Showing 171001 words to 174000 words out of 281271 words
kwalla, be ce mata komai ba tun da suka shigo motar ita ma bata ce masa ba ko inda yake bata kalla ba, gashi ta dan bata fuska alamar fushi take, fushin da be san na minene ba. Rage wutar motar yayi ya faka gefen titi ya kashe motar yayi relaxing akan kujera yana kallon dayan gefen titin. Hakan ya saka ta juyo ta kalleshi sai ta ga ba ita yake kallo ba.
“Me yasa muka tsaya a nan?”
Ta tambaya a cikin wani yanayi mai kama da shagwaba da bata ma san tana yi ba. a juyo a hankali ya kalleta.
“Kuka na ga kina yi, shiyasa na tsaya har ki gama kukan, idan kuma bakin zon zuwa ne sai na maida ke, ni ban shirya tarbar wani karin bakincikin akan wanda nake ciki ba, bana son kukan kowa akaina a yanzu”
“Ba saboda kai nake kuka ba”
“Saboda wa?”
Ta yi shiru, sai ya kai hannu ya riko fuskarta ya juyo da ita yadda zata fuskance shi da kyau.
“Waira saboda na katse miki sarka ne? Ko saboda na yi magana da Maleek”
“Duka ne, ina son abun da Sulem ya ba ni, kuma ni bana son kana fada da Ya Maleek bana so ko kadan”
“Amman kina kallo a gaban idonki, shi ya fara fada min maganar banza, and ni bani da wani kuduri na lalataki ko rayuwarki, Allah ya sani ba ni da wani mummunar manufa akanki”
“Minene mummunar manufa?”
Ya kawar da kai.
“Manta kawai”
Sai kuma ya juyo ya kalleta.
“Zoben ki kuma zan siya miki wani bana son an sake ganinki da duk wani abun da ya shafi wani, bana son wata mu'amala tsakaninki da kowa, ba saboda Ummi kawai na dawo gidan nan ba, har saboda ke, so please don disappointed me”
Ita dai kallonsa kawai take ba dan ta fahimci mnufar zancensa ba.
“Amman Sulem shi ba a gidan yake ba, sau biyu kawai ya taba zuwa, kuma ya ba ni kyauta ne”
“Miye alakarki da shi?”
Ta yi shiru tana murza yatsun hannunta, so take ta tuna alakar dake tsakaninsa da ita.
“Shi ne wanda yake min sauki lokacin da ka barni a daji nan, shi yana so na baya min kamar yadda sauran mutanen suke min ba, kuma yana lalabani yana ba ni abubuwa kuma yana min magana mai dadi”
Ya sauke numfashi tare da kai hannu ya kunna motar.
“Ba dan'uwanki ba ne, baki da alaka da shi, Waira baki da alaka da kowa a yanzu sai ni”
“Kai ma ba dan'uwana ba ne!”
A wani irin dum maganar ta fado masa a kune ta fara rawa a kirjinsa. Ya dan karkato kamar zai kalleta sai kuma ya fasa ya cigaba da tukin motar.
“Ni ina son Sulem, Sulem ba ya min fada”
“Miye abun fada a cikin magana ta? Gaskiya na fada ai, waye silar zuwanki garin nan ba ni ba?”
“Amman ai a daji ka bar ni, baka taimaka min ba lokacin da maciji ya cije ni”
“That's was my mistakes, amman na taimake ki mana, na dauko ki saka ki a motar Nimra”
“Baka yi ba, Sulem ne yayi?”
“To a ina kika ga Sulem din?”
“Ni ban sani ba, amman shi na gani a gidan Hospital kuma shi ne yake min da sauki ba kamar saura ba”
“Shi fa likita ne kawai, amman ba shi yaje daji ya dauko ki ba, ke dai kawai kin farka kin ganki a asibiti ne, ya taimake ki ne saboda an ba shi kudi ba free yayi miki ba?”
“Ba a bashi kudi ba”
“Waya fada miki?”
“Na gani ai, babu wanda ya bashi kudi, kuma da iyayensa suka masa fada sai ya dauke ni ya kai ji wani gurin muka kwana a can, be bar ni ni kadai ba, kuma da masu bakin kaya police aka ce su kawo ni a nan be min fada ba, ni ina son shi”
Ya daki sitiyarin motar da karfi
“Haba Waira ina da fushi sosai, karki saka raina ya bace mana, don't make me angry, kar na fadi wata maganar da zata saka ranki ya bace har Maleek ya yi kwatance da haka”
“Toh ka daina min fada, gashi ka daki mota next ni zaka daka kamar Ya Maleek”
Ya amsa da sauri.
“God forbid ni ba zan taba dukanki ba, ba wannan ranar fada kuma na daina, zan siya miki sarka mai tsada sosai ki saka a wuyanki ba zobe ba, ba a saka zobe a wuya”
“Ni Sulem ya saka min ina so”
“Wannan Sulem din dan'iska ne”
Sai ta ji kamar ta fashe da kuka saboda ya zagi Sulem, ita duk mutanen da take kauna bata son a taɓa su.
‘Idan mutum yana kyautata miki shikenan ya zama masoyinki? Zan rufe idonki da kyautata har sai kin manta kowa a rayuwarki’
Ya saka a ransa sannan ya kalleta yana murmushin ya ce
“Yi hakuri, Sulem mutumen kirki ne, yanzu idan mun koma saka miki zobenki a wuya shikenan?”
Ta daga masa kai.
“Okay Smile”
Ta yi murmushin kadan, hakan kuma sai ya saukar masa da farinciki duk wani bacin rai da yake ya ji kamar an yaye masa shi
[7/17, 6:23 PM] My S Line: 56
Daddy yayi murmushi bayan ya gama sauraren hukuncin da Ameer ya yanke na zama a gidan Ummi for some days.
“Ka yi tunani mai kyau, kuma a yanzu na yarda ina ɗa mai hankali da sanin ya kamata, Allah ya maka albarka”
“Ameen”
Ya amsa sannan ya aje jaridar dake hannunsa ya mike tsaye.
“Idan dai akwai wani taimako da kake bukata zaka iya fada min”
Ya juyo ya kalli Daddy.
“Okay thank you Daddy”
“Your Welcome”
Daddy ya amsa masa da murmushi sannan ya daga masa hannu. Ameer ma murmushin yayi ya juya ya fice daga dakin. Falon Mummy ya shigo ga mamakin Waira ya samu zaune a kasa ta baje gashinta Fiyya na mata kitso kamar ba ita ba, Teema zai dariyarsu take, domin Waira son kitson take a gasken gasken, Fiyya kuma yawan gashin Waira ne ke burgeta yadda ya sha gyara ya sauko har gadon bayanta.
“Fiyya me kike”
“Kitso nake mata”
Murmushi yayi domin ya san shirme kawai za a tabka, Fiyya bata iya komai ba kawai dai tana son taba gashin ne. Ya zauna a kujerar dake fuskarta Waira ya kura mata ido ko kyabtawa babu, shi dai kam kallonta yana masa kyau matuka, ba ma kamar a yanzu da take ta far'ah kamar wani kitson arziki za'ayi mata.
“Is she your new girlfriend”
Ya dan juyo ya kalli Teema sai kuma ya juya ya kalli Waira da bata ma san ana yi ba, sai murmushi take tana taba gafen gashin da Fiyya take murdawa da sunan kitso, a rayuwarta ba a taba yi mata kitso ba, bata ma san wani abu kitso ba sai a kan su Ummi, abun ya burgeta amman bata taba sha'awar gwadawa a kanta ba, Ummi kuma bata damu da tace ayi mata ba, lura da yawan gashinta ba kowa zai iya mata kitso ba, kuma ba lallai ne ta yarda ba, domin zai iya mata zafi saboda abu ne da ba'a taba yi ba. Hakan ya saka ta maida hankali gurin gyara mata gashin kawai ba tare da kitsawa ba.
“Me ya saka ki tunanin budurwa ta ce”
Ya fada bayan ya dauke idonsa daga kallon da baya gundirarshi.
“Baka taba zuwa da wata mace a gidan nan ba, baka taba gabatar mana da wata ba, amman wannan kana shigowa sai ka cewa Mummy ga Waira suka gaisa, baka jira wani ya bata abinci ko abin sha ba, da kanka ka dauko mata lemu, ka nuna mata gurin da zata zauna, har kana fadar ta saki jikinta nan din ma gidansu ne”
Ya yi murmushi, sam be taba tunanin Teema ta lura da abun da be san ma yana yi ba.
“Kuma tana da kyau, da irin wayewar da nake tunanin idan mace bata yi ba, kamar ba zaka yarda ka kulata, kalli yadda ta shigo rigarta kadan ta wuce knees, bata rufe kai wata kila saboda yawan gashin kanta, ga ta fara har farinta ya fi naka kyau, idonta irin mai kyaun nan ne, bakinta da hancinta iya ita”
A karo na yi yayi murmushi yana kara bawa kansa abun da ya kusa zame masa dole, wato kallon Waira.
“Komai kin canka daidai, amman ba girlfriend dita ba ce, rashin saja mayafi kuma ya samo asali ne saboda addinita da al'adarta, ita din ba musulma ba ce”
Teema ta sauke wayar hannunta ya kara kallon Waira da mamaki.
“Ikon Allah kiristace?”
“Ban san wane kalar addini take ba tukuna, amman dai zan sani soon”
“Gaskiya da zan baka shawara ka dauka, zan ce karka bari wannan ta wuce ka, domin ta hada komai da duk wani namiji zai gani ya ji yana sonta, sai idan namijin nan wani kala ne mai neman wani abun dabam a jikin mace ba wannan ba, kuma zaku yi matukar dacewa da juna, yayanku za su yi kyau”
Yayi murmushi ya mike tsaye still yana kallon Waira kamar zai cinyeta.
“Waira na barki a nan naje na dawo?”
Ta fisge kanta ta mike tsaye da sauri tana girgiza masa kai alamar aa.
“Okay saka ribbon dinki mu tafi yanzu”
Ta dauki ribbon din ta saka sai gashin ya hade guri.
“Ba zaka barta har ka dawo anjima ba?”
“Ba nan zan kwana ba yau”
“Amman ai dare yayi already”
“Yeah gida zamu tafi”
“Idan kun ci abinci ko? ”
Mummy ta tari numfashinsa tana aje kulolin abinci dinning.
“Bata cin irin abun da muke ci, tea kawai take sha sai cake ko biscuits”
Waira ta daga masa kai tana murnushin jindadin be manta abun da ta fada masa tana ci ba.
“Akwai cake ai, zan dumama mata”
Mummy ta fada ita ma tana yi ma Waira kallon budurwar Ameer ne dan haka so take ta kyautata mata saboda shi. Fiyya ta ware hannayenta tana fadin.
“Mummy ina da cake dazun da Ya Ya aje ni gurin birthday Ikram ta raba mana cake da zamu dawo gida”
“Toh dauko mata ta ci bari na hada mata tea, zo nan ki zauna yata”
Mummy ta mika mata hannu, sai ta kalli Ameer har sai da yayi mata umarni da ta tafi sannan ta isa gurin Mummy, Mummy taja mata kujera ta zauna ta zauna.
“To kai Malam ka zo ka zauna, zata fi sakewa da jindadi”
Ba musu Ameer ya iso gurin ya ja kujera ya zauna.
“Mummy ba abun da kike tunani ba ne, not yet”
“Ni ka ji na ce wani abu? Ko kuma ka shiga zuciyata ka ga ina wani tunanin ne?”
Mummy ta fada da murmushi a fuskarta sannan ta juya ta shiga Kitchen. Ameer ya dauki plate ya zuba abinci ya saka spoon, ya dauki cup ta zuba lemu ya zuba ruwa. Ya fara cin abinci kenan Mummy ta fito da ruwan zafi a cup ta aje a gaban Waira.
“Teema tashi ki dauko mata kayan tea ta hada da kanta ban san wane kalar tea take so ba kar na mata ba daidai ba”
Fiyyata nufo gurin da zimmar zama Mummy ta yi mata alama da aa da ido, sai kawai ta zarce kitchen ta dauko plate ta zo dinning din ta zuba abincinta ta nufi hanyar dakin baki dake kasan benen, Teema ma tana gama jera mata kayan tea ta shige ita da Mummy aka bar Ameer daga shi sai Waira. Da kansa ya mike tsaye ya fara hada mata tea yana tambayarta me da me zai zuba, sai ta nuna masa idan ta shimshina ta ji kamshi be yi ba sai ta ce ya kara.
“Ba a shinshina abinci ba kyau”
“Saboda me?”
“Saboda zaki sakawa kanki cuta ne kawai, abun da za'a ci ba a shinshinawa, kuma ba a hurawa musulumci ya hana”
“Me yasa ake hana ku abubuwa da yawa? Haka Ummi take cewa ba a cin abinci da hagu”
“Yes duk wani abun da zai cutar da mutum addinin mu yana hana mu aikata shi, idan kuma kika ji ance ka aikata to a cikin aikatawar akwai lada da karin kariya ko lafiya da kuma natsuwa”
“Minene lada kuma”
Yayi murmushi ya koma mazauninsa ya zauna ya fara cin abincin.
“Lada wani abu ne da ba a gani a ido, amman ana iya fadarsa kuma wani abun kana ganin ribarsa tun a duniya, bari na baki misali da karatun da kike yi, idan kuka yi assignment ko test ba ana baku maki ba?”
Ta daga kai.
“Kina ganin makin?”
Ta girgiza kai.
“Amman da makin ake auna abun da kuka yi mai kyau ko? Kuma a soke inda kuka yi ba daidai ba, a gyara musu wani gurin ko kuma a nuna muku yadda ake yi right?”
Ta daga kai cike da gamsuwa.
“Toh haka yake ko a gurin Allah, yana saka mala'ikonsa su auna ayukan da mutum yake na lada, idan ya aikata alheri kuma yayi da yawa, sai Allah ya saka masa da aljanna, kuma tun a duniya Allah zai masa gata har zuwa kiyama”
Kalmar kiyama, da Lada da kuma aljanna a gurin Ameer ta fara jinsa, kuma kalmomin sun daure mata kai, bata san ma'anarsu ba.
“Minene Aljanna? Da Kiyama?”
Ya kai spoon din abinci a bakinsa, sannan ya sake debowa ya kai saitin bakin Waira, ta kalli abinci sai ta matsa da kanta baya.
“Ni ban taba ci ba”
“Toh ki gwada mana, akwai dadi sosai it's high time ace baki fara dandana abincin garinmu ba, ya kamata ki iya ci saboda zaki cigaba da zama da mu ne fa, ni idan na je garinku ba zan kyamace kalar na ku abincin ba, zan ci komai aka ba ni”
Ta yi dariya.
“Ba zaka iya zuwa garinmu ba ai”
“Zan iya, kuma zan je na miki wannan alkawarin, zan je tare da ke ko kuma ni kadai, zan roki su yafe miki kuma su barki ki zauna a tare da mu”
A take yanayin fuskarta ya sauya.
“Za su iya kasheka”
Yayi murmushi ya kara matsar da spoon din bakinta.
“Bude baki”
Ta bude kadan sai ya saka hannunsa ya bude mata bakin ya zuba mata abincin a hankali.
“Tauna”
Ta fara taunawa tana yamutsa fuska, domin duk abun da baka saba da shi ba, zaka ji shi babu dadi kamin ka saba.
“Zan iya yin amai”
“No ba zaki yi ba”
Taunawa take tana jin zakin abincin har cikin kanta yana sarrafa kwakwalwarta.
“Bari mu koma gurin tambayar da kika min, kin ce minene kiyama da aljanna ko? Kiyama wani guri ne da Allah yake tara dukannin bayinsa musulmai da kafirar, bayan sun mutu sai ya sake tayar da su, su yi tsayuwa na jiran sakamakon abun da suka aikata kamin ganin makoma, kusan zan iya c miki guri ne na interview idan aka ga aikinka na kwarai ne za a baka sakamakon abun da ka aikata, idan kuma ka yi mummuna nan ma za a baka sakamakonka, sannan a tura yan wuta cikin wuta, yan Aljanna kuma cikin aljanna, kuma akwai wadanda sai an konasu a wuta sannan za a saka su a Aljanna. Aljanna ma wani guri ne da ya ninka duniya dadi da kyau da farinciki, akwai gulbin zuma da na giya da na madara, duk wani abun da kike so akwai a Aljanna, talaka a aljanna shi ne wanda yake da gida kamar girman duniyar nan”
Ta zaro ido tana mamaki.
“Daman bayan mutuwa ana sake tashin mutane?”
Ya sake kai mata spoon din abincin a bakinta.
“Kwarai da gaske, a addininku ba a fada muku ana sake tashi ba?”
“Aa a addininmu ba a sake tashi idan an mutu”
“Ba gaskiya ba ne, idan ba a tashi to taya zaka kwatarwar wanda aka zalunta hakkinsa? Ta iya za a saka maka da abun da ka aikata na alheri? Mutanen da suke zaluntar ka ta ina saka musu da abun da suka yi? Ibadar da muke a kullum ko a wata ko a shekara ta ina za mu sakamakonta?”
A nan ya yi nasarar dasa mata wani tunanin, domin a can da bata yi tunanin idan wani ya zalince ka ba za a sake tashinsa a kwatar maka hakkinka.
“Ai tun da can da ke kinsan babu ki, aka hallince ki, to ko kin san zaki mutu kuma dole zaki jira sakamakon abun da kika aikata”
“Mu sau daya muke bauta a shekara”
Ta fada tana sake bude baki ya zuba mata shimkafar da cinta ya zame mata kamar dole.
“Kin ga mu kuma kullum muke ibada, sallah sau biyar a rana, ta wajibi kenan, ban da ta nafila, ga sadaka ga kyautatawa, a cikin ibadu azumi da hajji ne kawai ake yi shekara shekara, shi ma akwai na nafila da zaka iya yi a wata ko a wasu ranaku da aka kebe mana, ga kuma karatun Qur'anen da Annabinmu ya kawo mana”
“Wanene Annabinku? Minene Qur'ane?”
“Karatu mai tsayi sosai, amman dai zaki san komai tun da muna tare a yanzu”
“Ina son na sani, addininku yana da abubuwa da yawa”
“Sosai ma kuwa”
Ya fada yana jan karan hancinta, sai ta yi dariya ta saka hannu biyu ta dauki tea ta sha. Kamin ya dago kanta ta kalli Ameer da ya mike tsaye yana shafa kanta.
“Kin ga a addininmu ba a yarda mace ta bar jikinta a bude ba, ko da kuwa gashin kanta ne, ana son ta bayyana adonta ne kawai ga mijinta”
“Saboda me?”
“Idan kika je siyen minti a shago da wanda aka rufe a cikin leda da wanda aka bari kuda ya taba yayi datti wane zaki zaba?”
“Wanda aka rufe”
“Toh haka mace take, tashi mu tafi”
Ta mike tsaye, sai ya haura sama ya sanarwa Mummy zata tafi, sai gata ta sauko da ledar turare kusan kala hudu ta bawa Waira.
“Ga wannan, kin san mace yar kamshi ce”
A nan ma Waira bata karba ba sai da ta kalli Ameer yayi mata alama da ta karba sannan ta karba ta wuce gaba.
“Allah ya sanya alheri”
Ameer ya bude ido yana murmushi.
“Mummy baki yarda ba kenan”
Kamin Mummy tace wani abu Fiyya ta fito da mayafinta.
“Zan bika mu tafi na ga gidan”
“Wa zai dawo da ke?”
“Yeah daman ina son naje da motata kuma gashi na zo da motar Ummi, so kija min motata zan shiga ta Ummi sai muje ki ga gidan, in ya so direba sai ya dawo da ita”
“Okay”
“Yeeeee Mummy sai na dawo”
Fiyya ta yi gaba abunta. Sai da Ameer ya shiga dakinsa ya dauko key din motar sannan ya fito ya bata key din shi kuma ya shiga motar Ummi. Waira ta juya