Showing 111001 words to 114000 words out of 281271 words
ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
37
AMEER POV.
Tun da ya shigo gurin Humaira ta lura da yanayinsa, yau ya dan fi sakewa fiye da jiya da shekaranjiya. Gorar ruwa ta dauka ta nufi inda yake, sai da ta fara aje masa ruwan sannan ta ciro biro da dan karamin littafi.
“Me za a kawo?”
Ya daga kai ya kalleta be jin zai iya amsa mata dan haka ya sauke kansa ya saka hannu aljihu ya ciro wayarsa ya fara latsawa.
“Me zaa a kawo maka?”
Ya mata banza, ta daure ta sake tambaya a karo na uku.
“Me za a kawo? Idan na bar gurin nan baka fada min ba, ko na kira ni ba zan dawo ba, me yasa kai a rayuwarka kake son ƙuntatawa mutane ne? Kai baka san dan adam yana da daraja ba?”
Ya dago ya kalleta a hankade.
“Nuna min inda taki darajar take, kina mace kin so kina aikin siyar da abinci a karkashin mahaifina, kina daukar order ko wane shege da dan'iskan, sannan ki tsaya a gabana kina min zancen daraja, be kamata kalmar ta fito daga bakinki ba ai, domin ke baki da ita, kudi su ne daraja, daraja shi ne ka cire talkami wani ya zo da gudu ya dauka ya wanke maka, ka zo restaurant wata ta zo ta tsaya a gabanka da abun rubutu tana jiran ka fada mata abun ka kake son ci ta kawo maka, daraja ka shiga mota idan ka tsaya mutane ta nufoka suna son ka ba su kudi, daraja ka zama mai ikonka kanka ba a karkashin ikon wani ba”
Ta kalleshi da kyau zuciyarta cike da bakincikin kalaman da ya fada mata.
“Dan'adam ba shi da zabin rayuwa kamin a haife shi, zabin iyaye ko yan'uwa ko gari ko addini, yadda Allah ya so haka yake halittar bayinsa, amman dan'adan yana da zabin yadda zai gode Allah bayan ya samu kansa a cikin wadannan abubuwan da na lissafa, saboda Allah ya baka kudi ko iyaye masu kudi, ba shi yake nufin ni baya so na, kuma be yi alkawarin zan tabbata a haka ba, Ameer kana butulce Allah da ni'imar da yayi maka, kana yawan fariya da abun da Allah baya so, girman kai ma alama ce ta yan wuta. Aikin da nake a nan ya fiye min na je na yi zina ko na lalata rayuwar wani hakkin zai min yawa. Amman a nan ko ba komai zan iya rike mutuncina kuma na kula da tarbiyar da iyayena suka min”
Tana akai aya ta juya zata tafi.
“Wonderful, ina yaba yadda idonki ya tsaya kam kike iya fada min magana any how”
Ta juyo ta kalleshi tana murmushi.
“Kasan dalilin wannan kwarin guiwar? Saboda wannan kamfanin na mahaifinka ne ba naka ba, mahaifinki nake yi ma aiki ba kai ba, yanzu da za a tambaye ka waye kai ka ce ne mai gurin nan zai fi burgewa fiye da ka ce a tambaye ka kace kai ne ďan mai gurin nan, kimarka zata ragu, kuma ka ga arzikin ba naka ba ne na mahaifinka ne, ina tausayin rayuwarka Ameer dadi da wahala basa tabbata har abada ka ji tsoron ranar da wannan jindadi zai gushe”
“Matsakar talaka kenan hassada ke yanzu har fata kike jindadin da nake ciki ya gushe?”
Ta saka hannu ta share hawayen da suka zubo mata.
“Arzikin da kake cin amanar yayan mutane kana lalata rayuwar yar mutane ka haifar da iyayensu bakinciki da damuwa, Allah sai ya isar musu”
“Baki ma san yadda abun yake ba sai na dandana miki”
“Na fi karfinka Ameer ko hannu baka isa ka rike ba balle har ka aikata abun da kake so da ni, ni ba irin dolayen karuwanka ba ne domin ni ba mazinaciya ba ce irinka..!”
Ta fada cikin ihu da kururuwa har hankalin mutanen da nesa da su sai da suka dago suna kallonsu.
“Kina wasa da wuta yarinya, ni zaki yi ma duniyanci? You will regret this”
Ta jefa masa littafin dake hannunta.
“Aiki ne? Na daina ko da kuwa rai ne a gurin nan sai dai na rasa shi”
Ta wuce fuuu ta koma ciki ta cire tufafin aikinta ta saka nata ta fice ba tare da ta yi ma kowa sallama ba. Yana kallonta ta fice sai ya mike tsaye yana amsa wayar Nimra.
“Hello”
Ta yi shiru sai hawaye take.
“Talk ba zan iya gane abun da kike nufi ba idan baki fada ba”
“Ameer zan tamvaye ka tsakaninka da Allah ka amsa min”
“What?”
“Ka taba son wata yarinya kamin ni? Kasan yadda Ciwon so yake? Ina daf da haukacewa Ameer”
“No ban taba soyayya ba, akwai dai wacce muka zauna a tare sunanta Angel, amman mun rabu kamin na hadu dake, sai dai daga ke har ita ban tana jin ina son kowa ba, ni a rayuwata ban taba son mace ba, but you lucky na ji jna tausayinki”
“Ba gaskiya ba ne Ameer ka ce duk soyayyar da ka nuna min ta karya ce, na san kana jin kwatankwacin abun da nake ji a raina, kawai kana bin cilastawar da iyayena suka maka ne cewar ka ce baka sona saboda su raba mu”
“Babu wanda ya isa ya cilasta ni, sau nawa zan fada miki wannan maganar ne?”
“Zaka iya rantse min Ameer?”
“Idan na rantse miki zaki yarda?”
Ta daga kai kamar yana gabanta.
“Wallahi tallahi ban taba sonki ba Nimra, ban tana jin ina kaunarki ba, ban tana jin soyayyarki a raina ba, duk wani kokarin kulla alaka da nake dake da kalaman da nake fada miki ko wani abun da nake nuna miki ina yi ne kawai saboda na samu nasarar yaudarar zuciyarki kuma na yi nasara sai dai ban yi amfani da damar kamar yadda na ayyana zan yi ba”
Wani abu ta ji ta soketa tun daga cikin kai har kasan kafafuwanta sai kuma ya dawo tsakiyar kahon zuciyarta ya tsaya, ta lumshe ido hawaye masu zafi suna sauko mata yawun bakinta ya canja dandano zuwa wani mai daci.
“Now I'm hurt... Thank you so much for everything, na gode Ameer”
Ta sauke wayar tana kamar ta hade zuciyata ta mutu gaba daya, gaskiyar da ya fada mata ta fi yi mata zafi siye da rabuwar da iyayenta suke son ta yi da shi. Maganar da Ummi ta fada mata cewar sun sha nono ďaya bata zauna mata a kai ba domin a tunaninta Ummi tana son raba tsakaninsu ba, sai dai a yanzu ta gamsu da maganar dan'uwanta Maleek cewar bata san waye Ameer ba. Ta saki wayar hannunta ta fadi kasa kafufuwanta suka fara rawa kamar ba za su dauke ta ba, tana kokarin mika hannu ta rike karfen windows din da take tsaye a kusa da shi ta kasa sai dai ta yi nasarar rikon curtains din windows din ta janyosu da karfi suka fado kanta ita kuma ta fadi kasa, nauyin kirji ya danne mata numfashi tana son ta daga murya ta kira akawo mata taimako amman ta kasa saboda numfashin baya barin muryarta fita, sai shakkuwa take kamar mai fitar rai.
“Hello...”
Jin shiru bata amsa ba kuma bata ce komai ba ya saka ya yanke kiran, ya cira kafa ya taka zuwa gurin motarsa ya shiga har ya murza key sai kuma ya fito koma ciki, sai dai wannan karon ba cikin yafa kai tsaye ba sai da ya tambaya ina kitchen din gurin yake aka fada masa sannan ya shiga kai tsaye ya doahi kitchen din wadanda suka san fuskarsa suna ta gaishe shi, be amsa musu ba domin ba gaisuwar ce ta kawo shi ba.
“Ina kuke aje kayan da kuke aiki?”
Ya tambayi wani namiji wanda daya ne daga cikin masu dafa a abinci a gurin, sai ya nuna masa hanyar da ake zube kayan da aka wanke, Ameer ya nufi gurin yana dubawa sai da idonsa suka sauka akan wukaken dake aje a gafe daya na aiki, ya isa gurin ya zari daya ya juyo sai duk suka ja baya da suna kallon juna irin kallon na gulma wasu na ala ala idan ba a cikinsu zai dabawa wani ba.
“Ranka ya dade wukar nan ta aikinmu ce”
Ameer ya juyo ya watsa masa harara sannan ya fice, kamar zai tashi sama haka ya isa gurin motarsa dake kunne yana ta sauri, ya bude ya shiga yayi reverse ya fice daga gurin. Left side ya fara bi yana tafiya yana duba gefen hanyar, ganin babu abun da yake nema bata isa barin unguwar ba domin hanya ce mai tsawo kuma guri ne da ba a cika zirga zirga da motoci, wannan dalilin ne ya saka mutane ke son restaurant din ne, unguwa ce dake nesa da mutane kuma guri ne da babu hayaniya da ganin mutane barkatai, wani ma har ya shiga yayi abun da zai yi ya fito ba za a san ya shigo ba, saboda yanayin gurin da kuma unguwar. Ya juya kan motar ya dawo right side yana gudu sai yana kallon gefen titin addu'a kawai yake a ransa Allah yasa ya ganta, kuma ya san zai ganta matukar ba wani gurin ta shiga ba, ko kuma wani ya rage mata hanya.
Humairah na tafiya gefen titi wata motar aka rage gudun motar ta dawo daidai ita ta tsaya, tsoro ta dan ji domin bata san waye cikin motar ba, tsayawa ta yi tana kallon bakin gilashin da aka sauke, ga mamakin Ameer ne matukin motar, da kai yayi mata alama da ta shigo ciki sai taja tsaki ta dauke kai ta cigaba da tafiyarta, tuka motar yake a hankalin yana binta ganin kamar bata fahimci abun da yake nufi ba ya saka shi mika hannu ya bude mata front seat. Sai ta tsaya kamar zata shiga sai da ta ga shi ma ya tsaya sannan ya kama murfin motar ta rufe da karfi har sai da yayi kara kamar zai cire, ta cigaba da tafiyarta ya sake binta ya bude mata gambun motar.
“Get in”
“Ba zan shiga ba, har ka isa me kake nufi da na shiga an fada maka ni yar iska ce? Ko kuma ni an fada maka ban san ciwon kaina ba? Ko an fada maka tsoronka nake? Ba zan shiga ba, aiki ne daga yau na zan sake yi ba, balle har ka wulakanta ni”
Jan motar yayi ya matsa gaba ya faka yana jiran ta karaso, ita kuma ta ayyana a ranta cewar ba zata shiga motar ba ko da kuwa hankata zai yi. Sai dai abun da bata sani ba ya shirya mata, tana isowa gurin ya bude motarsa ya fito ya zagayo gefen da take.
“Wai Ameer me ka dauki mutane ne? Bayinka? Ka rika juya su yadda kake so kana cilasta kowa yin abun da ka ga dama? Ni abun kunya ne a gareni a gan ni a motarka, domin ni ma zai ayi min daukar yar bariki...kuma... ”
Bata karasa ba ya dago wukar dake boye a hannunsa ya nunata saitin wuyanta.
“Ke idan kika fara zuba baki san ki tsaya ba, idonki yayi tsauri baki tsoron kowa”
“Ina tsoron wuka Ameer dan Allah karka kashe ni”
“Shiga mota or will cut your throat”
“Toh”
Jikinta na rawa ta bude motar tana ta kallon titin ko zata samu wanda zai taimake ta, motoci biyu da suka wice ba su damu da kula da abun da le gafen titi ba balle har a kawo mata dauki, haka ta shiga motar ya rufe sannan ya zagaya, wani bangare na zuciyarta na raya mata cewar ta fita ta gudu kamin ya shiga sai dai ina tsoro irin na masu bakin tsiwa ya hana ta aikata komai har ya shiga motar ya fara tuki fa hannu daya, dayan hannunsa kuma yana rike da zumgurariyar wukar ta yankan nama.
“Dan Allah karka cutar da ni Ameer? Me na maka?”
“Baki san abun da kika yi ba?”
“Toh ka yi hakuri ba zan sake ba, yaushe kuma ka koma yin dabanci ba a san yayan masu arziki da wannan dabi'ar ba”
“Yau na fara, kuma kina yin wasa zan yanka wuyanki ko na fada cikinki kin ga dai ba za ayi min komai ba ko? Idan na kashe ki an kashe banza dan haka ki bini a hankali”
“Toh... Yanzu gida zaka kai ni?”
“Saboda gani direban ki ba”
“Amman Wallahi tallahi na rantse da Allah ni ban taba iskanci ba, dan Allah karka lalata min rayuwa Ameer”
“Ni na taba iskancin, negative mind daman shi ne a ranki, you should be praised kin shiga motata ma ni me zan yi a jikinki?”
“To miyasa zaka dauke ni a motar kana ta tafiya me zaka yi min? Dan Allah karka yi tsafi da ni toh”
“Dodona baya son irin jininki”
Cikin dabara ta kai hannu ta murda gambun motar da zimmar ta bude sai ta ji shi a rufe.
“Na shiga uku na lalace”
Ta fara kuka, hankalinta ya tashi sosai domin bata san manufar Ameer na yi mata haka ba, kai ta zai yi wani gurin ya aje ko ya hukuntata akan abun da ta yi ko kuma wani abun zai mata.
“Ni zan iya baka hakuri a bainar jama'a idan dan abun da na yi maka ne, zai saka ka hukunta ni, dan Allah dan darajar iyayenka ka yi hakuri”
Kallonta kawai yayi ya dauke kai, yadda ta makure a cikin motar ta zama marainiyar gaske duk sanyin ac motar ita gumi take ga idonta ya zurma kamar zuru. Faka motarsa yayi gefe ya bude ya fita rike da wukar da kuma wayarsa da key motar da Daddy ke kira. Yana piciking kiran Daddy ya tambaye shi.
“Kana ina Ameer”
Ya juya kalli inda yake.
“Wani guri Daddy?”
“An fada min ka shiga har gurin da ake dafa abinci ka dauki wuka, me zaka yi da ita?”
“Wani zare na yanke a jikin tayar motata”
“Ameer ba ka min karya karka fara, ni nasan ko me zai faru ba zaka yanke zare a jikin motarka ba”
Yayi dariya.
“Daddy maganar gaskiya wata yarinya na yi ma barazana da ita”
“Subhanallahi barazana da makami Ameer? Kar zuciya ta dauke ka ka aikata kuskure, ka zo ka same ni gida yanzu nan, sai mu ji idan akwai matakin dauka kamata a adauka akan yarinyar kuma na ji abun da ta yi maka”
“Ba wata babbar matsala ba ce Daddy karka damu”
“Na ce ka zo mu tattauna, kuma karka tana yar mutane Ameer dan Allah”
“Okay Daddy gani nan zuwa”
Ya sauke wayar ya nufi motar ya cire key ya shiga ya zauna, tun da suka kama hanya suna tafiya bata ce masa uffan ba sai share hawaye take gabanta na zillo tana ta tunanin inda zai kaita zuciyarta sai sake sake take mata. Tafiya mai nisa suka yi sannan ya shigo umguwar manyan mutane ya fama gaban wani katon gida da gate din gidan ma ya isa bakauye kallo. Wani karamin littafi ya dauko ya fara rubutu, yana yi tana leko har ya gama ya nade takardar ya mika mata sannan ya bude gurin daya aje wayar Nimra ya dauko ya mika mata.
“Shiga gidan nan ki kai wannan wayar tare da takardar nan, amman idan kin shiga ki ce ke kawar Nimra ce kin zo ganinta, sai idan kun kebe zaki bata”
“Wallahi ba wata Nimra yanke min kai za'ayi wannan katon gidan na yan mafiya ne”
“Kwarai kin san mahaifina kudin tsafi yake da su”
Ta lake kafada tana kuka.
“Ni ba zan shiga ba, Allah ya fika”
“Ke look babu abun da za'ayi da katon kan nan naki, yarinyar da kika rika zagina kwanakin baya saboda ita, to gidansu nan, so nake ki shiga ciki ki kai mata wayar nan da wannan takardar, daga nan sai ki duba lafiyarta daman na ga kin damu da ita ai”
“Idan aka kashe ni hakkina yana kanka”
“Idan baki shiga ba, zan saka wukar nan na yanka ki, ko kuma na dauke ki na kaiwa abokaina su yi miki wulakanci son raina, dan haka ki zabi ďaya”
“Ameer me yasa kake mugu ne? Kana ta daukar hakkin mutane da basu maka komai ba”
“Toh bari na zabar miki a cikin ukun”
“Zan tafi, ka bude min motar”
“Idan na bude miki motar kuma ki gudu, na biki da wukar nan ko kuma na aika har gidanku a daukoki ai kin san dai na san gidanku ko?”
Ta daga kai, ta zabi shiga ne saboda shi ne mai sauki a cikin hukuncin abubuwan uku da ya shar'anta mata ta zaba, ta san ko da masu fille kai ne zata musu addu'a, idan kuma abun da ya fada ne a ciki idan ta aikata ga huta. Ta karbi wayar da takardar ta saka a jakarta sannan ya bude motar ya fita ya zagaya bangarenta ya bude mata ta fito.
“Kina yin wani abu kin san sauran”
“Me yasa kai ba zaka shiga da kanka ka bata ba, idan har da gaske gurinta ka zo”
“Ki kwankwasa kofa a bude miki”
Ya koma cikin motarsa ya zauna yana kallonta tana kallonsa, yana ganin ta matsa jikin gate din ya danna mata horn ta koma. Cikin tsoro ta kai hannu ta kwankwasa kofar gidan dake rufe sai da ta yi haka sau uku sannan aka bude kofar ganin mutumen daya fito yana sanye da uniform din police ya saka ta dan ji sanyi a ranta, ta juya ta kalli motar Ameer yayi reverse da ita zat tafi ya barta a gurin.
“Na zo gurin Nimara ne”
Ta fadi sunan a birkice tsabar tsoro da rashin rike sunan da ta yi.
“Ke wacece?”
“Kawarta ce”
Police din ya kalleta kasa da sama, shi dai be san yaran gidan na da kawayen da basa da motoci ba, yanayin mu'alamarsu ya saka ba kasafai suke zuwa gidan kawaye ko kawaye su zo nemansu ba, idan ma sun zo suka zo da manyan motoci ne, sai dai Humarai a kasa ta zo duk kuwa da ya hango motar da ke kokarin juyawa wacce yake kyautata zaton a ciki aka kawota.
“Kun yi da ita zaki zo?”
“Eh ga ma wayarta a hannuna tace na zo mata da shi”
Ta saka hannu a jaka ta dauko wayar tana nuna masa.
“Toh jira a nan ina zuwa, wa a ce mata?”
“Ka ce... Ka ce... Ka ce.. Aisha Humaira ce Ameer”
“Aisha Humaira Ameer?”
Ya maimaita sunan sai ta daga masa shi.
“Yeah”
“Okay shigo sai ki jira nan”
Ya matsa