wanda ya koya miki karya ya yaudara yace ki zo ki koya min ko?”

“Ummi dan Allah ki rufa min asiri, karki fadawa Abiey wannan maganar”

“Idan kika ga ban fada masa ba, to na mutu kamin ya iso ne”

Tana jin hakan ta tashi da sauri ta dauki wayarta ta jakarta ta fice daga dakin. Dakinta ta shige ta maida kofa ta rufe ta saka key. Cikin hanzari irin na magidanci mai damuwa da iyali Abiey ya shigo gidan, kamin na isa ďakin da matarsa take har ya matsu. Ko sallama be yi ba ya tura kofar ďakin ya shiga.

“Madam Lafiya”

Ya tambaya yana zaunawa a kusa da ita cike da kulawa. A yanzu ba hawaye take ba bacin rai ne a tare da iya daya maye kukan da take a na bakinciki a dazun.

“Ba lafiya ba Abiey, wani nauyin ne ya fado wanda ba zan iya dauka ni kadai ba”

“Fito fili ki fada min abun da yake faruwa”

“Shawara ce na yanke, daga Nimra har Namra za su fito da miji cikin satin nan kuma aurensu ba zai wuce kasa da wata ďaya ba”

Yanzu ma kallonta yake, sai dai kallon mamaki ne yake mata wannan karon.

“Hiayatee ba zaki yanke wannan hukuncin mai zafi a cikin kankanen lokaci haka nan kawai ba, dole akwai abun da kika gani fada min meya ke faruwa ne?”

“Jiya.. Dare bayan na fito daga bangarenka na leka ďakin kowa har na kai ga na Nimra, sai na samu wayarta a kasa bachi ya sace ta, na duka na dauki wayar sai na yi arba da wani sabo daya daga min hankali, number bata da suna sai heart emoji, ya turo mata sako cewar ta san irin karyar da zata sake yi su hadu, yayi missing dinta, and he can't wait for her hug and kiss...”

Wani dim dim dim gaban Abiey yayi ba, ya kara tattara hankalinsa ya maida gurin Ummi.

“Ban mata magana ba, sai na kyaleta daman ta fada min cewar jiya ta tararda taro da yawa a gurin saloon din da taje bata samu ba, dan haka yau tana son ta koma, na bata dama saboda na gane da gaske can zata tafi ko wani gurin, bayan ta fita na bibiyi motarta ina cikin tawa motar har ta isa wani gida aka bude mata gate ta shiga...”

Ummi ta bashi labarin komai har zuwa yanzu da ya shigo cikin gidan. Abiey ya mike tsaye ya cire babbar rigarsa ya aje har sai da Ummi ta ji tsoro ta tashi ta bi bayansa da sauri. Dakin Nimra ya nufa yana tabawa ya ji kofar a rufe sai ya banki kofar dakin da wani irin karfin zuciya da jiki.

“Nimra ki bude dakin nan, idan ba haka ba zan saka a balle kofar nan kuma idan aka balleta sai na rabaki biyu sai dai a buga ni a Jarida ki bude dakin nan na ce”

“Abiey calm down bari na yi magana da ita”

Ya dakawa Ummi tsawa.

“Ya zaki ce na kwantar da hankalina? Kamar baki san girman abun da ta aikata ba? Dole na yi magana da ita”

“Zata bude amman ka matsa jiki kofar zan mata magana zata bude”

Ya matsa gefe yana sauke numfashi da karfi, rabon da ya samu kansa a bacin rai irin haka tun a lokacin da Deen yake raye. Ummi ta matsa kusa da kofar ta ce.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login