Showing 18001 words to 21000 words out of 281271 words

Chapter 7 - Wani Gari Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1191

CP bana son ka je gurin nan but it seems like dole sai ka je da alama yaron da ka taba shi ma dan masu gari ne”

“Me suke zargina da shi?”

“Wai cin mutumci da barazana akan rasa rayuwar wani, da wa ka yi fada Ameer? Na sha gargadinka akan abun da kake tun kana yi abu yana wucewa yanzu ya kai har a turo police a gidana da sunan ana son a tafi da ďana? Na so na kashe case din ba tare da kaje ba amman CP ya nuna min abun ba zai yiyu ba Ameer ina tsoron ka dauko rigimar da zata fi karfina na kasa cireka daga wata matsalar”

“Waye yayi karata ne Daddy? Shi nake son sani”

“Akwai yaron da ka saka yayi wani aiki a gurin da kuke shakatawa?”

Ameer na jin haka sai yayi murmushi abun da ya bawa mahaifinsa mamaki.

“Yeah akwai wanda na saka ya bawa wani abokin mu abu”

“Kamar ya? Ka yi min bayanin komai so that na san yadda zan bullowa lamarin”

Daddy ya bukata.

“Ya taba ni ne Daddy, kuma zan koya masa hankali nan gaba kadan”

“Me ka yi masa a yanzu?”

Ameer ya kalli mahaifinsa.

“Ba su fada maka ba?”

“Wata kila laifin yana da girma shiyasa CP be fada min ba yace min sai na zo”

Babu kunya babu tsoron Allah Ameer ya fadawa mahaifinsa abun da ya aikata da kuma wanda yake da kudirin aikatawa a gaba. Daddy ya mike tsaye yana kallon đansa cike da tsoro.

“Ameer yaushe ka lalace har haka? Ka kullawa abokinka Sherri saboda kawai ya watsa maka yawu a fuska? Bayan kai ka fara takalarsa?”

Ameer ya daga kai yana kallon mahaifinsa.

“Daddy sai ka rika daga hankalinka akan abun da be kai ya kawo ba”

“Ameer kana da hankali kuwa?Miye be kai ya kawo ba? Kokarin bata sunan abokinka ko kuma kallon tsabar idona ka fada min saboda ka tambayi friends dinka yarinyar ka ta zo ya hada ka da abokinka? Ko kuma abun da ka aikatawa abokinka?”

Momy ma kallon Daddyn take  tashin hankalin da ta gani a fuskarsa ya daga mata hankali sosai, ta dade ta sanin cewar Ameer yana gwada aron hannu sai dai ba damar ta fadawa mahaifinsa gudun kar ta hada su ko kuma yayi zaton tana yi ma ďansa sheri ne. Daddy ya nuna kansa.

“Kwarin idonka ya kai ka kalleni ka fada min cewar kana da budurwa sheke aya? Dukanin arzikin da na baka na nufin ka lalace ba, amman kullum sai ka saka ni ciwon zuciya, a kullum ina nuna maka abun da kake be dace ba amman ka kasa fahimtar hakan, tun kana dauko kanana har ka fara dauko mana magana”

Ameer ya mike tsaye yana kokarin danne bacin ransa.

“Daddy wannan abun da na aikata har ya kai ka fada min magana marar dadi kamar wannan? Simple abu? Ashe wani ba zai iya taba ni na gudu bayanka na buya ba”

“Zaka iya only idan kana sa gaskiya, bana son zalinci bana son cin mutunci da rainin wayo, ka wuce mu tafi gurin CP yanzu nan, kuma karka kuskura amsa cewar ka aikata laifin nan”

Daddy ya fada yana nuna shi da yatsa, domin ya san karamin halinsa ya amsa laifin a gaban kowa a kokarinsa na nunawa duniya cewar shi baya tsoron kowa ko kuma babu mai iya hukunta shi. Ameer ya kalli Daddy kamar yace wani abu sai kuma ya juya ya fice daga falon rai a bace. Motar da ya shigo ya sake shiga yayi mata key Daddy na jin karar tashin motar ya san ďansa ba zai bi umarninsa na zuwa inda ya bukata, wani kulikulin bakinciki ne ya taso masa har sai da ya fadi kan kujera zaune.

“Ba mu yi ma iyayenmu haka ba, kullum muna gudun bacin ransu, tarin dukiya da yawan gata be saka mun lalace ba”

Momy ta matso kusa da shi tana kokarin kwantar masa da hankali.

“Zamani ne ya zo, wasu abubuwan da baka tana ji ko gani ko zato ba za su faru, wani abun jarabawa ce dole sai ka yi hakuri zaka iya ci, dan Allah karka saka komai a ranka, shi ma na san anjima kadan zai sauka ya gane kuskurensa”

Daddy ya lumshe ido ba tare da yace komai ba.

“Yanzu ka samu kashe wannan wutar, da alama shi ma yaron da ya tsokano dan manya ne shiyasa har CP ya aiko maka da police har cikin gida, idan ba haka ba ba zaka san ma an kashe case din ba”

Ya amsa mata kai yana jin yadda zuciyarsa take masa mugun ciwon, irin ciwon da ta saba yi masa tun kamin ya samu Ameer.




A gurin da ya koyawa kansa zama ya nufa, ya isa gurin a lokacin da wata zuciyar ta jika da jiransa, gaban motar Nimra ya faka motarsa sannan ya fito motar ya nufo inda Nimra take jingine da motarta fuskarta ba yabo ba fallasa ba kamar yadda ya saba yi ganinta da far'a ba.
Tsaye yayi ya kasa ce mata komai, he need someone to talk to amman ba ya jin zai iya fara yi mata magana sai dai ita ta yi masa.

“Tun safe nake a nan”

Ta fada tana kallon harabar cikin wani yanayi da ya fi kama da na damuwa. A gogon hannunsa ya kalla 12pm da mintuna ya gani, ya saka hannayen nasa aljihu yana wani shan kamshi.

“Why?”

Ta kalleshi a karon farko.

“Daman na saba zama a nan, saboda guri ne da babu hayani sosai, kuma babu mutane da motoci idan kuka kake son yi zaka yi kuka babu mai ce maka domin me? Idan kuma nishadi zaka yi duk zaka iya yi a nan, na saba na kan zo wani lokacin da kawatau zauna a nan mu ci wani abu ko mu yi hira, kamar yadda ka tararda muna ci abincin a farkon zuwanka gurin nan”

Ya daga kai yana karewa gurin kallo.

“Mi ke damunki?”

“Ban sani ba, tsoron rasa mahaifiyata ne ko kuma damuwar da ďan'uwana ya shiga ne? Na matukar son family na, musamman mahaifiyarmu ko kadan bana son na ganta a cikin damuwa, damuwarta tana haifar min da tashin hankali, wani lokacin sai na rika jin kamar zan iya rasata idan na rasata ya zan rayu? Ummi tana yawam shiga damuwar da bata fadawa kowa, tashin hankalin da na gani a cikin idonta a jiya saboda yaya da kuma halin da yayana ya shiga ya saka na tashi ina jin wani yanayi na dabam”

A karon farko ya jingina jikin motarta ba tare da tunanin kar tufafinsa su kwashi datti ba kamar yadda ya saba jin tana cikin damuwa ya saka ta sa damuwar nisantar ruhinsa.

“Akwai ta inda zan iya taimakawa?”

Murmushi ta yi.

“No... Karka damu komai ya wuce a yanzu, fada min ya kare da abokinka?”

“Kamar baki cikin yanayin da ya kamata mu yi wannan hirar, but na yi nasara kuma ina daf da sake yin wata nasarar, but yau din ma an sake mata min saboda shi”

“Waya bata maka rai?”

“Daddy na”

“Karka damu da sannu zamu ga bayansa da yardar Allah, duk makiyin da ya saka mu gaba sai mun ga bayansa”

Ya daga mata gira

“Yeah...”

Tare da yin murmushi mai sauti kamar ba shi ba, ita ma ta yi murmushin tare da busar da numfashi.
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*


_Na Khadeeja Candy_


BARKA DA SALLAH
Allah ya maimaita mana ya karbi ibadun mu, Ameen.


7️⃣


MALEEK POV.

Maleek ya hade carpet din da yayi sallah da shi ya mike tsaye ya juyo ya kalli Mahaifiyarsa dake cikin shirinta na fita.

“Ummi da zaki taimaka ki fita a maganar nan, tsakanina da friends dina ne?”

“Friends...?”

Ummi ta tambaya tana matsowa kusa da shi da wani irin mugun kallo.

“Maleek har kana da karfin halin sake kiran mugayen mutanen nan friends dinka? Maleek kasan abun da abota take nufi? Abota na nufin mutanen da za su tsaya da kai a lokacin da kowa ya guje ka, ku fadi tashi ku tashi tare, ba mutumen da zai cutar da kai ko a hada kai da shi a cutar da kai ba, kamin na haife ka na yi wata ƙawa wanda na gudu da cikina na farko na tafi garinsu na boya, kuma ta bani mafaka a lokacin da nake tsananin bukatar mafakar, na ji ciwo na kwanta asibiti ta kwanta tare da ni da yi jinya ta har na samu sauki, idan na fada mata sirri na ce bana son kowa ya ji ba zata fada ba, wannan ake kira abota, ba mai cutar da kai ba...”

Cikin fada take masa maganar, sai ya jefar da carpet din saman gadonsa ya kalleta.

“Ummi kin taba haihuwa kamin ni?”

A take sai ta ji kamar ta kwancewa kanta zane a kasuwa, tsoron kalar amsar da zata bawa danta Maleek ya maye gurbin bacin ranta.

“Cikinka nake nufi.....”

Ta furta murya na rawa tare da dauke idonta daga barin kallonsa ta juya ta fice daga dakin. Iskar bakinsa ya juya fuskarsa gurin wayarsa dake ringing.

“Dawood”

Ya fada sannan ya karasa ya dauki wayar ya danna picking.

“Hello”

“Maleek ya ne kana lafiya”

Ya fada kansa

“Lfy Kalau for now”

“Muna tare da Abdull zamu zo gidanku yanzu nan”

“No karku zo yanzu, Ummi fada take zan kira ka later”

Be jira cewar Dawood ba ya sauke wayar ya nufo kofar dakin ya bude ya fito, tsaye yayi a stairs din yana kallon mahaifiyarsa dake zaune Namra na rumgume da ita tana kuka.

“Matsalata da ku karamin abu sai ku mayar da shi babba, miye abun kuka a nan kuma?”

Nimra dake tsaye rike da keys din da alamar shigowarta kenan ta watsa masa harara kamar wani sa'anta.

“Ba komai ba ne? A saka maka abun da zai iya zama sanadiyar lalacewar rayuwarka ko ma rasa ran gaba daya? Sannan ka ce ba komai ba ne? Ba laifinka ba ne mu muka da mu da kai”

Ta risina kusa da Ummi ta rika hannunta.

“Ummi dan Allah ki daina zubar da hawayenki a banza, ki daina damuwa da Maleek dan girman Allah, ta so mu je ciki”

Ummi ta mike tsaye Nimra na rike da hannunta ta juyo a hankali ta fara takawa, Maleek kuma ya fara saukowa tare da kawarda fuskarsa daga barin kallon kukan da mahaifiyarsa take yi. Hajiya ta lumshe ido ta hade yawu wannan karon ba kuka take na abun da aka yi ma Maleek ba, kukan marmarin danta Ameer take, ko a wane hali yake ciki a yanzu? Waya yake kula da shi a yanzu? Su waye abokansa? Wacece uwar rikonsa? Tana bashi kulawa kamar yadda danta yake samu? Har yanzu Mr Bashir yana kaunarsa kamar da ko kuma ya sauya? Yana ma raye ko ya mutu?

“Ummi...”

Kamar wacce ta farko daga dogon bachi haka ta bude ido da sauri ta kalli Nimra dake rike da ita, sai ta sake fashewa da kuka ta kwantar da kanta jikin Nimra.

“Ba zan taba zama lafiya ba Nimra, ba zan sake samun farinciki domin na siyar da shi da dadewa, shiyasa kullum da kalar kalubalen dake fuskantar yayana ko kuma ni”

“Ummi me kike fada haka ne? This too shall pass, ki daina saka kanki a damuwa please, idan kina saka damuwa a ranki muma sai ki saka mu shiga wani hali, muna bukatar rayuwarki Ummi”

Ta kalleta sai ta yi murmushi cikin hawaye, daf da zata kai hannu ta share hawayen Abiey ya shigo falon yana fada kamar zai tashin falon.

“Sai ga waye uban yaron nan a Abuja, sai na ga abun da yake takama da shi a garin nan, sai an daure min shi a ceil”

Ummi ta kara hanzarin kai hannu ta share hawayenta, karaso kusa da shi tana tambayar abun da ya faru, Maleek ma kallonsa yake kamar yadda Nimra ma take yi.

“Miya faru?”

“CP ne ya kira ni, wai yaron baya garin nan, amman mahaifin yaron ya bada hakuri, daga shi har yaron babu wanda ya je gurin, ni za a nuna isa? A taba min yaro kuma ace za a taka ni?”

Maleek yayi tabe baki abun mamaki ba ne idan aka ce Ameer yaki zuwa gurin, kadan daga cikin halinsa ne, kuma mahaifinsa zai goya masa baya akan haka.

“Indai wanda nake tunani ne, ba zai je ba daman, kuma baka bukatar yin komai akai Abiey mahaifinsa yana da kudi sosai, zai iya yin komai ya kare dansa, wannan wasan a tsakaninmu ne, dan Allah ka hakuri ka kyale ni da shi kawai”

“A tsakaninku? Wannan ya wuce a tsakaninku, komai Ubansa ya Mallaka sai na hukunta yaron nan, kuma kar na sake ganinka da abokan nan naka”

Ummi ta kalleshi kamar ta yi magana sai kuma ta yi shiru ta sauke ajiyar zuciya. Namra ta yi kwafa tace

“Wannan abun ya zama rainin hankali, danka ya aikata abu kuma ka kasa zuwa balle har ka tura shi ya bada hakuri, ta ina za ayi musu iyaka kenan? Kuma hakan ai zai bashi damar sake aikata wani abun a nan gaba”

“Na fadawa CP shi idan ba zai yi ba, zan saka DSS su kama shi, kuma sai na hukunta shi ko dan ya zama izina ga wasu”

Sam ran Maleek baya son abun da mahaifinsa Abiey yake kokarin aikatawa, sai dai be isa ya hana shi ba, ya san idan ya nuna mahaifinsa hakan zai bude wani sabon shafin fadan ne a tsakaninsu, domin Abiey baya wasa da abun da ya shafi iyalinsa, musamman yayansa a yanzu.


AMEER POV.

Rabuwarsu da Nimra da uku ya bude motarsa ya shiga, ba mutum ne ma'abocin yawo ba, duk kuwa da kasancewarsa tantari gurin zuwansa uku ne idan baya gida yana tare da abokansa idan baya can yana tare da falkarsa sai kuma a yanzu da ya samu wannan gurin zuwa da yake haduwa da Nimra. Gurin da suka saba zama da abokansa ya nufa sai ya samu gurin a rufe, abun da ba a taba ba.

“Miya faru?”

Ya tambayi kansa, kamin wani gefe na kwalkwalwarsa ya tuna masa da abun da ya faru..

“Oh...”

Ta tabe baki, ya juya motarsa ya ciro wayarsa number Tarig ya fara kira ta yi ringing har ta yanke be daga ba, a ka'ida baya kiran mutum sau biyu amman haka ya daure ya sake kiransa nan ma be daga ba, ya kira Dawood shi ma be daga ba, then Abdull ma yaki dagawa.

“Me yake faruwa?”

Ya tambayi kansa gabansa na faduwa, zuciyarsa na raya masa ba lafiya ba, domin be saba kiransu gaba daya ace kowa be daga ba, juya akalar motarsa yayi zuwa dayan gurin da suke hutawa, maybe zai samu wani a can, if not sai dai ya wuce gida domin a tsakaninsu babu mai iya zuwa gidan wasu neman wani. Ya isa a sa'a after faka motarsa da minti biyu ya fito ya shiga VIP din dake gurin, part din da suke zama ya nufa tun kamin ya karasa ya hango Abdull da Dawood zaune a gurin with serious face da alama wani abun suke tattaunawa. Kujera yaja ya zauna kamin ya ce komai Dawood ya fara mikewa tsaye Abdull ya bi masa baya suka fice daga gurin suka bar shi zaune da mamaki.

“What this mean?”

Ya tambaye kansa domin ransa be kawo masa komai ba, sai yanzu fushi suke da shi akan abun da ya faru? Or Maleek yayi masa wani sharin a gurinsu?

“It's because of....”

Sai kuma yayi shiru, a ganinsa ko da saboda abun da yayi ma Maleek ne be kamata su shigar da kansu ba, domin a tsakaninsa da Maleek ne, idan ba haka ba miyasa ba su yi ma Maleek haka ba a lokacin da ya watsa masa yawu a fuska? Be tabbatar abun da friends dinsa suka masa ya masa zafi ba sai da ya shiga motarsa yayi mata key, da wani irin karfi ya daki sitiyarin motar yana jin kamar ba a taba bata masa rai irin haka ba, domin be taba samun matsala da friends dinsa da ta kai ya zauna su tashi ba sai a wannan karon and all because of Maleek, bayan fadan da Daddy yayi masa.
  Wayarsa ce ta yi ringing da gangan yaki kallon gefen da wayar take ma balle har ya duba ya ga mai kiran balle kuma ya amsa, har ya isa bakin gate din gidansu be bi ta kan wayar ba, kamar zai tashi gidan haka ya danne horn har sai da Masu gadin gidan suka bude masa gate. Har gaban kofar Momy ya faka motarsa ya fito va tare da ya dauki wayar ba ya karasa gurin kofar falon, yana ganin yadda kanwarsa ta bude masa kofar falon tana jiran shigowarsa ya san wani yakin zai tarar a gidansu. Kallo daya yayi mata ya dauke kai ya shiga ciki, sai ya samu mahaifinsa a tsaye yana jiran shigowarsa. Kamar ya san nemansa Daddy yake sai ya karasa gurinsa ya tsaya ya kasa ce masa komai kamar yadda be yi sallama a farkon shigowarsa falon ba, daman can kuma ba al'adarsa ba ce sai dai ya kan gwada yi wani lokacin idan Daddy na gurin saboda ganin fuskarsa.

Tassss Daddy ya wanke masa fuska da mari mai kyau, har sai da Ameer ya hade hakoransa na sama da kasa ya dantse ya yarfar da fuska gefe ya rufe ido. Kamin ya bude idanuwansa sun hada wani karamin yaki da ya haifar da sauyawar launin kalar idonsa daga fari fes zuwa ja.

“For What Dad?”

Ya tambaya wasu jijiyoyin bacin rai da takaici na bayyana a goshinsa, a take Daddy ya sake marinsa a barin da ya mare shi dazun yana masa wani mugun kallo irin na fadan Uba da ďa, wannan karon Ameer be rufe idon ba, sai dai ya sake yarfar da fuskar ya kalli kasa, da wani irin tashin hankali Momy ta hade yawun bakinta, idon kanwarsa Humy kamar zai fito tsabar mamakin Daddy ya mari Ameer har sau biyu a lokaci daya. Ameer ya dago yana yi ma mahaifinsa wani kallo da be taba yi masa irinsa ba, kallo ne mai kama da harara irin na Ƴaƴan da suka gagari iyayensu, a take Daddy ya sake marinsa, cikin karfin hali Ameer ya sake dagowa nan ma Daddy ya sake sauke masa wani lafiyayyen marin, Momy na ganin hakan ta shiga tsakiyarsu ta tura Ameer baya tana kallon Daddy da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login