Showing 243001 words to 246000 words out of 281271 words

Chapter 82 - Wani Gari Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1260

macizai ne daga inda Sarki zai dora kafarsa kuma kunamu ne da ka tsafe aka hade su guri daya aka busar da su aka yi ma Sarkin gurin dora kafa. Babu annuri babu far'a babu sakewa da walwala a fuskar Sarkin da ya kwana biyu har tsufa ya fara cin karfinsa, sandar sarauta ce a hannunsa wasu zaratan jarumai suna tsaye dama da hagu suna masa fita, kujeru da aka jesa a fadar suna cike da masu rike da Sarautu a garin, daya bayan daya Nuwaira ta bisu da kallo har idonta ya sauka a kujerar da ake aje mata ta tsafi abun da ta yi arba da shi ya bata mamaki matuka Eid ne zaune a kujerar shi ma fuskarsa a hade take babu alamar ya taba dariya babu imani da tausayi a idonsa Maleek kawai yake yi ma mugun kallo na fitina. Sai da suka iso tsakiyar fadar sannan suka tsaya mutanen da suka yi musu rakiya kuma suka matsa daga gefe aka bar Maleek da Nuwaira tsaye suna fuskantar Sarki.

Cikin halshensu Sarkin ya fara magana da Nuwaira.

“Kin karya dokar da muka saka miki, kika gudu kika bar garin Garuk, bayan kuma kin san hukuncin da muka shai'anta miki idan har kafarki ta bar garin Garuk me yasa kika gudu”

“Saboda na tsorata a wacan lokacin, kuma ban shirya karbar hukunci akan laifin da ban aikata ba, ba ni na kashe mutumen da kuka zargina da kashewa ba, haka kuma ban shirya karbar Sarautar da kuke cilasta dole sai kun ba ni ba”

“Kin gudu kin tafi a gurin mutanen da suka fi mu tsafi da iya sarrafa aljanu saboda su baki kariya daga garemu, kin watsar da al'adarki da addininki kika dauki ta su. hakan be wadatar da ke ba har sai da kika gayyato daya daga cikinsu zuwa cikin garinmu, ya karya mana dokoki ya ci mutumci yayi fada da jininmu akan wani dalili”

“Ku kuka kira ni, Eid kuka aika har cikin gidan da nake rayuwa tare da mutanen da na dauka a matsayin dangina, gashi nan be fada muku ba?”

“Mun tura shi ne kawai saboda shi kadai ne yake iya sarrafa kansa ya shiga cikin gidan da kike, babu kalar tsafin da ba mu aika miki ba, amman ya kasa samunki saboda kina cikin gidan da tsafinsu ya dara na mu, daga lokacin da kika gudu na kira taro na sanar da duk wanda ya kamata ya sani ya dauke mu kwana hudu kamin mun hanke shawarar abun da zamu yi, daga karshe muka cin ma matsaya akan kasheki, amman Eid ya tsaya kai da fata wajen ganin kin rayu, babu kalar azabar da ba mu yi masa ba a lokacin da yake ziyartarki a haka ya jure, muna daf da yafe ki ya bukaci a dawo da ke ko da ba za a baki Sarautar ba, sanadin guduwar da kika yi ya saka mun sauya sarautar tsafinmu ta shekara da shekaru, a dole muka yi mata garanbawul daga karshe aka cin ma matsayar baiwa Eid Sarautar, hakan ya kara masa kima da daraja a idonmu, shiyasa har ya roki mu dawo dake a cikin garinmu kuma muka saurareshi”

Cikin tsananin mamaki Nuwaira ta kalli Eid da har lokacin Maleek yake harara, sannan ta kalli Maleek da be san abun da take fada ba balle kuma abun da Sarkin yake tanbayarsa.

“Me kuke tattaunawa?”

“Wani abu mai ban mamaki Ya Maleek”

“Ku tambaye shi, me yake bukata daga garemu? Idan rakiya yayi toh zai iya komawa mun gode da zuwansa, amman ba zamu zauna da butulu irinki ba, idan muka yi kora ba ma bukatar dawowarta a cikin danginmu, a da mun yanke shawarar kasheki, sai dai Eid ya bauta miki ya jure duk wata kalar azabar mu saboda mu barki ki rayu, ta karkashin kasa mun yi ta aika miki da mutuwa har a daren jiya, abun mamaki kin aje al'adarmu da addininmu saboda kin ga na wadanda suka fi mu karfi. Tabbas yaro baka shigo garin mu ba sai da ka shirya, domin wani be taba gwada karya mana dokoki haka ya kwashe lafiya ba, ba mu tana tsarrafa tsafi irin wanda muka yi a daren jiya ba, amman komai ya kasa samunka a kusa da dakin ma aljannunmu ba su kusanta ba, a tare da kai mun ga aljanna mai irin tsafinka mun saka wadanda suka fita karfi da iko sub rabata da kai a tunaninmu ita take baka kariya, da muka sake aika tsafi sai ya dawo mana, tun farkon shigowar muke ta jefarka amman jifar ta kasa isa a inda kake, madubin tsafinmu ya kasa ganin fuskarka, jama'ar da ake turawa su kiraka kana saka musu fargaba da tsoro, a yanzu ba ma jayya da kai mu dai ba ma shiga gonar kowa kuma ba ma son a shiga gonar mu, Eid ya fada min tun jiya ka dage sai ka ga Sarki zaka tafi, fadi bukatarka Sarki zai sallame ka ka yi tafiyarka”

Sarkin ne da kansa yake fada Eid na fassara masa dan dolensa, mamaki da jindadi da kauna ya hana Nuwaira cewa komai sai kallon Maleek dake cike da burgewa.

“Alhamdulillah, hakika duk wanda ya dogara ga Allah shi kadai Allah ya isar masa, ni bana tsafi van tana tsafi ba, kuma ban taba sanin yadda ake yinsa ba kuma bana fatar yinsa, ni dai na san ina bautar Allah ba tare da shirka ba, sannan ina karanta ayoyi da addu'o'in kariya, a jiya ma na kwana ina karanta suratul Bakara, kuma duk wanda yake karanta iya da ayatul kursiyu Allah ya turo mala'ikunsa su yi gadin Mutum ne, a inda mala'ika yake kuma aljani be isa ya raba gurin ba, muka karanta ta a gidanmu shiyasa kuka aika tsafinku be isa a garemu, domin idan aka karanta sau daya a wata tana tsare gida ta hana duk wani abu mai cutarwa rabar gidan har wani wata, saboda wannan ni ba tsafi nake ba da za ku surfafa bincike da za ku fahimci wannan addini ne ba tsafi ba, kuma ina fatar wata rana za su aje na mu addinin da al'adar ku karbi cigaban da duniya ta zo da shi haka ma ku rumgumi musulunci ku watsar da tsafinku”

Cikin alfaharin da jindadi Maleek yake fada ana fassarawa Sarkin da yarensa, har sai da ya kai karshe sannan Eid ya ce.

“Ba mu bukaci ka tallata mana addininka ko al'adarka ba, ka bar mu da na mu, kai ma ka rike naka, Sarki yana tambayar dalilin ganinsa da kake son yi, kuma ina ganin ka samu abun da kake bukata zaka iya tafiya”

“Aa ban fadi bukatata ba tukuna, dan haka ba zan bar garin ba sai na isar da abun da ya kawo ni”

Eid yaja numfashi da karfi da bakinciki sannan ya fadawa Sarki abun da Maleek ya fada.

“Tuk rid jaur bhakar suuf hutk garfha ifftuk galink galink ket”

Eid ya juya ya fassarawa Maleek.

“Ya fadi bukatarsa ba ma son zamansa a cikin garinmu”

“Ina neman auren yarku Nuwaira ne, saboda a yanzu irin addini take yi, ta saba da irin al'adata da kuma dangina, ina tunanin bata da bukatar zama a cikin garin nan, domin ba zata canja addini ba ba zata sake komawa addininku ba, kuma ba zata karfi kujerar tsafin da kuke son bata ba, idan har kuka yarda kuka ba ni aurenta zan dauke ta mu bar garin nan da ita yau din nan ba sai gobe ba, kuma ba za su sake ganinmu ba, ina tunani bata da amfani a gareku a yanzu saboda ta karya dokokinku kuma kun yafe ta kamar yadda ka fada”

Eid ya mike tsaye ya bar kujerar da yake zaune ya nufo inda Maleek yake cikin zafin nama, kamin ya karasa Sarkin ya daka masa tsawa.

“Karka kuskura kai kanka ga halaka, kana ganin wannan matashin ka san sai da ya shirya sannan ya shigo garin nan, neman yake a taba shi ya janyo mana fitina, fassara min me yake da bukata”

Sai da Eid yayi da gaske ya yaki zuciyarsa sannan ya iya fadawa Sarki abun da Maleek yake da bukata, daga baya ya jadadda masa da cewar ba za su aminta da haka ba, domin wannan ya zama cin fuska, kuma saboda ta karya dokokinsu har sun yi fushi da ita sun yafe ta ba shi yake nufin a barta ta aure wani bare ba. Sarki ya daga masa hannu.

“Yanke hukunci ba a hannunka yake ba Eid karka zafafa, kuma kar bacin rai ko soyayya ta saka ka manta da ka'idodi da dokikin garin nan, idan muka yafe mutum muna nufin cire hannayenmu daga duk wani lamari nasa, ko da kuwa zai mutu ne, kuma ba zamu tarbe shi ba ko da zai bukaci dawowa a garemu, ba kuma zai aura daga garemu ba.
Kaka ya taba fada min cewar kamin a haife ni, wasu mutane biyu sun taba karya mana doka, ya saka aka koresu daga garin nan, har yanzu babu ruwanmu da iyalansu, ta farko daga cikin gari take, lokacin da dadin tsafi yayi mata yawa sai ta zurfafa ta dauki maita, mu kuma ba mu yarda da maita ba, duk wani tsafi bayan wanda muka gada gurin iyayenmu ba mu yarda da shi ba, sanadin hakan muka kora Iya ta bi duniya, har yau babu ruwanmu da zuri'arta, bayan ita kuma Wasim ɗa daga masarautar nan, soyayya ta dibeshi kamar yadda take son dibarka a yanzu, ya karya mana dokoki ya shigo mana da bare, kuma ya fitar da ita ba tare da izinin kakanmu ba, daga karshe ya zabi addininsu da al'adarsa ya watsar da ta mu, hakan ya saka shi ma muka yafe shi, shi ma babu ruwanmu da shi da zuri'arsa, dan haka karka yi kuskure biyewa son zuciya ta kai ka ta baro”

“Duk wata azabtarwa da wahala da na jurewa sha a gurinku, tsawon lokacin da Waira ta dauka bata kusa, na jure ne saboda ina sonta ban taba fadawa kowa wannan maganar ba amman zan fade ta a cikin fadar nan, na san kowa ya lura da hakan, na raine ta tun tana karama har ta fara wayo, rana daya kuma sai wani ya dauke min ita?”

Wani daga cikin manyan masarauta da suke gurin ya mike tsaye ya isa gurin da Eid yake tsaye ya dafa shi.

“Kwantar da hankalinka Jarumi na, akwai mata da yawa a cikin garinmu da suke sonka, akwai matan da suka fi Waira kyau da komai ciki da wajen masarautar nan, ka rufe idonka daga ganin Waira ka bude idonka a garesu cikin kankanen lokaci za a gama da su, karka yarda zuciya ta deba ka gujewa umarnin masarautar nan, domin wannan matashin ba zai yarda ya barka maka Waira ba, ko da kuwa ka yarda ka koma cikin kalar tsafinsa ne, idan kuma muka hana masa ita zai iya gwada jayayya da mu”

“Toh a bar mu mu kara mana, sai a gane waye jarumi”

Ya fada da kakkausar murya yana tabe baki kamar zai yagashi.

“Ba mu taba gwada yaki ba, kuma ba zamu gwada saboda wata korariya a garinmu ba, ban yi tunanin karfin tsafi zai yi tasiri a gareshi ba, ko da ya ce ba zai aureta ba, ba samu yarda ta aura daga garemu ba wannan shine magana ta karshe”

Eid da duk sauran mutanen da suke fadar suka risnar da kai domin nuna biyayya ga Umarnin Sarkin da ba a musawa. Eid ya dago yana kallon Maleek fuska kamar an aiko masa da mutuwa, zuciya kamar bakin maciji dake cike da dafi, ya fice daga fadar yana hararar Maleek yana huci kamar zai fitar da hayaki. Duk wani abun da ake fada Maleek be ji ba, domin da yarensu suke maganar, Waira kuma jinta da ganinta tunaninta mamakinta zuciyarta da ruhinta gaba daya sun tafi gurin mutumen da take kira da yayanta wato Ya Maleek. Furucinsa na cewa yana son aurenta da jarumtar da ya nuna akanta sadaukarwa neman kareta sassauta ra'ayinsa da nema mata farinciki da yanci wani abu da ya kai ta rubuta a dutsen da ba goge zane da alkalamin zinari. Hawaye take irin hawayen da ba zata iya fadar na minene ba a yanzu, na farincikin abun da Maleek yayi mata ne ko kuma na samun yancinta ko kuma na komawa da zata yi gurin matar da ta zame mata uwa? Ko kuma dai na fasa kasheta da aka yi ne? Wata kila kuma na tsafin da suka ce sun yi ta aikawa Maleek ne be same shi ba.

“Nuwaira...”

Kamar wadda aka jefowa numfashi daga sama haka ta zabura ta dawo hayyacinta, sai ta lumshe ido tana jin ba a taba kiran sunanta da dadi kamar yadda Maleek ya kirata a yau ba. Rufe idon da ta yi sai ya saka shi tunanin ko bata ra'ayi ne musamman ma da yayi arba da hawayen dake zuba a idonta gashi tun da ya furta maganar take kallonsa ta kasa cewa komai kuma ta kasa dauke idonta daga gareshi.

“Ko baki so ne? Karki damu, na yi hakan ne saboda na sama miki hanyar fita daga garin nan, idan sun amince sun ba ni aurenki da zarar mun fita ba aurenki zan yi ba, za a miki aure ne best on zabinki”

Rashin Eid a fadar da zai iya fassara musu abun da Maleek yake fada, ya saka Sarkin amfanin da nasa baiwar ta tsafi ya yi communicating da aljannunsa suka fassara masa abun da Maleek ya fada, hakan kuma ba karamin dadi yayi masa, domin ya fahimci Maleek ba gaske yake son Waira ba, hakan na nufin zai fara mata yi mata butulci da zarar sun bar garin kenan, kuma hakan ya nuna Waira bata son shi, a kokarin Sarki na bakanta musu ya kalli na hannun damansa ya ce.

“A fadawa Dardu ya tada busa ya hura wuta, mata su fara nika ganyen za a daura aurensu a yanzu”

Nuwaira ta bude ido da sauri ta kalli Sarki domin daga ita sai jama'ar garin suka iya jin abun da Sarki yake fada ban da Maleek. Sarki ya kalleta yana tana tauna hakora ya ce.

“Zamu aura miki shi, kuma zamu cire duk wani tsafi da kariya ta mu da take jikinki yanzu nan, kuma duk wani abun da zai faru ko ya biyo baya karki neme mu, babu mu babu ke da zuri'arki”

Kasa cewa komai ta yi sai har lokacin hawayen ba su daina sauko mata ba.
[8/12, 6:08 PM] 🦋-🦋: 77

Duk wata al'ada da ake gudanarwa kamin bikin auren sai da sarkin ya saka ka yi ta, ba a daura auren ba sai da suka hanka hannun Nuwaira suka cire layar dake cikin hannun nata, suka shafe jikinta da maganin da ke karya duk wani kalar tsafi na mutum, sannan aka daura musu auren har aka yi aka gama kuka take na azabar cire mata layar da aka yi a hannu. Maleek ya nemi izini ya koma masaukinsu ya dauki wayarsa sannan suka rakosu har bakin kofar garin suna tafiya ana wasa farar kasa a duk inda suka taka da haka har suka fita daga cikin garin. Kamin su isa gurin da motar Maleek take Nuwaira kamar zata fadi taka take taka kasar kafarta babu talkami ga jikinta sai rawa yake tana jin wata kalar azaba kamar an tsaga mata duka jikin. Maleek ya rigata karasa gurin motar ya bude mata back seat ta shiga ta kwanta domin bata iya zaman kirki ma, tun da ta rufe ido bata bude ba har ya kama hanyar Abuja. Sai da yayi tafiya mai nisa kiran Ameer ya shigo wayarsa shi har ya manta da waya a jikinsa ma sai a lokacin ya tuna. Hannu daya ya saka ya ciro wayar aljihunsa dayan hannun kuma yana driving da shi all his thoughts is Ummi ko Abiey ne ya kira but ga mamakinsa sai yayi arba da Number Ameer, haka nan kawai ya ji baya bukatar amsa kiran dan haka ya aje wayar a gefen seat ya cigaba da tukinsa a haka Ameer yayi masa kusan miss calls 30 da ya gaji da jin ringing din ne ya dauki wayar sai ya kiran Abiey ne ke shigowa wannan karon and ba zai ki amsa kiran mahaifinsa haka nan kawai ba.

“Hello”

“Maleek kana ina? How are you? Are you okay?”

“Ina lafiya kalau Abiey babu abun da ya same ni Nuwaira ce kawai bata da lafiya ina hanyar Abuja yanzu haka tare da ita”

“Alhamdulillah, amman me kake nufi tare da ita?”

“Labari ne mai tsawo Abiey but at the end dai sun ki karbarta sun yafe ta, and sun aura min ita bayan sun rabata da duk wani tsafi da yake jikinta”

“What? Okay Allah ya kawo ka lafiya”

“Ameen ina Ummi?”

“Tana saurenka muna tare da kowa a nan ka kula da hanya, mun yi magana da police akan cewar za su tafi yau su taho da kai bari na kira na fada musu kana hanya”

“I will”

Ya aje wayar ya maida hankalinsa gurin tukin yana yi yana dan juyawa ya kalli Nuwaira da idonta suke rufe.

“Nuwaira Nuwaira”

Ta bude idonta daker ta kalleshi.

“Sannu”

Bata amsa masa ba ta sake maida idon ta rufe. Haka yayi ta da ita har suka fara jiyo kamshin garin Abuja, ba shi tsayawa komai sai Allah ko ruwa be sha ba tun da suka bar Katsina har suka kusa isa Abuja. A lokacin da ya isa da ita cikin garin Abuja be sauka a ko'ina ba sai asibiti, domin ya lura da Nuwaira ta galabaita har bata iya bude idon ma idan ya kirata sai nishi take kamar mai nakuda.



AMEER POV.

Cikin wani yanayi na rashin lafiya ya isa gidansu Humairah ba dan ta kira a waya ya kasa amsa ba kuma yayi mata alkawarin zuwa ba da ba zai tafi a wannan yanayin da duniyar bata mishi dadi ba. Yana fakawa harabar gidan ta fito ta tarbe shi da far'ar irin na zumudin ganinsa sai dai yanayinsa da ta ganin bayan fitowa daga motar ya saka jikinta yayi sanyi daukin ganinsa da take sai ya ragu.

“Are you okay?”

“I don't know ina jin dai kamar ba ni da lafiya”

“Akan Waira ne?”

Yayi kamar be jita ba ya cigaba da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login