Showing 276001 words to 279000 words out of 281271 words
ta san komai yanzu”
“Amman ta fahimtar da ni ai, kuma ta yi min karin haske akan period kuma she teach me yadda zan kula da gida na zama full house wife”
“Tana jna yanzu?”
“Bachi take fa, yanzu karfe sha biyu na dare ne”
“Oh Really okay ke ma ki tafi ki kwanta bana son ki gaji”
“I will amman yaushe zaka dawo i miss you kuma idan Humairah ta tafi ni kadai ce na gidan, wannan big house ba zan iya zama”
“Idan na dawo zaki yarda mu zauna lafiya komai na ce ki yi babu musu?”
Ta daga masa kai.
“Zan duba na gani, give me a kiss sai ki je ki kwanta”
Ya mika bakinta kamar yadda suka saba ta sumbanci wayar, shi ma ya kai bakinsa ya sumbanci screen din wayar sannan ya furta mata i love you cikin rada.
“I love you too good night”
“Sleep tight my princess my happiness”
Ya masa murmushi tare da daga masa hannu sannan ta kashe wayar. Sai da ta shiga Kitchen ta sha ruwa sannan ta nufi dayan dakin da suke kwana ita da Humairah domin Humairah ta fada mata dakin mai gida ba a shigar da kowa kuma ba a barin kowa ya kwanta daga ita sai shi, wannan ya saka suke using dayan dakin domin duka three bedrooms din sai da Abiey ya suka mata su da kaya. Ganin Ummi na ta kara samun sauki ya saka Abiey ya umarce Ameer da Maleek da su koma gida, idan ma suna son dawowa kamin Ummi ta bar asibitin sai su dawo tare da matansu. A tare suka yi booking flight kuma a tare suka iso Lagos sannan suka kama hanyar Abuja. Ranar da za su dawo Humairah da wuri ta bar gidan ta koma gidan mijinta domin gyara na su muhallin da kuma girka masa abun da zai ci, sai dai duk abun da ake Nuwaira bata san tare da Ameer Maleek zai dawo ba, ita kam tana zaune a nata gida bayan ta gyara iya inda zata iya ta dafa shimkafa da ganye ta ci, ta dawo falo ta zaune rike da kofinta na lemu, ta dauki remote ta canja channel can kuma ta ji kallon ya isheta sai ta kwanta saman kujera ta turo baki gaba, babu wanda take hangowa sai Humairah Ameer ya dawo ba zata kwana ita kadai a gida ba, amman ita zata kwana ita kadai a wannan babban gidan da bata gama sake jiki da shi. Tashi ta yi zaune ta nufi dakinta ta zauna saman gadonta ta dauki wayarta tana shirin kiran Maleek sai gashi ya kirata sai da yi picking da sauri tana share hawayenta.
“Toh kuma yanzu kukan me ye?”
“Ni ba zan iya kwana a gidan ni kadai ba?”
“Saboda me?”
“Tsoro nake ji”
Ya daga wayar hannunsa yana juyawa harabar gidan ta inda kofar falon take.
“Wannan gidan kike tsoro”
Bata san lokacin da ta zaro ido ba ta mike tsaye da sauri ta fito dakin da gudu, kamar walkiya haka ta fice daga falon ganinsa ta yi tsaye harabar gidan yana sanye da kananan kaya sai jacket din dake sama, ta kalli video wayar ta kalleshi a zahiri murmushi kawai yake mata, a take ta saki wayar ta sauka entrance din da gudu, tana isa inda yake ta daka wani irin tsalle ya saka hannu biyu ya cabeta ya rumgume yana dariya.
“Surprise.....”
Dagowa ta yi tana ta kissing dinsa ta ko'ina saman kai gefen fuska cikin kunne saman ido kan baki, jikinta sai rawa yake na murnar ganinta, haka ya rikota daukota suka shigo falon yana rufe kofar ya sauketa ya rike fuskarta sai ta rufe ido tana sauke numfashi, ita dai har cikin ranta ta san tana son Maleek irin son da bata san yadda zata kwatanta ba, yadda take numfashi da karfi ma ya isa ya sanar masa da haka.
“I miss you alot, ina kaunarki Nuwaira kauna ta gaskiya kuma mai tsanani ji nake kamar na bude zuciyata na sakaki ciki na rufe”
Ya kwantar da kanta a kirjinsa sai ya rumgume ta, ya jefar da wayarsa kan kujera. Kusan a tare suke dauka da aje nunfashi zuciyar ko wannensu na cike da farinciki. Dagota yayi a hankali ya kai bakinsa saitin bakinta ya lashi lips dinta sannan ya hade bakinsa yana kissing dinta the same time ita da shi suna tsutsar sweet dn da ya shigo da shi a bakinsa. Sai da tsayuwa ta fara gagararta sannan sai ya saka hannunsa ga tallafota ta yi sama ta dalle gaba daya a jikinsa. Yana ganin hakan ya juyar da ita ya kwantar jikin kujera sai da ta ji yana kokarin wuce tunaninta sannan ta daga saman jikinsa ta sauka da sauri.
“Baka ce min zaka dawo ba, ni ma da sai na maka girki, Humairah ta fada min girki zata yi ita ma”
Fisgota yayi ta fado jikinsa ya rumgumeta.
“Ganinki ya fiye min girki i love you”
Sai da ta yi da gaske sannan ta samu ya sake ta, ruwa da lemu ta fara kawo masa kamar yadda Hunairah ta fada mata, da zai shiga dakinsa kuma ta bi bayansa ta san babu abun da zai bukata a bandaki amman haka dai ta shiga ta duba ta tabbatar babu abun da babu sannan ta juyo sai ta jin ta yi an rike mata hannu.
“Ba zan yi wanka nan ni kadai ba”
Ta zare ido bata gama rufe baki ba ya kara tura a bathroom din ya rufe, ya saka dayan hannunsa ya cire tawul din dake jikinsa, duk yadda ta so ta kwaci kanta sai abun ya faskara, a tare suka yi wanka sai ta kasa kallonsa shi kam sai dariya yake kamar ba shi ba, bathrobe ya saka mata ya rufe mata duka jikinta ta saka karanin tawul ya daure mata kanta sannan ya daura wani ya hanyo hannunta suka fito domin ta zama kamar hoto. To his surprised gurin rubbing jikinsu ta yarda ta shafa masa har a baya, amman ita bata yarda ya shafa mata ba.
“Ni me yasa kika min”
“Kai ka ce na maka ai, ni kuma ban bukata ba”
Ta masa gwalo tana tunanin ta fishi wayo, ta cikin madubin yayi mata murmushi tana ganin haka ta mike tsaye da sauri sai ya riketa ya dorata saman gado ya fara kokawar rabata da bathrobe din dake jikinta yana mata chakulkuli sai kyalkyalar dariya take kamin ta samu sa'ar kubucewa ta haye can karshen gadon ta fara daukar pillows din da aka tula saman gadon aka yi ado da su tana jefa masa, shi ma pillow ya dauka suka fara trowing junansu da su sai dariya take har sai da ya gaji ya fadi kwance kasa, saukowa ta yi kasa tana lekonsa ya buge mata kafa ta fado kansa ta tare da hanneyensa sai ta saka dariya yana hakki ta kwantar da kanta a kirjinsa shi ma hakkin yake yana dariya kamar wadanda suka yi yaki, hannayensa ya saka ya rufeta ruf.
“I love you Nalik”
“i love you too”
Ya dagota.
“Rufe idonki”
Ta rufe daman bata taba jin zata iya mutsa masa ba indai bangaren bada umarni ne. Sai ya saka hannunsa ya warwar rigar daga gabanta ya bude kirjinta tana ganin haka ta yi saurin kwantawa manna kirjinta da kasa dariya, sai ya lumshe ido daman abun da yake nema kenan ya kara matseta a kirjinsa. Da wayo da wayo Maleek yayi ta jan matarsa a jiki kasancewarsa mai son wasa da kiriniya sai ta biye masa, wani abun ma ita take kirkirowa saboda hankalinsa ya kawo su yi ta mugun wasa a gida kamar wasu kananan yara, and Nuwaira got lucky mijinta mai son irin rayuwarta ne if not zata sha wahala zaman aure, mutum ne mai gujewa bacin ranta da son farincikinsa. Shiyasa idan ya dade a waje take jin babu dadi, shi ma idan bata kusa da shi ba shi da walwala sai ya dawo gida. Ranar da Maleek yayi nasara Nuwaira ta yi masa maraba da zuwa a duniyar da be taba ziyara ba, be raga mata ba sai da ya samu abun da yake so, domin ya dade yana lallabata yana bibiyarta, sai da ta raina kanta a ranar babu kalar kukan da bata yi masa ba, tun tana magana da hausa ta hada masa da turanci har ta koma yin yaren su Garuk, amman Maleek be fahimci komai ba sai bayan ya samu natsuwa, a nan ya gane yayi yar karen barna, gashi gimbiyar tasa ko a banza kuka take balle da dalili haka ta rikirkita shi duk ya bi ya rufe ko motsi ta yi sai ya tashi. Kamin ya samu ta saba abun ya zame mata jiki sai da ya sha wahala sosai.
*** *** ***
Rayuwar farinciki da kwanciyar hankali ce ta cigaba da guduna tsakanin iyalai biyu da suke karkashin inuwa daya, wato Ameer da Maleek. Ta ko wane bangare ba su da farabar komai a yanzu, domin Ummi sai kara samu sauki take fiye da yadda suke barta ma, farincikin hakan a gurin Abiey har baya misaltuwa ada kam yana ta tunanin yadda rayuwa zata tafi masa idan babu Ummi a raye, gaba daya ya gama katsewa kuma yayi giving up akan abubuwan da dama sai dai saukin da take ta samu a yanzu ya fara dawo masa da farincikinsa. Kana iya jin hakan ko da waya ka yi da shi balle kuma ace kana kallonsa, wasa wasa Ummi ta kwashe 6 months a asibitin, har ta kai ita ma kanta sai da ta gamsu da ta samu lafiya a yanzu, domin yanayin da take ji yanzu ba kamar na da ba ne, duk kuwa da ta san da cewar yana nan tare da ita amman hakan ya kara mata imanin babu mai kashewa ya raya sai Lillahi. All those months da ta yi a asibitin sau biyu kawai Nuwaira ta je dubata shi ma saboda ta matsa ne, Maleek yayi mata international passport yayi da visa suka tafi tare kwana biyu suka yi suka dawo tare ya sake komawa bayan ya dawo kuma ya sake tafiya da ita ta duba Ummi ta sake dawowa. A week later da dawowarsu aka sallamo Ummi ta dawo gida, ranar farincikin a gurin zuri'ar ba a magana Abiey kamar ya zuba ruwa kasa ya sha. Tun a ranar Mr Bashir ya dauko matarsa suka zo har cikin gidan suka duba Ummi, domin tun da yaje dubata sau daya lokacin da take cikin ibadar jinya ba be samu komawa ba. Namra da mijinta tun ana saura two days ta dawo suka tare a Abuja, after zuwanta Namra ta dawo gidan Shuraim ma zuwa yake gaisheta ranar da yayi marmarin matarsa sai ya dauketa su fita yawon shakatawa.
Nuwaira a zama kamar ita kadai ce yar Ummi kusan kullum sai Maleek ya kawota ta duba Ummi bata tafiya gida sai dare, kusan duk wani abun da Ummi take bukata ita take kokarin yi mata domin a ganinta ta wannan hanyar ce kawai zata iya biyan Ummi ta saka mata da abubuwan da ta yi mata a baya.
[8/23, 4:03 PM] 🦋-🦋: 87
** *** **
“A hankali”
Cewar Ameer yana mikawa matarsa hannu ta rikoshi tana tafiya a hankali. Cikin dake jikinta kawai Nuwaira take kallo har suka shige cikin falon, cikin yanayi damuwa ta juyo ta kalli Maleek.
“Ina so Ya Maleek”
Ya kai hannunsa ya rika fuskarta.
“Zamu samu na mu soon”
“Kullum haka kake cewa, kuma har yanzu”
“Allah ne yake bada haihuwa Princess kuma duka duka yaushe muka yi auren ma? Be kai ace kin daga hankali har haka ba”
Saurin dauke hannun yayi jin motsin bude kofar falon da za ayi, ya dan matsa baya. Hajiya Jamila ce ta fito da lullubinta hannunta rike da makullin mota.
“Zan shiga gari na nemowa sukata kayan kwala, kamin mu kai ga naki idan kuma na ji shiru na kara masa aure kin ga dai yadda gidana yake cike da yan mata”
Da zolaya ta yi maganar tana dariya, Maleek yayi mata Allah ya tsare Nuwaira kuma ta yi murmushi sai da ta fice daga gidan sannan Nuwaira ta kalli Maleek maraininta ta fara masa kukan shagwaba.
“Ka ji ko? Kuma zata iya baka wata fa tana da yan mata manya”
“Duk babu nata a cikin rikonsu take, kuma ni daga ake ai bana fatan kari”
“Ummi dai tace ka rike ni amana ai”
“Oh Ummi ta hada ni da aiki ko kallonki na yi kika ji baki gamsu ba sai kin tuna min da wasiyar Ummi, da ta rasu da na shiga uku da rigimarki, toh Allah yasa tana da rai dole a daga min kafa, kuma rike manar Ummi baya nufin a hana ni kara aure”
“Auren zaka kara kenan?”
Yayi dariya ya rumgume ta ta baya.
“You make me hate wannan Hajiya Jamila more, daman Ummi ta fada min duk abun da ta yi mata a can baya ai, ni bana son wanda be son Ummi kuma gashi tana cewa zaka kara aure”
“Wacan ai duk ya wuce yanzu, ba ki har ganin Ummi take Abuja ba?”
“Ni ban gani ba”
“Baki nan lokacin amman taje kuma ba gashi mu munzo ba? Ke tsaya ma wai me kika sani a auren mace biyu?”
“Na sani ba, ka dauka ni jahila ce? Islamiyar da muke zuwa ai ina ganin masu miji daya su biyu, kuma Malam yana mana bayani ai, ni bana son na ga wata macen ta so ka, shiyasa nake son gobe ta yi mu tafi gida ma”
Gefen fuskarta ya sumbanta.
“Ni bana da wannan ra'ayin ma, baki ga Abiey ba tun bayan rasuwar Mahaifiyarsu Yasmeen be sake aure ba, ni ma bana son yawan aure mata daya ta wadace ni da yarana biyar ko hudu kamar dai Ummi”
Ta juyo ya kalleshi.
“Ni ina so da yawa kamar goma”
“Zaki iya haifar yara goma”
Dirty words ya watsa mata a kunne sai ta daga kai, alamar ta yarda.
“Laa ashe yarinyar nan ta lalace yanzu bata da kunya”
Ta yi saurin rufe fuskarta tana dariya sai ya rungume ta a kirjinsa daman duk tsayin nata iyakarta kafadarsa. Kamin goben ta yi Nuwaira duk ta matsu daman can bata son zuwa ba ita dai ta tsani Hajiya Jamila tun a lokacin da suke daf da zuwa Ummi ta fada mata abubuwan da Hajiya Jamila ta yi mata, sai ta ji duk ta tsaneta daman kuma ita bata iya tsanar mutum ba, gashi kuma ta yi mata zancen yan matan da suke gidan ita kuma ta maida abun gaske. Misalin sha daya na safe jirginsu ya tashi daga Katsina zuwa Abuja, a duk zaman jirgin Ameer yana kusa da matarsa hannunsa cikin nata, ba motsinta ba har numfashinta lura yake da yadda yake fita da shiga balle kuma idan ta yi zaman da be gamsu ba sai ta ji kamar zai yi effecting babynsa dake cikinsa ne.
Two days da dawowar wani sabon laulayi ya kama rufe Humairah daman tun da ta samu cikin kusan kullum cikin laulayi take idan ta yi wata daya lafiya wata biyu ko uku da zai zo sai ta ci kwakwar wahala. Around 2am mai ya tasheta sai ta sauka saman gadon a hankali ta nufi toilet a kasa ta zauna ta tara bakinta a ta yi da kwara aman. Tana cikin yi ta ji Ameer a bayanta yana shafa bayanta da hannunsa sai sannu yake fada mata cikin yanayin damuwa, kusan abun da ta ci da rana sai da ta amaye tass sannan ta samu sukuni, yana wanke mata tana hawaye domin tana wahala sosai da cikin nan. Da kansa ya cire rigar bachin dake jikinta ya cire tasa ya kunna shower ya tara jikinta sai ya tsaya daga bayanta ya saka hannayensa a gaba a karkashin cikinta ya daga mata cikin yayi sama sai ya lumshe ido tana jin kamar babu cikin ma gaba daya a jikinta nauyin cikin ya cire lamo ta yi a jikinsa ruwan dake sauka a saman kansa suna saukowa a kanta, kuzarin da ta rasa sai ta ji ya dawo har bachi ya fara daukarta a haka.
“My guideline”
Ta bude idon a hankali.
“Bachi zaki ki yi?”
Ta daga masa kai tana kara kwantawa a kirjinsa. Ya kashe shower ya dauko tawul ya daura mata ya daura ya riko hannunta suka fito saman gado ya kwantar da ita sai ta bata masa fuska domin ta san ba lallai ne ta iya bachin ma.
“Shiiiiiiiiii zaki yi bachi yanzu nan?”
“How?”
“Ina zuwa”
Wani lotion ya dauko ya matsa a hannunsa ya fara shafa mata a kafarta tana mata massage a hankali, a duk time din da yayi rubbing kafarta sai ya sumbance feet dinta har ya gama ya bude drawer ya dauko karamin cup din honey ya aje kusa sannan ya hau saman gadon ya ya fara bin jikinta yana shafa mata cikin siga mai dadi da kwantar da hankali.
“Kina bukatar cin wani abu? Kin ga ki amayar da komai”
“Aa bana so”
“Please ko kadan ne”
Kamar zata fashe masa da kuka ta ce.
“Ka daina min magiya bana so mana”
“Na daina, I'm sorry”
Ya sumbanci goshinta, sannan ya dagata ya jingina da gadon ita kuma ya kwanta jikinsa zumar ya dauka ya bude yana saka yatsansa ya lakato ya kai mata a baki.
“Bana so na ce bana son komai ba”
Da sauri ya janye hannunsa, domin ko kadan baya son bacin ranta a yanzu, ba dan tana da cikinsa sai dan hallayarta da dabi'un gashi ya sameta cikakkiyar mace, ba kamr yadda yake tunanin duk budurwa ta ta wuce 20 ba za a samu samu budurci a tare da ita ba, amman abun ya canja tunaninsa kuma ya tabbatar masa har gobe akwai na kwarai, and Humairah mace ce mai yawan dora shi a hanyar kwarai, tana nuna masa kulawa yadda yake son samu a mace, a yanzu kam ya yarda idan Allah ya hana ka wani abun zai baka wanda ya fishi ko ba komai Humairah cikakkiyar mace ce mai wayo da kaifin basira. Samun cikin da ta yi kuma sai ji a duniyar babu abun da ya fi