Showing 81001 words to 84000 words out of 281271 words
take. Nazarinsu ne be gama yi ba.
“Babe..”
Nimra ta fada bayan ta sauke wayar cike da zumudi. Ya dauke idonsa daga barin kallon Humaira dake goge desk tana ta rera wakar har dan kada kai.
“Uh.. -hmm”
“Yayar Babanmu ce ya zo, kuma Ummi tace tana ta tambaya ya kamata na tafi kamin a sake kirana”
Ya murza yatsun hannunta dake cikin nashi.
“Tun yanzu? Ba mu dade da shigo gurin nan ba”
“Amman mun dade a can ai, kuma ka ga na yi karya tun safe fa na fito gida”
“Ai ba gajiya nake da ganinki ba”
“Na sani, ai gobe da jibi na nan ko?”
“Yeah, shiyasa nake son gidanku a san da ni amman kin ki yarda”
“Ba yanzu ba”
“Sai yaushe? Kullum cewa kike ba yanzu ba, to sai yaushe?”
“Sai nan gaba, komai yana son natsuwa Ameer ka san yadda iyayena suke, ba kamar sauran iyayen bane nawa suna da tsauri dole sai mun bi a hankali”
Ya daga mata kai tare da kai hannu ta shafa fuskarta.
“Okay zan jira har zuwa lokacin da kika samu natsuwar gabatar da ni”
Humaira dake gefe ta taba baki ba dan tana jin abun da suke fada ba, sai dan taba Nimra da ta hango yana yi, tana jin tsigar jikinta na tashi, da ace ita ce ta tabawa fuska da yanzu ta dauke shi da mari saboda yadda take jin haushinsa balle kuma ota bata daukar wannan iskancin na namiji ya taba jikinta. Ta cigaba da rare wakarta ta nufo inda suke ta kwashe kayan kawo musu ganin sun mike tsaye.
“Idan ka biye ta kan saurayi, sai ya kai ka ya baro, Samarin yanzu yan shan minti ne, yar'uwa ki yi hankali 🎶 Duniya budurwar wawa yarinya ki yi hattara... 🎶 iyeee yaraye nanaye Humaira.... 🎶”
A nan ma sai da Ameer ya dan saurari wakar, Nimra kam duk zuwan da suke bata taba kula da abun da Humaira take ba... Sai da suka nufo hanyar fita daga gurin sannan ta janye hannunta daga rikon da yayi mata ta gyara zaman mask din dake fuskarta, shi ya fara shiga sannan ta bude ya shiga yayi motar key, a hankali yake tuka motar har suka isa gidansa ya danna horn mai gadi ya bude masa ya shiga da motar, a da can idan ta shigo gidan tsoro take ji saboda bata saba ba, sai ta rika ganin kamar wani zai ganta, gashi daman bata saba zuwa dakin saurayi ba, yanzu kuwa Ameer ya bude mata ido, domin basa da gurin hira sai a nan kadai saboda bata son yan gidansu su san tana soyayya da Ameer, bata shiryawa hakan a yanzu ba, kuma bata san ranar da zata shirya ba, domin a kullum tana fargabar barinsa yaje gidansu da sunan hira, ta toshe duk wata hanya da za a gane cewar da shi take mu'amala tun daga kan hotunansa har zuwa chat din da suke da kiran waya.
“Sai yaushe?”
“Wani lokacin kuma”
“Karki dauki lokaci kin san bana son nisa dake, ni far har tsoro nake Allah yasa ba breaking heart dina zaki yi ba, saboda kin ki yarda yan gidanku su san ni”
“Ba zan taba iya breaking heart dinka ba Ameer kasani, kawai ina tsoron abun da zai biyo baya ne, ina matukar tsoron Mahaifina kara ma Ummi tana da fahimta da hakuri, amman Abiey idan ransa ya bace baya yi da sauki”
“Baki shiryawa fuskartar ko wane kalar kalubale akaina ba kika bari na fada sonki? Mi na yi ma iyayenki ne suka tsane ni? Just because of abun da ya faru tsakanin da Maleek ni fa na dade da watsar wannan abun, soyayya ba haramun bace kuma aure ba zamu yi ba wai muna soyayyar ba ne dan mu rabu, da kin san yadda Daddy yake matsa min lamba akan maganar aure da kin tausaya min”
“Ni ma ai matsa min ake yi, kawai na kasa fitowa na fada musu cewar kai bake so ne, na kuma kasa bawa kowa kofar da zai furta min so ko ya nuna min haka, saboda gudun kar a cilasta ni na fitar da wani ba kai ba, ina matukar sonka Ameer, na jefawa maza da yawa dutse saboda da kai, kamin na hadu da kai idan maza sun taya ni bana amsawa balle na siyar, bayan haduwa ta kai ma kamar ammin turaren farinjini haka maza bina da nuna soyayyar a gareni, amman na saka amsar kowa, idona be ganin kowa zai kai Ameer, bana jin muryar wani namijin na jidadi sai kai, sunan kowa baya min dadi sai kai, kullum mafarkina da burina yadda zan yi rayuwa da kai ne, na karya dokakin gidanmu, na gurbata tarbiyata saboda kai Ameer, yanzu kuma ina shirin fuskarta wani babban kalubalen saboda kai, Allah yasa wata rana karka juya min baya, karki min irin abun da wasu mazan suke yi na butulcewa matarsu, idan na rasa ka zan shiga mawuyacin hali, ina matukar sonka Ameer...”
Tana maganar hawaye na sauko mata, gaba daya sai jikinsa yayi sanyi zuciyarsa ta yi wani iri, a sirrance ya sauke ajiyar zuciya, ya matsar da fuskarsa kusa da tata ya tsatsa bakinta, sai ta lumshe ido hawayen na cigaba da yi mata zuba....
“Ya kamata ki tafi kar a sake kiranki, i love you”
Ta bude ido ta share hawayen tana kallonsa, sannan ta bude motarsa ta fita ta nufi tata motar ta shiga, ta murza key ta yi reverse tare da horn Mai Gadinsa ya bude mata ta fice. Ta madubin motar yana hangota har ta fice sannan ya kwantar da kujerarsa baya ya jingina ya lumshe ido yana busar da iskar bakinsa...
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 27
Hanne ta kawo ma Dr Zainab abincinta a daki, yaranta kuma suka ci nasu abinci a falo bayan sun yi sallah. Maleek ne kawai ya fito da abincinsa a waje ya zauna ya ci a balcony da ya gama kuma sai ya zauna a gurin be tashi ya cigaba da latsa wayar da yake. Sai da yamma list Ummi ta hada Waira tea ta kuma saka Hanne ta soya mata dankali, sai ta fito ta zauna a Balcony nesa da inda Maleek yake zaune tana sipping tea da Biscuit, irish din da aka soya mata ma bata taba shi ba, idonta harabar gidan kawai take kallo da motocin da aka faka, har yanzu tana mamakin yadda rayuwarsu mutanen gidan take duk girman gidan ace su kadai suke rayuwa a ciki, ga kawata ko'ina da aka yi kamar ba za a mutu ba, har gobe tana tsoron hawa mota sai dai tsoronta ya ragu ba kamar da ba. Jin an zauna kusa da ita ya saka ta juyo a hankali sai ta yi arba ďaya daga cikin bakin da suka zo dazun, murmushi yayi mata ita kuma ta maida kanta kasa ba tare da tace masa komai ba. Ya kai hannunsa ya dauki biscuit ďaya ya fara ci.
“Waya saka miki zobe a wuya?”
Ta kalli zoben.
“Sulem...”
“Sulem.... Waye kuma Sulem.... Saurayinki ne?”
Ta yi shiru, sai ya kara matsowa kusa da ita.
“Na sanki ni na tsince ki a lokacin da aka jefar da ke kin tuna”
Ta kalleshi da kyau.
“Yes karki min karya kin san dai na sanki ko? Fada min ina iyayenki suke, na sani ma domin yayanki abokina ne kuma na ga suna nemanki, amman ina son na sake sani ne”
Ba zata iya fadar wanda ya dauko a lokacin da hankalinta ya gushe ba, sai dai ta san kamin ta suma mutumen da ta gani ko kadan be yi kama da wannan ba. Hakan ya saka ta mika hannunta ta taba hannunsa be san manufar ta yi hakan ba shiyasa be hana ta taba hannun nashi ba, sai ma kallon hannun da yayi. Gardamar da suka yi da Mahmood ta gani har yayi ikirarin cewar shi ya san yadda zai yi ta fada masa inda iyayenta suke, bayan Mahmood ya labarta masa cewar har yau bata taba cewa komai akan iyayenta ba.
Be ankaro ba ya ji ya bushe da dariya sosai har tana tintsirawara, shi ma murmushi yayi yana kallon yadda dariyarta take da burgewa. Maleek ma sai da ya dago ya kalleta ya dauke kai ya cigaba da latsa wayar da yake.
“What...”
Jabir ya tambaya yana kallon kansa da mamaki domin ban san abun da take yi ma dariya ba, Waira kam plan dinsa take dariya da yadda ya sha alwashin sai ya mata wayo ta fada masa komai. Kofar falon aka bude Ummi ta leko tare da Mahmood da Nimra har da Hanne suna kallon ikon Allah.
“Jabir me ka fada mata take dariya haka?”
Ya dan karkato ya kallesu.
“Nothing bata dariya ne?”
“Tun da take a gidan nan bata taba dariya ta kyalkyata ba”
Ya juyo ya kalleta a yanzu kuma murmushi take wanda ya bayyana hakoranta. Ummi ta yi murmushi cike da jindadin ganin farincikin Waira.
“Well done Jabir daga zuwanka ka saka min ƴa dariya”
Yayi dariya shi ma ba tare da sanin abun da Waira take yi ma dariya ba, shi dai ya san tambayar kawai yayi after that be fada mata wani abun dariya ba. Ummi ta juya ta koma ciki tare da Hanne suna ta mamaki, Nimra kuma ta kashe masa ido irin na zolaya.
“Yaya dai Jabir ko dai taku ta zo daya?”
“Da wa? Ai ba zaki yarda ba”
“Saboda me? Indai ruwan zai maka wanka ai sai dai mu nama maka na dauraya”
“Hmmm -Nhmmm Nimra kenan ke zaki yarda ki barwa wata ni?”
Ta saka dariya domin ta san halinsa da barkwanci musamman idan baya son abu yanzu ne zai juye ya mayar akan wani.
“Ni na mashinshini na kai ne baka da kowa, shiyasa nake maka kamu ka samu wannan yarinyar ta taimaka maka”
Ya girgiza kai yana cije baki.
“Ko waye mashinshinin nan na ki ki fada masa you're taken kuma ina da kishi bana son wani na rabar iyalina”
Dariya ta saka gudun kar Maleek dake zaune can gefe ya gwatsaleta ya saka ta juya ta koma falon tana gyara dankalin kanta. Shi kuma ya sake juyowa ya fuskanci Waira.
“Fada min ina iyayenki suke?”
“Waira zata fada, amman ba wayo ka yi ba”
Fada masa take zata fada masa, amman ba dan yayi mata wayo ba, shi kuma sam be gane salon karin halshen nata ba, shiyasa be yi kokarin cewa komai ba har ta cinye biscuits din dake kan plate din gaba daya ta kalleshi idonta na cika da hawaye ta ce.
“Waira bata da yaya, bata da Baba, bata da Mama amman tana da Eid”
“Waye Eid?”
“Dan'uwanta ne, yana sonta, Eid yana mata komai amman yanzu be neme ta ba, Waira ba zata koma garinsu ba, idan ta koma Sarki zai kasheta”
Mamaki ya kama Jabir.
“Saboda me? Me kika aikata? Wani kika kashe”
Sai ta girgiza kai hawaye na sauko mata.
“Bata kashe kowa ba, amman Sarki yace idan Waira ta gudu ba zata iya dawowa ba, kuma wani ya mutu saboda ita, za a kasheta”
“Miyasa kika gudu? Baki da yan'uwa a can? Ke baiwa ce ko kuma me?”
Ta girgiza kai hawaye na sauko mata kamar ba gobe.
“Waira bata san kowa ba, ita kadai take zaune tana da....”
So take tace bera da zakara kuma ba zata iya fadar hakan da hausa ba, ta suna sunan da aka fada mata na zaka da bera.
“Waira tana da Hens, Waira tana da Rat, Waira Waira zata mutu kusa Sarki ba zai kyale ba, zai kasheta”
Ta girgiza hancinta na zubar da majina kamar yadda idonta ke zubar da ruwan hawaye.
“Waira bata son ta mutu, Waira tana son ta ga Eid Waira bata son ta koma, ba zata gane hanya ba”
Da gaske take fada domin tana yawan tuna mutanen garin da rayuwar da take a garin amman ko kadan ta kasa tuna sunan garin ma balle kuma ta san hanyar da zata bi ta tafi, ita dai ta san ta rayu a wata duniyar kamin ta samu kanta a nan, kusan kullum sai ta kwanta da tunanin Eid da berayen da suke rage mata kewa. Ta kalli Jabir tana kuka sosai.
“Waira bata son ta mutu, Waira tana son Eid, Eid ba zai zo ba, Sulem ba zai zo ba... Waira tana Son Sulem....”
Ya matso kusa da ita ta jingina kanta jikinsa yana jin tausayinta na kama shi. Har suka ci suka sude Maleek be dago ya kalleta ba tun bayan kallon da yayi mata da farko, sai dai kunnuwansa suna sauraren komai take fada and one by one ya fahimci ko wace kalma dake fita bakinta.
“Waira bata son makaranta, suna mata dariya idan ta yi magana, Waira bata da kawa a makaranta”
Kusan duk wani abu dake cinta a rai sai da ta fadawa Jabir, the way da yan makaranta suke tsokanarta yana mata ciwo sosai, idan aka tambayeta ta kasa bada amsa ko kuma ta yi bayani ba a yadda suke yi ba, suna mata dariya ita kuma tana jin zafin haka, idan an tashi cin abinci bata da abokin zama ta ci abinci, she's not that child da za a ce tana tsoron mutane domin ba small girl ba ce, but yanayin rayuwarta ya saka tana shakkar kusantar mutane, ga yanayin mu'amalarta da shigarta ya ya banbanta da na sauran yan makaranta domin bata son taka talkami har yanzu, tana isa makaranta sai take cirewa ta rike a hannu, ta inda Allah ta taimake ta rashin rufe kai ba ita kadai ce bata yi ba, domin akwai yara da yawa a makaranta da basa rufe kansu wasu ma ristoci ne wasu kuma musulmai ne da suka ari rayuwar turawa suka yafa.
Ko baya ga wannan ma ita dai gani take an cilasta mata na cewa dole sai ta koyi rubutu da karatu, abun da bata iya ba tun farko, sai dai hakan ya taimaki rayuwarta domin tana jin yaren hausa da English a yanzu, sai idan an yi mata mai sarkakiya ne kawai ba zata gane ba. Rike hannunta ďaya a ciki ďayan.
“Waira tana son Ummi.. Tana son Nimra.. Waira tana Son Mahmood... ”
Ya nuna kansa.
“Waira tana son Jabir?”
Ta dago ta kalleshi idonta har sun sauya kala saboda kuka. Sai ta girgiza masa kai alamar aa.
“To Waira tana son Maleek?”
Nan ma ta girgiza kai.
“Waira tana Son Namra? Da Abiey?”
Ta girgiza kai a karo na uku cewar bata son su.
“Mun shiga uku har da Mai Gidan gaba daya? To shi mi yayi?”
Bata son Abiey da ďansa Maleek saboda basa sakar mata fuska yadda Ummi da Nimra suke, kuma basa janta a jiki yadda ya kamata, Jabir kuma yau ta fara ganinshi taya zata san halinshi har tace tana son shi. Maleek ya mike tsaye ba tare da ya dauke plate din da ya ci abinci ba ya fice daga gurin ya koma cikin falo. Ita kuma sai ta saka gefen rigarta ta share fuskarta, Jabir ya yamutsa fuska alamar kazanta.
“Noooo bari na dauko miki tissue”
Ya tashi shi ma ya bi sahun dan'uwansa Maleek, sai ita ma ta tashi ta nufi hanyar Garden tana tunani kala kala, a cikin abubuwan da take tunanin babu mao mata ciwo kamar rashi ganin Eid tana son ta sake saka shi a idonta kamin ta mutu, domin ta san mutuwarta zata iya zuwa mata a ko wane lokaci, Sarki be taba alkawari ya saba ba, kuma ba zai fasa akanta ba.
Abun ka da gwani, daga shiga dauko tissue Jabir ya shantake da bawa Ummi labarin abun da Waira ta fada masa, da kuma fahimtar manufarta da yayi. Tausayinta da kaunarta sai ta karu a zuciyar Ummi.
“Shiyasa bata da sakewa yarinyar nan kullum tana zaune kusa da ni, komai ake hira ba zata saka baki ba, shekararta ďaya a gidan nan amman taki ta sake jiki da kowa, wata kila shiyasa ta ki ta fada mana inda garinsu yake saboda bata son a maida ta garin, Allah kadai ya san abun da ta yi going through”
“Tace bata son Abiey da Maleek amman tana son da Nimra da Mahmood”
Ummi ta yi murmushi tare da mikewa tsaye tare da mika hannu ta karbi tissue dake hannun Jabir.
“Ba ni tissue”
Jabir ya mika mata ta zara ta share hawayenta daman abu kadan yana saka ta kuka a yanzu saboda zuciyarta a raunace take. Jabir har ya mike tsaye zai bita sai mahaifiyarshi sai dakatar da shi.
“Yanzu kuma ai sai ka ba ta damar magana da ita tun da ka yi mai yuyuwar, sanadinka ta fadi abun da ta boye kar kaje yanzu zata ce ka tona mata asiri wata kila yardar da kai ta yi shiyasa ta fada maka”
“Gaskiya yarda ce kam tun da bata fadawa kowa ba sai ni”
Nimra ta kwantar da kanta jikin Dr zainab.
“Ta ba ni tausayi”
“Darasi ne agareku ku da kuke da iyayen a raye, kuma suka dage suka ba ku gata da tarbiya daidai gwargwado, sai ku bisu da addu'a kuma ku cigaba da yi ma Allah godiya kuna musu biyayya”
Maganar da Dr Zainab ta yi ta soki Nimra, sai ta yi shiru kamar ruwa ya ci tana kallon wani gurin na dabam har sai da Jabir ya fice sannan ta tashi zaune tace.
“Mommy akwai maganar da nake son na yi da ke, amman ba yanzu ba sai mum kebe saboda magana ce mai girma, but ke kadai zaki iya taimako a nan saboda Abiey yana jin maganarki kuma zaki iya tankwara Ummi ta aminta ma”
Dr Zainab ta kalleta da duba da babu wasa a cikinsa.
“Wace magana ce?”
“Akan wani ne, kusan dai zan iya cewa maganar aurena ne, amman dai sai kin kara hutawa zuwa gobe ko jibi zai mu yi maganar, amman for now karki fadawa kowa mun yi maganar wannan sirrinmu ne”
Dr Zainab ta gyada mata kai cike da jindadi daman kullum burinta ta ga sukana dan'uwanta, kusan ta fi kowa damuwa da rashin auren da kowa be yi ba a cikinsu tun daga kan Maleek da be son zancen aure har zuwa Nimra da Namra da suke mata, a take ta ji duk ta matsu goben ta yi fada mata ko minene.
*** ***