Showing 75001 words to 78000 words out of 281271 words
“Wannan be dace ba Ameer haramun be”
Dariya ya saka mata yana mata kallon mamaki.
“Karki ce min baki taba yin saurayi ba, or baki taba rike hannun namiji ba ko kissed even slept with him?”
“Subhanallahi Wallahi ban taba ko daya ba, ban taba saurayi ba balle har na kai ga aikata abun da kake tunani”
“So you're still Virgin? ”
Ta dauke idonta tana kallon wani gurin.
“You miss alot, babbar yarinya kamar ke? Baki da kawaye ne? Ina kika yi rayuwa?”
Ta bude motar.
“Ya kamata na tafi kar wani ya dawo be same ni a gidan ba”
Hannunsa ya mika ya juyo fuskarta ya matso da ta shi yana kallon bakinta sai ta juya ya sake juyawa da ita wannan karon gaf da ita yake, har tana shakar numfashinsa.
“Taya zan yarda baki taba kissed wani namiji ba?”
“Saboda ban taba yi ba, kuma ba zan yi karya ba”
“Can you swear?”
“Wallahi ban taba yi ba Ameer”
“Idan kuma kin taba yi kika min karya Allah ya halakaki kamin ki isa gida kin yarda?”
“Na yarda”
Tana rufe baki ya saka bakinsa cikin nata, abun ka da wanda be saba ba sai ta kasa komai har ya gama yawo da halshensa a bakinta ya cire, a nan kam tsoro ya bayyana a idonta sosai kamar yadda ya bayyana a jikinta take rawa har yana iya gani, wannan kadai ya isa ya yarda cewar bata taba tarayya da wani ba.
“Ki aje mana wannan sirrin, saka min number wayarki zan kira ki anjima amman zaki min wani alkawari a duk lokacin da na bukaci ganinki zan ganki?”
Ya dauko wayarsa ya mika mata, ta karba ta saka mashi number, sannan ta juya zata sauka ya sake riko hannunta.
“Baki min alkawari ba”
“Zan duba”
“Ba zan ce dubawa ba ne, zance ake na rayuwata i can not breathe when you're not near idan kuma kin fison na rika zuwa gidan ku kai tsaye then fine zan dauki ko wane risk just to see you Nimra...”
Kallonsa take, da gaske so take ta gane idan kalaman da suke fitowa a bakinsa har a zuciyarsa suke, miyasa zai sauya mata a iya yau kadai? Ya sumbace ya fada nata ba zai iya numfashi idan bata kusa ba, ya rika hannunta kuma yayi mata godiya da kawo masa sarewar da ta yi. Ganin irin kallon da take masa ya saka shi cewa.
“Na san fada muke, amman dukan abun da kika ba ni na karba na karba ne saboda na yarda dake, and now na bukaci ganinki kawai ba dan ina son sarewar ba, na san hakan kadai zan miki ki yarda mu hadu, zuciyata taan samawa kanta abun da take so ne Nimra ba tare da duba matsayi ko gaba ba”
Mutumen da ke ta rigima da ita ya ki yarda ba da hadin bakinta aka shirya masa komai ba, mutumen da girma kai kadai ya isa ya hana shi yin godiya a gareta. Da gaske abun da yake fada haka ne har zuciyarsa? Ta janye hannunta ta sauka a motar.
“Zamu rika haduwa wani gurin ba gidan mu ba”
“Okay take care of yourself”
Ta juyo ta kalleshi sai yayi mata murmushi, wata kalmar bata sake fitowa bakinta ya nufi motar da ta zo da ita ta bude ta shiga. Har ta yi ma motar key ta hau titi be bar gurin ba kuma be fasa kallonta ba har sai da ya daina hangota. Tana tukin tana tunanin yadda zuciyarsa ta karaya da wuri haka, ya yarda da ita kenan? Ta kai hannu ta taba bakinta amaimakon ta ji haushin abun da yayi mata domin bata taba aikatawa sai ta yi murmushi tana jin wani irin kimarsa na karuwa a idonta.
“Is this the sight of love?”
Ta tambaye kanta, domin wani irin yanayi take ji na dabam tun farkon haduwarta da shi har zuwa yau da wani abun ya shiga tsakaninsu? So ne ya saka take ganin abun da ba daidai ba a daidai har take iya karya dokar gidansu data mahaifinta? Take iya kyale wanda ba muharraminta ba ya rika hannunta har ya sumbance ta? Wata kila shi ma son ne ya saka shi saurin yarda da ita, daman ance wanda be taba yi ba idan ya fara masa baya masa da sauki. Kamar wanda aka yi ma albishir da yafiya haka Nimra ta wuni da farinciki da annashuwa a ranta ba ma kamar lokacin da ya kirata yana ta kashe ta da kalamai duk kuwa da be furta mata cewar yana sonta ba, gaba daya sai ta manta da wata damuwa ta tattara rayuwarta da duk wani tunani nata ta maida a gurin Ameer cikin wuni daya ta canja kamar ba ita ba. Tunanin yadda zata yi da iyayenta idan ta kulla alakar soyayya da Ameer sam be zo mata a rai ba a lokacin saboda farinciki ya dauke mata hankali.
AMEER POV.
Yana isa gida wanka ne abun da ya fara yi, ya wanke sarewar tas sannan ya zo gaban madubi yana kallon yadda Allah ya tsara halittarsa da mazantaka aka jera masa six pack kamar shi yayi kansa.
“Yaushe na yi arha haka, i kiss Nimra i hold her hands”
Shi kansa ba zai iya fadan yadda kyamarsa ta boye kanta har ya iya Sumbanta Nimra kai tsaye ba, duk kuwa da yanayinta da jikinta be nuna bata kula da kanta ba and the most abun da ya ja hankalinsa fada masa cewar bata taba yin kiss ba, ya kuma yarda domin ya lura da yanayinta macen da bata taba kebewa da namiji ba tana da banbanci da wacce ta saba yi ko ta taba, ita ce mace ta biyu da yawun bakinsa ya taba kaiwa a bakin wata bayan Angel, ita ma kuma Angel ribantarsa ta yi da tsabtarta da kuma aske gashin kanta da tayi kamar yadda ya bukata bayan ta daukar masa alkawarin tsare kanta, shi kuma shaidan ya rinjaye shi har ya saka rike kansa, a duk lokacin da bukatar hakan ga taso masa baya cilastawa kansa hakura da abun da yake ganin yana da iko da halin yinsa akan me zai cutar da kansa then?
Ya tsuke baki, tunanin daukar fansa da son lalata rayuwar kanwar makiyinsa ya mantar da shi wani abu kyama, wata kila kuma ita din bata da kazanta shiyasa be ji hakan a lokacin da yayi unkurin karya tarbiyar da iyayenta suka bata. And this fitinanniyar yarinyar ta ja hannunsa har cikin kazamin gidansu be mata komai ba. Ya tuna irin kalaman da kakarta ta yi masa cewar ita marainiya ce kuma ta dogara da abun da take samu a gurin aikin ne. Ya dan tabe baki zai kyale ta ne kawai saboda Kakarta da ta durkusa har kasa tana rokonsa ba dan haka ba sai ya koreta saboda ta masa tsiwa shi kuma baya son haka ya lura tana da zafin zuciya kamar shi. Tawul ya nufa ya dauka ya daura ya fada kan gado ya ya dauki wayarsa ya kira Nimra sai da ya fara tambayar ya ta isa gida da lafiyarta, sannan ya dora da wasu kalaman da zasu kashe mata jiki kuma ta yarda son ta yake ko da be furta ba.
UMMI POV.
Tana tsaye da mamaki take kallon matar dake goye da yaro a bayanta tana ta fada da Waira.
“Idan kika raba wannan auren ki yi yaya da ni? Ga yaya? Akan min zaki zo ki ce zaki shiga tsakanin masoya, a wace hujjar?”
Ganin Waira na kuka ta kasa cewa komai ya saka Ummi ta nufi matar ta fara bata hakuri.
“Dan Allah ki yi hakuri baiwar Allah bata sani ba ne”
Sai ta juyo ta yi kan Ummi da masifar.
“Ta sani mana, idan ta gani sai ta nuna? Haka kawai zan kyale ta? Hauka ake yi? Auren shekara da shekaru zata ce a rusa a rana daya? To ba zan dauki wannan ba, ni ina son mijina, yayanmu hudu da shi, ke ba auren kike ba da kike son shiga tsakanina da shi na aureshi tun da dadewa dan haka babu wanda ya isa ya raba wannan auren, ke da ake son a kashe ma komai ta dade sai sun kashe ki”
Jin matsifar ta yi yawa ya saka Ummi ta sake kallon babbar macen da zata yi sa'arta ta ce.
“Wai wayen wannan mijin na ki Baiwar Allah da kike ta wannan masifar?”
“Gashi can...”
Ta nuna bayan Ummi a tsawace tana zaro ido tsabar masifa, Ummi ta juya ta ga waye mijin kenan ta farka a firgice sakamakon taba ta da Mahmood yayi.
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Ta fada tana mika sannan ta kalli Mahmood dake kallonta.
“Magana kike kina bachi lafiya?”
Juyawa ta yi ta karewa inda suke zaune kallo sai a yanzu ta yarda ba mafarki take ba, domin dan zaunawar da ta yi jiran a fito da Waira daga dakin hoto bachi mai nauyi ya dauke ta, kuma mafarki ya zo mata kamar a zahiri. Wacece wannan matar? Kuma waye mijin nata? Miyasa kuma take masifa da Waira shi ne abun da ya zo mata a rai.
“Are you okay ko kina jin wani ciwon ne?”
“Aa bana jin komai lafiyata kalau”
Ya sauke ajiyar zuciya domin ciwonta ne abun da ya fi damunsa a yanzu.
“Ummi har yanzu baki fada min yaushe ciwon nan ya sake ki ba, kuma me likitoci suka ce akai?”
Ta dubeshi.
“Ba nace wannan sirrinmu ba ne?”
“Ban fadawa kowa ba”
“Amman ka so ka yi maganar a gaban Namra ai, bana son kowa ya sani”
“Na ji, amman kina zuwa asibiti?”
“Na dade ban tafi ba, shakara biyu kenan da na gane cutar tana tare da ni”
“Amman Ummi kina shan magani? Kin san illar wannan cutar kuwa? Har kike cewa baki son kowa ya sani? Kin san abun da take janyowa”
“Likita ya min bayani, kuma yanzu zan duka da shan magani. Ina Waira?”
“Sun bata gado hoton ma daker ta yarda aka yi mata sai ihu take yarinyar bata da hankali”
Ummi ta mike tsaye tana tunanin mafarkin da ta yi wanda yayi kamanceceniya da abun da Waira ta yi a lokacin da ta so shiga dakin Maleek, suna tafiya Ummi ta juyo ta kalleshi.
“Kar dai ace aljana ta auri dan'uwanka Mahmood”
Mahmood ya girgiza kai.
“Haba Ummi wane irin aljana kuma? Yadda Maleek ya tsani mata har wata aljana ta samu damar aurensa?”
“Maybe ita ta saka mishi tsanar matan ai, wani mafarki na yi da ya ba ni tsoro...”
Jerawa suka yi suna tafiya tana labarta masa yadda ta yi mafarkin.
“Mafarki ba gaskiya ba ne, kawai dai dan kin saka abun a ranki ne ya saka kike yi mafarki, Ummi damuwata yanzu ciwonki ne yaushe zaki ga likitan? Kuma wane likitan ne yake dubaki, ba a wasa da ciwon nan”
“Sai na gama da matsalar Waira”
“And Ummi miye reason dinki na boye wannan sirrin ciwo ne fa”
“Bana son na tashi hankalin Babanku, kuma bana son hankalin Nimra da Namra ya tashi har da kai, dan dai Maleek na san ko ya rasa ni ba zai yi bakinciki ba”
Ta karasa a lokacin da Mahmood ya kai hannu ya tura kofar dakin da Waira take ciki.
“Maleek yana sonki Ummi, kawai dai wannan ciwon ne na kyamar mata ya saka shi nesantarki amman abun na masa ciwo, ya fada min haka kuma yace baya iya ayyana rayuwarsa idan babu ke, addu'a kawai ya kamata mu yi masa komai zai wuce”
“Kuma dole mu tashi masa tsaye, domin mafarkin nan da na yi jikina na bani kamar gaskiya ne in ba haka ba miyasa na ga Waira a mafarki har tana fadar wai kasheta za'ayi ban san ko suwa za su kashe ta ba”
Ummi ta zauna bakin gadon tana kallon fuskar Waira dake bachi.
“Akwai abun da yarinyar nan ta gani dazun tun da har gashi ta nuna”
Mahmood yayi shiru saboda baya son musawa Ummi. Ba shi kadai ba Abiey ma da ta labarta masa mafarkin a waya ta fada masa abun da ya faru be yarda ba.
“Mafarki ba gaskiya ba ne, kowa da yadda Allah yake halittarsa ku mata komai sai ku rika cewa aljannu ne, mun bincika abun nan a likitance an fada mana cewar halittace da Allah yake halittarsa kowa da irinsa”
Ta sauke ajiyar zuciya daman ta san ba lallai ne ya yarda ba.
“Hiayatee ki kwantar da hankalinki dan Allah komai zai wuce”
“Haka zamu saka masa ido ba tare da komai ba? Kullum sai dai ka ce min komai zai wuce when?”
Ta fashe masa da kuka kasancewar dakin babu kowa sai ita kadai da Waira dake bachi har lokacin, Mahmood tuni ya fice daga asibitin zuwa gurin aikinsa.
“Bari ki dawo sai mu zauna mu yi maganar abun da ya kamata, zamu saka ayi addu'a kuma muma zamu dage da yi har da sadaka idan ta kama har gurin dakin Allah sai aje ayi masa addu'a shikenan?”
“Eh amman da kullum baka yarda da zancena sai ka rika cewa komai zai wuce”
Daga can cikin wayar yayi dariyar manya, wadanda ke nishadi da matansu ya san halin sahibarsa tun kurciya na dawainiya da ita har zuwa yanzu da girma ya kama.
“Haba Madam yanzu ai na zubar da makaman yaki na ce za'ayi duk abun da kike so, kina asibitin har yanzu?”
“Eh ina son na tafi gida yanzu sai Hanne ta zo ta zauna da ita”
“Ya jikin nata? Likita ya fadi wani abu?”
“Sun duba komai a game da jinin idonta ba su ba mu sakamakon ba har yanzu, amman cizon dake hannunta sun ce da sauri tana da kyau jini, kuma likitan da ya duba da farko ya iya aiki shiyasa abun ya zo da sauki, sai dai yace duk da haka za su bata gado ta zauna har sai ta samu sauki gaba daya”
“Toh Allah ya biyaki, ita kuma ya bayyana mana iyayenta kuma ya shirya mana na mu yayan, ya nuna mana aurensu da yayansu a tare”
“Ameen... Abiey Ameen... Allah ya amsa....”
Ta amsa tana jin wani iri a zuciyarta, gani take kamar ba zata ga lokacin ba.
“Amman dan Allah ki saka ido akan yaran nan, bana son a samu wata matsala kuma ke ma ki kula min da kanki yawam tunani da damuwa ki ciresu kin fi kowa sanin yadda nake son farincikinki”
“Allah ya ba ni iko”
“Ameen, to sai na dawo?”
“A dawo lafiya Habibi”
“Allah ya sa”
Ya aje wayar, ita ma ta sauke wayar idonta na cika da kwalla, number Maleek ta lalubo ta danna kira ta saka hands-free. Ringing ďaya ya daga kamar yana jiran kiranta.
“Hello Ummi...”
Ya fada muryarsa har rawa take, sai da ta rumtse ido ta bude sanin uwa bata fushi da ďanta ta amsa masa.
“Na'am”
“I'm sorry ki yi hakuri da abun da ya faru bana nufin bata miki rai, ban san mi ya zo kaina ba kawai na samu kaina da bacin rai ne marar misaltuwa”
“Ba komai kana gida?”
“Aa na fita”
Ta yi shiru tana saurarensa sannan ta ce.
“Maleek ina son na tambaye ka, akwai mafarkin da kake ko kana ganin wani abun?”
Ta san it's not the right place ta yi masa tambayar, sai dai bata da zabin da ya wuce haka saboda baya zama da ita idan kuma ya dawo gida ba zai amsa mata tambayar ba.
“Ban fahimta ba”
“Baka mafarkin komai?”
“Ina mafarki kamar yadda kowa yake idan ya kwanta”
“Okay idan ka dawo za ku yi magana da Abiey”
“Okay amman kin hakura Ummi?”
“Ya zan yi Maleek uwa ai bata fushi da ƴaƴana na yi hakuri tun kana karami har ka girma, mi zai haka na ki hakuri akan abun da ka yi min? Ni dai ina son ka dage da azkar na safe da yamma, kuma idan zaka kwanta ma ka yi addu'a sannan ka roki Allah ya yaye maka wannan abun saboda yana damuna, bana son na mutu ban ga ka warke daga wannan damuwar ba Maleek, ciwon zai min yawa, idan zaka kwanta ka rika alwala kuma ka yi addu'a, sannan ka tsare karatun Qur'ane fiye da yadda kake yi, sannan ka rika daurewa ko da baka so kana zauna cikin kanenka da ni dan Allah duk abun da kake ji ka daure ka yaye abun a ranka idan ka ji abun ya taso maka ka nemi tsarin Allah”
“In Shaa Allah Ummi”
“Ka yi alkawari?”
“Na yi, ni ma abun yana damuna fiye da yadda yake damunki”
“Allah ya maka albarka, ya yaye maka ko minene?”
“Ameen na gode”
Ya amsa yana jin sanyi a ransa, ita ma sanyin ta ji domin daukar lokaci tana hira da ďanta Maleek ko da a waya ne zata iya kirgashi. Dawood ya dafa kafadarshi.
“This too shall pass Maleek In Shaa Allah, mu kan mu abun yana damun mu balle kuma mahaifiyarka da kai kanka dole ku damu, sai ka dage da addu'a nima kuma zan taya ka In Shaa Allah”
Maleek ya gyada masa kai, ya sauka daga kan motar da yake zaune ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi ya nufi wata almajira ya saka mata a robar baranta sannan ya dawo gurin motar suka yi sallama da Dawood....
*AFTER ONE YEAR.....*
*BAYAN SHEKARA ƊAYA....*
_Ku yi guessed abubuwa da da yawa🥰🙌_
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: *W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
26
Tsaye take ta jingina da karfen dake gabanta tana kallon harabar gidan, Mahmood na tsaye kusa da ita shi ma nasa hannayen suna jingine kamar nata. Daga ita har shi Maleek dake wasa da kallo suke kallo, farar singlet ce jikinsa sai short jean, da dukan kuzarinsa yake buga ball ya hada gumi sosai kamar mai yi tare da wasu team.
Kusan lokaci daya suka kalli Gate din gidan da aka bude manyan motor alfarma ta kunno kai harabar gidan.
Maleek ya tsayar da ball din da yake yana kallon motar data faka gabansa fuskarsa da murmushi. Wani kyakkyawan bakin saurayi ne ya fito gaban motar dayan kuma ya fito a gurin zaman driver, Maleek ya nufi wanda ya fito a driver seat da sauri ya mika masa hannu suka gaisa, Mahmood dake tsaye kusa da Waira kuma ya zagaya ta dayan side din ya koma dakin, ya sauka kasa gaba daya. Ummi dake falon tana gyara dankwalinta ta kalleshi tana murmushi.
“Sun iso