Showing 138001 words to 141000 words out of 281271 words
mahaifin Ameer ba ne.
“Ameer”
Daf da zai fice Daddy ya kira shi, sai ya tsaya cak sannan ya juyo ya kalleshi.
“Zo nan”
Ame
“Daddy boye min gaskiya zai kara jefani a cikin wani hali ne kawai, miyasa baka fada min sunan mahaifiyata ba even for once? Baka fada min garin da take ba? Baka nuna min yan'uwanta ba? Baka taba bani labarin dalilin rabuwarka da Ammy ba, baka fada min dalilin da ya saka Ammy take kauna har yanzu ba duk kuwa da kasancewar ta rabu da kai, babu ta inda nake kama da kai, bana kama da danginka, baka taba bani labarin mahaifiyata ba, yanzu kuma kai tsaye ka fadi sunanta, me zai kasa ka boye min gaskiya? Why?”
“Saboda ba gaskiya ba ne, Ameer ni mahaifinka ne? Baka da wani uba sai ni...”
“Wata kila zaka fada min gaskiya a lokacin da gaskiyar ba zata amfanin komai ba, sai dai ka tsaya a gaban gawata kama zubar da hawayen nadamar boyen da kake kokarin yi, Daddy kai da kake ďa kamar ni mai saka ka cikin tashin hankali da fitina da faduwar gaba da ciwon kirji, kake tsoron fada min gaskiya saboda karka rasa ni? Ina ga ni da nake da uba kamar kai? Na san gaskiya Ammy ta fada min amman ina tsoron gaskiyar saboda rasa ka Daddy”
Daddy ya fadi zaune kan kujera idon na sauya launi.
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, Ameer don't force me to do this please”
“Amsa kawai nake so daga bakinka gaskiya suka fada ko ba gaskiya ba?”
Daddy ya mike tsaye a daidai lokacin da hawaye suka sauko masa ya nufi gurin windows din dakinsa ya tsaya ya rungume hannayensa ta baya yana kallon harabar gidan.
“A kowane dare da wuninsa, ina rayuwa a cikinsa da fargabar halin da zaka tsinci kanka idan irin wannan labarin ya zo maka, wannan tunanin yana haifar min da tsoro da bakinciki, sai dai ban saka tsammanin zuwan hakan a yanzu ba? Domin ban yi tsammanin na karya daya daga cikin alkawuran da na daukarwa Zahra ba, ta mallaka min kai bayan na mata alkawarin kula da kai fiye da yadda zata iya, na mata alkawarin baka tarbiya da ilmi, na mata alkawarin baka gata da duk wani kalar jindadin duniya, ban kuma yi tunani a akwai inda na gaza ba, sai dai abun da na gagara ganewa a yanzu shi ne, me zai saka ta saka min da wannan? Me zai saka ta daga min da tsohon ciwon da na yi zaton na warke shi? Akan wani dalili zata tambayi ni ajiyar da ce ta kyautarda zuciya daya?”
Ameer ya tako cikin dakin ya iso gurin Daddy ya rumgume ya fashe da kuka, Daddy ma kuka yake ya kasa juyowa kuma ya kasa barin kukan nasa ya fitarda sauti.
“A kowane dare ina bachi da bakincikin rashin haihu, sai dai saboda son kwanciyar hankalin Jamila a wacan lokacin na kan boye abun na barwa raina, daga lokacin da ta gabatar min da kai a matsayin ďa sai na ji kamar ba ni da sauran kunci a duniyar nan, bayan bayyanar gaskiya sai sonka ya karu, a lokacin ba ni da mafitar da ta wuce na mallaka ka ga mahaifiyarka, duk kuwa da irin kaunar da nake maka saboda na san ta fini bukatarka, domin ita dole ce ta saka ta rabuwa da kai, sai dai bana tunanin dole ce ta saka ta kyautar da kai a gareni, domin ban cilasta mata ba, ban kuma san wani ya cilasta mata ba, sai dai ina kallon abin a matsayin kyautar daban zata ba daga Allah, rahma Allah ce yayi min kyautarka, kuma tun daga lokacin da Zahra ta tabbatar min da kai a matsayin ďa, sai bakincikina ya yaye farinciki ya ninku, musamnan da na sake aure na haifi yaya mata, sai an fahimci hikimar Allah na bani kai kyauta da yayi. A yanzu ma ban san manufar sa, wata kila akwai abun da yake shirya mana, sai dai ina jin kamar ba zan iya jure kallonka a wannan halin ba, saboda ina matukar kaunarka, taso da wannan maganar da Zahra ta yi zata haifar min da damuwar da bata da magani”
Ameer ya sake shi ya fadi kasa ya fashe da kuka, gaskiyar da yake son sani ya santa amman ta haifar masa da karin bakinciki, damuwa da kunci suka bude masa sabon shafi, gaba daya komai ya zame masa ka rubutun littafi, wani abun kuma kamar mafarki. A cikin wuni daya duniyarsa ta juye, rayuwarsa ta sauya, mutanen da yake kallo a matsayin iyayen sun tashi daga iyayensa, wadanda be sani ba be taba mafarkin rayuwa da su ba, su ne iyayensa ta ina zai fara? Kiran wasu da suna da iyayensa? Da girmansa?e yasa wannan abun be same shi a lokacin da yake da kurciya ba? Sai yanzu da girmansa? Har ya mike tsaye ya juya ya fice daga dakin Daddy be juyo ba, Stairs ya sauko be kula da wadanda suke falon ba ya fice zuwa gurin motarsa. Ya shiga yayi mata key yayi reverse, kamin ya isa gate masu aikin kula da gate din sun bude masa. Sai da ya hau titi tunanin ina zai je ya zo masa? Wa zai fuskanta ya fadawa damuwarsa? Damuwace da ba a magani balle a magance masa this is reality. Tafiya mai nisa yayi sannan ya isa unguwar su Humaira, domin zuciyarsa bata raya masa ya je ko'ina ba sai can. Yana shiga unguwar ana kiran sallah Isha'i immediately yayi parking daidai inda Masallacin yake ya fito rike da ruwa ya wanke fuskarsa ya kuskure bakinsa sannan ya rufe motar ya nufi Mallasacin. Second time kenan da yayi sallah a cikin jam'i kafadarsa na taba ta wasu mutanen da be san inda suka fito ba. After gama Sallah ya sake daga hannunsa sai kuma ya rasa addu'ar da zai yi. Sai mikewa yayi tsaye ya fito daga Masallacin ya dawo ta saitin inda gidansu Humairah yake ya tsaya yana ta kallon corner.
Ya dade a haka sannan ya samu wanda ya aika ya fada masa sunanta kuma yayi masa kwatancen gidansu da taba shiga da shi, matashin saurayin ya ce ya gane ta. Takowa yayi ya dawo gurin motarsa ya jingina. Almost 30min sannan ya hango Humaira ta fito, kallonta yake har ta iso inda yake, hakan nan kawai ya ji kamar ya rumgume ta domin yana a cikin damuwar da yake bukatar hug, sai dai ya san Humaira bata cikin irin matan da zai yi ma wannan matukar yana son su kwashe lafiya.
“I thought na ce na aje aiki a gurinku? Miye na sallamo min kuma? Da na san kai ne Wallahi da ba zan fito ba”
Ya dauke idonsa daga barin kallonta ya kalli wani gurin dabam tare da rumgume hannayensa.
“Damuwata ta wuce ta kamfani ko wani gurin aiki, Humaira ban san inda zan je ba, na bata da yawa daga abokaina, some of them ma idan ma fada musu kallon marar hankali zasu min, bana ma son su sani, ban san me zan yi ba, na rufe kaina a daki na yi kuka kamar jariri ko na fito waje na yi ta ihu? Ko kuma na je gurin mutanen da ban sani ba, wadanda suka kira kansu a matsayin iyayena na yi fada da su? Or should I just died?”
Kalamsa sun sanya jikinta sanyi, domin a cikin lafazi mai rauni da neman mafita yake maganar. A wani yanayi na tsoron hantararsa da fadansa ta dago wayarta ta haska fuskarsa. Hawayen da ta gani a fuskarsa ya matukar daga mata hankali, domin duk wani abun da zai iya saka Ameer din data sani kuka to ita zai iya ma kasheta wata kila.
“Me ya faru Ameer?”
“I just need someone to talk to kuma na zo nan na ji kamar bana son magana akan damuwar anymore, I'm sorry for bothering you”
“No... No... No please don't, you need me just tell me me ke damunka?”
Ya sauke kai kasa.
“I'm so weak”
Ya juya ta bude masa motar.
“Shiga ka zauna”
Ya taka ya zauna cikin motar sai ta kwantar masa da seat din, ta rufe motar ta zagaya dayan side din ta shiga ta zauna ta bar nata bangaren a bude saboda idon mutane.
“Do you want water?”
Ya girgiza mata kai, sai ta kalli ruwan dake cikin motar.
“I'm sorry akwai ma ruwa a motar, to zaka ci wani abu?”
Ya girgirza mata kai.
“Ko kana son wani abu? Kana son zuwa wani gurin? Ko kana son shan magani?”
Murmushi ne ya zo masa a lokacin da be yi zato ba, domin ya fahimci so take ta dauke masa damuwa kuma bata san ta inda zata fara ba. Ya juyo yana kallonta sai ta wayarsa ta yi ringing, ya dago wayar yana dubawa sai number Ummi ya gani be hadace number ba amman ya fahimci number ta ne tun a lokacin da ya saka number daga wayar Nimra zuwa wayarsa. Rejected call din yayi a take mood dinsa ya canja.
“Na san bama shiri da juna, and ka tsane ni na sani, amman ganinka a cikin halin ya haifar min da damuwa a yanzu, please fada min meke damunka?”
“Humairah how would you feel idan wata uwar ta fito a matsayin mahaifiyarki, ta ce matar da kike kallon a yanzu ba mahaifiyarki ba ce ita ce mahaifiyarki, and mahaifinki da a kullum kike masa addu'a saboda ya rasu sai wani ya fito yace miki yana raye, yana can wata duniyar yana rayuwa da wasu iyalan da ya fi kauna fiye da ke, ke kuma ya barki duk da yasan shi mahaifinki ne be damu ya baki kulawa da kaunar da kike bukata, and abun da ya fi komai ciwo ya ce kyautar da ke yayi, kuma ya san kina raye amman ya ki baki kulawa saboda baya kaunarki, sai daga wasu kike samu kulawa da kauna, kuma saboda ya rusa farincikinki sai ya fito da rana tsaka ya rusa mafarkinki...”
Humairah ta yi fuskar mamaki jin wani abun banbara gwai, tana kokarin fahimtar hanyar da yake dorata, kamin ta zaro ido ta rufe baki da sauri tana kallonsa...
UMMI's POV.
Cikin rauni da fargabar zai dauko ko ba zai dauka ba ta zabura a lokacin da yanke kiran nata. Sai ta hade yawu da karfi ta zauna bakin gadonta, daman dai she wanted to know halin da yake ciki domin ta fahimci yana da saurin fushi da zuciya, kar ya jefa kansa a wani hali. Sakon kar ta kwana ta aika masa sannan ta aje wayar ta mike tsaye sai ga kira ya shigo, da sauri ta dawo ta dauki wayar a zatonta Ameer din ne ya kirata sai ta ga Namra. Lumshe ido ta yi ta sauke ajiyar zuciya sannan ta amsa kiran.
“Assalamu Alaikum Namra....”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Shi ne ya biyo bayan sallamar da Ummi ta yi wayar dake kunneta ta subuce ta fadi kasa...
[7/2, 9:43 PM] My S Line: 46
Labarin da Mahmood ya bashi ya zama masa wani sabon lamari a cikin kai da be taba mafarkin faruwarsa ba. A tunaninsa Mahmood zai fada masa cewar Ummi tana dauke da cutar cancer su tattauna akan cutar, amman sai ya fada masa wani labarin na dabam da fi karfin tunaninsa ya firgita kwakwalwarsa.
“Ya za'ayi na yarda da wannan? Ummi bata taba auren wani kamin Abiey ba, da ma Abiey ka ce sai na ce yes saboda Mahaifiyarsu Namra, amman Ummi bata taba aure ba, kuma bana tunanin zata samu ďan ta hanyar da be dace ba, idan ma gaskiya ba ne me zai saka ta ta boye tsawon shekarun nan bata bayyana ma kowa ba? Kuma ko sau daya bata taba nuna cewar Ameer ďanta ba ne? Maybe dai Ameer ya shirya duk wannan ne?”
Mahmood ya kalleshi.
“Da wa zai shirya? Ummi zai hada kai da ita ta fadi karya saboda me? Kuma ba shi ya fada ba ita ta fada in her own mouth, babu wanda ya matse ta, shi kasan a yanayin yadda ya bar gidan bana tsammanin zai yarda domin daukar yake ma bata cikin hayyacinta”
“Taya wai Ameer zai zama ďan'uwan mu? Not just dan'uwa ma ace dan Ummi ne wai ita ta haife shi da kanta? Ai kai ma kasan ba zai yiyu ba, wannan ba abun da hankali zai kama ba ne”
“Then ask her”
“Baka ganin halin da take ciki? Ba ta a halin da ya kamata ayi mata wannan maganar, amman ai dole gaskiya zai fito saboda Abiey ba zai dauka ba”
“Yanzu baka fahimci labarin da na gama baka ba, kenan? Abiey ma ya san da wannan, shi da kansa ya zo yayi mata fada akan me yasa ta fadi wannan abun sai gashi na gabatar masa da ciwonta a dole ya bar zancen”
“Amman taya Ummi zata haifi da ace bata bashi kulawa ba kuma be girma a tare da mu ba, ko sau daya bata taba fada mana labarinsa ba? Kuma shi Ameer mutanen da yake kallon a matsayin iyayensa ya alakarsu take da su kenan? Taya ma duk haka ta faru idan ma da gaske ne? Kuma shi Ameer ya san da haka ko kuma yaya? Kuma ďan ma na waye? Na mahaifinmu ne ko na wani”
“Nima ina son na sani sosai, sai dai bana son mu zurfafa tunani kar mu tunanin abun da be kamata ba, mu jira kawai mu ji ta bakinta zai fi, for now dai dole zata fada mana tun da gaskiyar ta bayyana”
Maleek ya gyada kai mamakin ya cika kansa har ya rasa ta ina zai fara tunani, abun sam be kama kanshi ba.
“If ma da gaske ne miyasa Ummi bata fada ba lokacin da muka samu matsala da shi? Karka manta fa har fada ta rika yi saboda ba a kama wanda yayi min aika aikar ba”
Maleek ya fada yana ciro wayar dake aljihunsa ya duba kiran Namra, he pick up the call ya kara a kunnensa kukan da ya ji tana rerawa har ya hana maganarta fita shi ya fara daga masa hankali.
“Namra are you alright?”
“Ciw...ciwo... Ciwon... Nimra ya tashi and.... She... Couldn't survive.... ”
“What do you mean?”
Ya tambaya da karfi. Sai ta amsa masa da ihu tana fashe da wani kalar kuka mai karfin gaske
“We lost her...”
“Innalillahi
Innalillahi
Innalillahi.... Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Haka ya rika furtawa sai a karshen ya samu hada kalmomin gaban dayansu, ya mike tsaye rike da wayar try to control himself.
“Lafiya?”
Mahmood ya tambaya shi ma yana mikewa tsaye ganin hankalin ďan'uwansa a tashe.
“Nimra ce we lost her...”
Maleek ya fada hawaye na zubo masa. Mahmood ya duke da sauri a gurin yana buga hannayensa a teburin dake gabansu har sai da hankalin mutane ya dawo kansu. Maleek ya yi following call din Namra amman bata daga ba ya sake kira bata daga ba sai ya nufi Waiters ya biya kudin ruwan da aka kawo musu ya fice da gudu, ya saka key din motarsa kusa da sau uku sannan ya shiga daidai ya shiga motar ya murza key da irin sifar da be taba tashin mota a haka ba. Kamar ya sato motar haka yake tukin yana ratsa motoci har ya iso gida, be tsaya danna horn asan da zuwansa har a bude masa gate ba a wajem gate din ya bar motar ya fito da gudu ya bar motar a kunne ya tura karamar kofar gate din da karfi, jin ta a rufe ya buga mai gadin ya bude masa, kamar an korasho haka ya shigo cikin gidan da gudu su kansu ma'aikatan gidan sai da suka tsorata, ta gudu ya shiga falon kitchen ya fara nufa ya leka sai ya tararda Hanne a ciki da Yesmin suna hira suna aiki, ya fito da gudu ya haura stairs din kamar zai zame, ta tura kofar dakin Ummi da sauri ya shiga.
“Ina wayarki Ummi ara min zan kira wani?”
Ummi ta juyo ta kalleshi hawaye na kwaranya a idonta.
“Mun rasa Nimra ko ba haka ba?”
Tsaye yayi cak ya rasa me zai ce mata eh haka ne, ko kuma aa ba haka ba ne? Tausayinta ya zame masa biyu. Daker ya cira kafarsa ya isa gurin da take tsaye ya rumgume mahaifiyarsa abun da be sani ba shi ma hawayen yake kamar ita, sai dai shi yana kokarin ya fita karfin hali ne saboda ta samu kwarin guiwa kar ita ma su rasa ta daman ba lafiya ce ya wadece ba.
“Ki yi hakuri Ummi mutuwa bata da magani”
Sai ta dago kamar jira take ta bashi amsa tana hakki tana kuka
“Haka ne Maleek, mutuwa bata da magani, na rasa mijina na farko a lokacin da nake da kurciya, na rasa mahaifina tun kamin girmana na rasa mahaifiyata a lokacin da girma ya fara kamani, yanzu kuma na rasa yata, bana fatar na sake rasa kowa kuma.. Bana fatar na sake ganin gawar kowa”
Ya saka hannayensa ya rike fuska yana kuka naman fuskarsa na rawa.
“Mu kuma ba ma fatar ganin gawarki Ummi, ba ku fata kar Allah ya nuna mana wannan ranar”
Ya maida ita kirjinsa ya rumgume ita kuka shi kuka aka rasa mai rarrashin wani....
“Ummi...”
Muryar Waira ta saka suka juyo gaba dayansu suka kalleta tana tsaye bakin kofa kanta ba dankwali kamar kullum sai kallonsa take idonta a waje daman can sarki tsoro ce balle ta ga suna kuka. Maleek ya saki Ummi ya saka gefen rigarsa ya share hawayensa ya nufo kofar da Waira take tsaye da niyar ficewa sai suka jiyo karar Yesmin dake kitchen hakan yayi daidai da tsayawar motar Jabir, Umar daki daki ma ya fito da gudu domin Namra ta rike kowa kira take tana fada masa yar'uwarta ta mutu har da wadanda be kamata ta kira ba. Kan kace kwabo gidan ya karade da kuka kana ji kasan an rasa rayuwa mai tsada, Waira ta gudu a inda ta saba boya ta boye tana kuka sosai kamar ranta zai fita, domin tana matukar son Nimra, Ummi da Nimra su ne mutane da ta fi kauna bayan Shuraim da Eid..
Wani tashin hankali be bayyana ba sai da aka iso da gawarta a falon Ummi, gata kwance cikin karaga an daure babban dan yatsan kafarta da dan'uwansa, an daure hannunta ba ta