Showing 93001 words to 96000 words out of 281271 words
“Nimra...”
“Na'am”
Sai ta amsa cikin kuka muryarta na rawa gwanin tausayi.
“Bude kofar nan, zamu yi magana da ke”
“Aa Ummi aa dan Allah”
“Ki bude na ce, so kike ki sake bata mana rai? Tambayarki zamu yi kuma dole ne ki amsa mana zamu yi magana ta fahimta ne ki bude kofar”
Ummi ma da kamar fada take mata maganar domin ita ma nata ran a bace yake. Sanin Abiey zai fi yi mata sassauci idan Ummi tana kusa ya aaka ta nufi kofar ta bude tana kuka sai ta matsa baya da sauri. Ummi ce ta fara shigowa sannan Abiey da sauri Nimra ta yi gefen Ummi sai Abiey ya daka mata tsawa.
“Karki kuskura taba min mata, dawo nan ki tsaya...!”
Wani irin dauke numfashi ta yi kamar zata shide, saboda tsawar ta ratsata kanta shiga har cikin jikinta, sai ta dawo ta tsaya a inda ya nuna mata jikinta na rawa.
“Tun yaushe kike aikata fasadin nan? Me ya saka baki bashi damar zuwa gidanku ba kika zabi kebewa da shi?”
“Saboda ba za su yarda ba Abiey, kuma ba mu aikata fasadi ba Abiey, Wallahi ban aikata zina ba”
“For how long kike tare da shi?”
Ummi ta tambaya.
“Anfi shekara.....”
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, waye ubansa a garin nan dan gidan uban waye? Akan wani dalili kike haduwa da shi a wajen gidanku?”
Abiey ya tambaya yana matsawa kusa da ita, muryarsa kuwa kamar zata tashi ďakin. Matsawa ta yi baya tana kallon Ummi kamar tace Ummi zo ki cece ni ba dama. Bata ankaro ba Abiey ya kai mata mugun naushi a fuska sai da hokoranta ďaya ta dago bakinta ya cika da jini, wani tsalle ta ta yi, ta yi baya da sauri ta rike bakin ta haura saman gadonta.
“Wayyo Allah na na shiga uku, Ummi ki taimake ni Abiey ka yi hakuri dan Allah”
“Waye shi na ce?”
Ya sake daka nata tsawa, a rike ce ta fara zazzago masa bayani.
“Ameer ne, Ameer dan gidan Alhaji Bashir, wanda suka yi faďa da Ya Maleek, Ameer din da na bawa Motata ta tafi da ita Katsina Ameer ďin...”
Bata karewa ba Abiey ya daga mata hannu ya rumtse ido, Ummi kuma ta fadi zaune tana kallon Nimra cikin matukar tashin hankalin da ba a saka masa rana.
“Bakar zuri'a, bakin jini, ubansa ya gama shi kuma yanzu na shuka min nashi, so yake ya lalata min zuri'a so yake ya ɗasa min bakincikin da ubanaa ya bari...”
Abiey ya fada cikin wani irin fusata da be san ma iya abun da zai fito daga bakinsa ba. Kamin ya juyo gurin Ummi.
“Duk laifinki ne, babu gargadin da ban miki ba akan yaron nan, ta ya za'ace yarinya tana fita waje ta hadu da wani sama da shekara ďaya baki sani ba a matsayinki na uwa sai bayan da ya gama lalata min ƴa?”
Ummi ta mike tsaye tana kallon mijinta cikin wani irin bacin rai ta amsa masa.
“Kwarai laifina ne Alhaji Aliyu sai ka hada ni da ita Nimra ka binne...!”
Ta daki kofar ďakin da karfi ta fice fuuu kamar zata tashi sama.....
MALEEK POV.
“Ohhhh”
Ya fada yana buga teburin dake gabansa, bayan Abiey ya fada masa ya tafi makarantar su Waira ya ji abun da yake faruwa saboda sun buga masa waya kan cewar ta yi fada, kuma ya kira wayar Mahmood be samu ba, ga Ummi ya ji yanayinta da matsala zai tafi gida. A dole dolensa ya tashi tare da wayarsa da key din motar ya fice daga office din, yana gwada kiran Mahmooda ya ji ko zai same shi ya fada masa Abiey yace ya tafi saboda shi ya fasa zuwan, be samu ba har ya shiga motarsa ya murza key ya dauki hanyar makarantar. Har ya isa cikin makarantar be daina karan Mahmood ba kuma be samu wayar ba.
Cikin makarantar ya shiga gurin principal din ya gabatar da kansa, sai suka isa da shi gurin vice principal, a nan ya samu Waira zaune rumgume da jakarta, tana ganinsa ta mike tsaye da sauri ta nufo inda yake wai ita ta ga wanda ta sani sai kuma ta ja ta tsaya tunawa da basa shan inuwa ďaya. Gurin ya samu a one of visitors chairs ya zauna yana kallon mutumen da ya mika masa hannu suka gaisa.
“Sunana Maleek na zo ne akan maganar wannan yarinyar”
Ya nuna Waira.
“Eh mahaifinka ya kira ai ya fada cewar ba zaka samu zuwa ba, amman ďansa zai zo”
“Lafiya me ya faru?”
“Fada suka yi da wata yarinyar, ita dai yarinyar tace Waira ta fara tsokanarta, sai suka fara fada shi ne ita Waira ta dauki dutse ta buga nata akai kanta har da jini yanzu haka ita ma mahaifinta yana hanya”
Maleek ya juya ya kalli Waira da ta rumgume jaka, sannan ya juyo ya kalli mutumen.
“Waira bata da fada gaskiya, sai dai ko idan ita yarinyar ta fara taba ta”
“Ba a gane gaskiyar kowa, ita ta kasa magana daidai yadda za a fahimce ta”
Maleek ya dauki takadar dake gaban teburin mutumen ta pen ya mika mata.
“Rubuta abun da ya faru”
Ta karba ta soma rubutawa tana hawaye.
“Kullum tana tsokanata tace min ni ban iya hausa ba, kuma bana magana da daidai, tana ce min kuma kafira ban san me hakan ke nufi ba, ko ta rika min dariya, shi ne yau da aka kai mu park ta tsokane ni kuma na buga mata dutse saboda ta fi ni girma ba zan iya fada da ita ba”
Ta mika masa sai ya karanta ya mikawa mutumen, mutumen ya karba yana tsaka da karantawa mahaifin yarinyar ya shigo tare da ita, har wani hakilo yake yana an taba masa ya.
“Wannan ne mahaifin yarinyar?”
“Aa yayanta ne bismillah zauna mana”
“Ba zan zauna ba, kuma sai na dauki mataki akan abun da aka yi ma yata matukar ba ku hukunta yarinyar nan ba sai kun ga abun da zai biyo baya domin ďa be fi ďa ba”
“Ka yi hakuri ka zauna muna tattauna ne a akan maganar?”
“Tattaunawar me? Ga ciwo kuna kallo ta ji wa yata kuma ku ce kuna tattaunawa karshenta a ba ni hakuri bayan an cucu yata”
“Toh me kake so ayi maka Malam? A fashe mata kan ita ma? Bayan kuma yar ka ce take tsokanarta?”
A take fada ya kaure a tsakaninsu, domin Maleek ya kasa jurewa da abun da mutumen yake yi ne, suka yi ta fadawa juna magana daker aka shigo tsakaninsu, Maleek ya saka Waira a gaba suka fito daga cikin makarantar zuwa gurin motarsa. A nan Waira ta nade hannayenta ba zata shiga mota ba, daman can bata kebewa daga ita sai shi a mota ba, fadan da ta ga yayi da wacan mutumen ya saka ta tsorata tana ganin kamar itama fadan zai mata idan ta shiga motar. Ya bude mata motar da kansa.
“Shiga mu tafi”
Ta lake kafada.
“Shiga ko na mareki yanzu nan”
Ya daka mata tsawa, sai ta shiga motar da sauri ya rufe ya zagaya dayan side din ya shiga ya saka key, wani yanayi ya samu kansa a ciki na dabam, domin be taba kusanci da mace a mota kamar haka ba, be ma taba daukar mace a motarsa ba, sai wannan karon wanda ya tabbatar da acan da ne ba zai ma iya ba, ko da kallonta ne balle har ya dauketa.
“Waira bata son Abiey, Abiey ya kira waya yayi mata fada, Waira bata son Maleek, Maleek ya zo da mota yayi mata fada ta shiga Mota”
Ta fada tana takurewa gurin daya sai hawayen da suka fi kama da na shagwaba take. Ya kalli gefenta ya dauke ido.
“Baki son uba, baki son ďansa sai ki kashe su toh”
Tana jin hakan ta san bakar magana yayi mata sai kawai ta fashe da kuka, ta kama zoben dake wuyanta ta rike. For the first time ya ji kukan mace ya sauka a kunnensa daidai wa daida ya cika kwakwalwarsa.
“Ohhhhhhhhh miye wannan kuma? Zaji min kuka for sake i hate this crying, Abiey why zaka aiko nan? Kai”
Ya bude wani guri a motarsa ya dauko airpod ya saka a kunnesa ya kunna Bluetooth din wayarsa yayo connected ya kure karatun Qur'ane dan ya daina jin kukanta. Har aka isa gida bata daina kuka ba, shi kuma be bata hakuri ba ko kallon inda take be yi ba. Tana ganin ya cire abun kunne ya kashe motar sai ta bude muryarta mai kara ta kwala ihu just to annoy him tun da ta lura baya son kukan.
“Louder please”
Ta kara karawa tun da ya bukaci haka.
“Very good well done, to fitar min a mota please...”
Bata fita ba sai cigaba ta yi da kukan, shi kuma ya bude motar ya fita ya barta a ciki. Yana shiga cikin falon ya san ya lafiya ba, domin tun a downstairs yake jin kukan Nimra bama kamar da ya haura sama. Dakin mahaifiyarsa ya fara shiga sai ya same ta tsaye gaban madubi tana hawaye, kamar jiran take ya shigo sai kawai ta juyo ta fara bashi labarin abun da ya faru tana ta maimaita gurin da Abiey yake dora mata laifi, tun fara bashi labarin har ta gama hawaye take.
“Ba zai bar ni da abun da ya ishe ni ba, sai ya dauko wani laifin ya dora min?”
Maleek be ce komai ba ya juya a fusace ya fice daga dakin Ummi, be yada zango ko'ina ba sai ďakin Nimra, yana shiga ya maida kofar ďakin dakw bude ya rufe ya saka mata key.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 31
“Nimra i thought mun rufe babin Ameer tun a lokacin da kika bashi aron motarki”
Maleek ya fada bayan rufe motar da yayi. Kuka kawai take ta kasa cewa komai.
“Tun a lokacin Abiey da ni da Ummi mun nuna miki ba mason wata alaka tsakaninki da shi, ko dan mu ya kamata ki nisanta kanki da shi, kin manta bacin ran da kika saka mu a wacan lokacin ne?”
“Ban manta ba, ban kuma fada soyayya da shi akaran kaina ba, ban yi soyayya da Ameer Saboda zuwan wannan ranar da zan bata muku rai ba, ban san miyasa kuka tsani Ameer da yawa ba, kamar wanda ya kashe muku wani”
“Baki san waye Ameer ba ne Nimra, duk mai kaunarki zai so ki auri mutumen kirki, I'm not saying Ameer ba shi da kirki no, mutum ne da wani be isa ya saka shi ko ya hana shi aikata abun da yake so ba, and i don't think ma yana kaunarki da gaske saboda mun hada jini da ke, and i know ya fi tsanata da kowa a yanzu”
Ya karasa bakin gadon ya zauna.
“Zai fi kyau ki hakura ki cire shi a ranki, saboda iyayenki basa so, kalli abun da ya ja miki a yanzu, and kin manta yadda ya batawa iyayenki rai lokacin da kika ba shi motarki? Da ace Abiey be yi nasarar rufe case din nan ba, ko kuma ace yarinyar nan gawa ce aka samu a motar baki san iya abun da hakan zai haifar miki ba”
“Ameer be ja min komai ba, shi kullum neman yake a bashi dama ya sanar da iyayena cewar yana kaunata, amman saboda tsoron abun da za ku fada ya saka na boye soyayyarmu, har hakan ya faru amman Ya Maleek ina son Ameer idan kuka raba ni da shi zan iya mutuwa...”
“Indai har baki mutu kamin ki sanshi ba, to ba zaki mutu saboda kin rabu da shi a yanzu ba, Ummi kuka take saboda abun da kika aikata Nimra, ta samu rashin fahimta da Abiey duk saboda ke baki ji kunya ba? Har kike iya fadar zaki mutu idan kika rabu da shi, da shi ne na tabbatar zai iya rabuwa da ke a take”
“Shi ma ba zai iya ba, yana so na tsakani da Allah ne, ya hade soyayyar masoyi da ta ďan'uwa da ya kasa nunawa yar'uwarsa shi ya nuna min, kana cewa na rabu da shi saboda baka taba so ba Ya Maleek wani digo be taba dirar maka a zuciya da sunan soyayya ko kauna ba, ba san miye a cikin shaukin son ba, saboda ka kasa rabar kanenka mata ma balle ka nuna musu so, baka taba yin budurwa ba, idonka be taba duba wata mace da rahma ko tausayi ba, balle kuma so! Wallahi Ya Maleek na shiryawa karbar ko wane kalar kalubale akan Ameer, idan ba har kuna da wani matsala da shi da dabam ba, be kamata fadanku ya taba soyayyar mu ba, idan har kasan zafin rabuwar uwa da ďa, to haka rabuwar masoya take, amman kai ba zaka gane ba saboda baka taba ďanďana zakinta ba, da gaske nake Ya Maleek idan kuka Ameer mutuwa”
“Ya ji wata yar iskar yarinya yaushe kika san Ameer din ma, da zaki fada min haka? Okay idan har Abiey zai yarda ki aureshi ko Ummi sai ki aureshi din, amman idan suka nuna basa so, ba zaki aureshi ba, ki rubuta wannan ki aje”
Ya mike tsaye ya juya.
“Saboda baka san me ye so ba Ya Maleek, aure zamu yi ba zaman banza ba”
A fusace ya juyo ya daka mata tsawa.
“Yanzu me kuke yi? Ke ce baki san waye Ameer ba Nimra amman ni na san Ameer in and out, na san abun da zai iya da wanda ba zai iya ba, da ace sonki yake da gaske, da ya sauke gabar da yake da ni dan shi ne ba shi da gaskiya, amman a halin yanzu Ameer ya bata da duka friends din mu saboda ni, idan na zauna a guri Ameer ba zai sake zamansa ba, idan na gaisa da wani Ameer ba zai sake magana da shi ba, taya zaki kalli idona ki fada min cewar Ameer da gaske yake son ki? idan ban soyayya ba ai na san hankali da tunani, don't you think yana amfani da ke ne kawai saboda ya bata min rai? Ameer baya yafiya, Ameer baya aje burinsa saboda wani, ba ya kashe kansa saboda wani ya rayu, ya sani duk ranar da na san yana soyayya da kanwata zan yi bakinciki wannan ma kadai abun farinciki a gurinsa, and i know one thing for sure Nimra, Ameer ba zai ajeki a gidansa for more than one year ba tare da ya taba ki ba, ko dan kasancewar ki kanwata zai aikata miki komai, and bari na fada miki wani abun da baki sani ba, Ameer yana da mistress ya ajeta a wani gidan na dabam you're not the only one wannan kadai be isheki abun kunya...?”
“Ameer ba shi da kowa sai ni, kuma ni Ameer ba taba min komai ba, saboda so na yake da aure, baka fahimce ba ne Ya Maleek, ka bude zuciyarka ka zuba mata tausayi da soyayya, ka zahilci so...”
Da mugun mamaki Maleek yake kallon.
“Ina fada miki gabas kina fada min yamma? Saboda an kyale ki?”
Baya son saka hannunsa dan haka ya nufi gurin Laptop dinta take ya fisgo carjar ya nufi Nimra da ita ya fara dukanta kamar an aiko shi, tun yana dukanta tana ihu har ta kai muryarta bata iya fita Ummi kuma ta saka fitowa ta ceceta sai nata kukam take a dakinta tana sauraren muryar Nimra. Waira ce ta hau sama ta tsaya bakin kofar ďakin Nimra tana buga kofar da karfi, ba dan ta san abun da yake faruwa ba, domin shigowar kenan bayan ta ga ji da zama a motar da Maleek ya barta. Kamar wanda aka cewa ka yi ta dukanta har sai bacin ranka ya fita haka Maleek ya rika zunawa Nimra wayar carjar laptop din a jiki ido a rufe har kafarsa ya saka ya shureta, abun da be taba ba, ya kan doke su amman acan baya lokacin da suke shige masa hanci da kududdufi sai dai ba kamar irin dukan da yayi mata a yau ba.
“Do you know what? Da ina tunanin idan Abiey da Ummi suka amince zan goya miki baya ki aureshi, but yanzu na yanke hukunci ba zaki aureshi ba, sai kuma na ga yadda zaki yi, ki mutum na gani”
Ya karashe tare da kwafa sannan ya juya ya nufi kofar ďakin ya bude, sai yayi arba da Waira, ita ma ta yi arba da shi da bulalar wayar dake hannunsa, hannunsa dake rike da bulalar ta fara kallo sannan ta kalli fuskarsa dake hade kamar bakin hadari, a zatonta ya gama dukan Nimra ne ya fito ita ma yayi mata nata, sai ta kwala kara iya karfinta har sai da ya dafe kunnensa ya kauce daga gurin ya sauka kasa da sauri zuwa ya nufi bangaren mahaifinsa yana jin kansa na mugun sarawa, domin tana da ƙyaƙyar muryar irin wannan mai shiga har can cikin amon kunne. Ummi ta fito da sauri tana share hawayenta ganin Waira tsaye a kofar ďakin Nimra ya saka ta karaso da sauri, ganin Ummi ya saka Waira ta yi shiru domin a yanzu ta gama fahimtar babu lafiya a gidan, ganin Ummi ma tana kuka.
“Lafiya? Waya taba ki?”
“Ya Maleek ya dauki bulala zai daki Waira”
Ummi ta rika hannunta taja ta suka nufi ďakinta, hakan ya bata damar rumgume Ummi ta sauraren dalilinta na kuka.
NIMRA POV.
Maleek na fita daga dakin ta ji ihun Waira da kuma Isowar Ummi taja hannunta suka bar gurin ta san, Ummi ta ajeta a gefe kenan, ba dan haka ba da yanzu ta iso da gudunta a lokacin fa Maleek yake dukanta ta tare mata dukan har ma ta yi fada da Maleek din, amman gashi bata zo ba, sai da Waira ta yi ihu, furucin da Maleek yayi mata da kuma bacin ran da ta gani a fuskar mahaifinta, ya matukar daga hankalinta ya kuma tabbatar mata da cewar ba za su taba yarda ta auri Ameer ba, ita kuma a yanzu tana jin ta shiryawa mutuwa akansa, bata taba so ba sai akan Ameer wani namiji be taba shiga zuciyarta ta juyawa yadda yake so ba sai Ameer, dabam wanda be saba ba idan ya samu ba shi ma so da sauki, iyakar gaskiyarta tana nufin