Showing 99001 words to 102000 words out of 363274 words

Chapter 34 - Duk Karfin Izzata Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

3192

nauyayyar ajiyar zuchiya Khalid ya sauke tare da faɗin "da gaske Auta Ammi ta faɗa miki ni zaki Aura, gyaɗa masa kai Zahra tayi alamar eh, gyara tsayuwar sa yayi kafin yace "to kina sona, juyawa Zahra tayi zata gudu yayi sauri riko hannunta sai lokachin idon'sa ya sauka kan Yusuf dake zaune ya zuba musu ido, diyana kam bata ma san sunayi ba game nata kawai take bugawa hiyana ma kanta na kan qur'ani karatun ta kawai take

Harara Khalid ya wugawa Yusuf zai yi magana ke nan haidar ya shigo da gudu yana faɗin Ammi, Ammi ina kike yaya Ahmad ya mut....✍️


💖The Talent Troupe Writer's 💖

1 Duk Karfin Izzata
2 Gidan Aunty
3 Jini Ɗaya
4 Sarki Sameer
5 Kafita Zakka

Kar kubari abaku lbr love Story's
*💫STAR LADY💫*27

💖The Talent Troupe Writer's 💖


*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
⬇️
*Star Lady*
Star lady


Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai



*Episode 2️⃣7️⃣*



......Ammi, Ammi ina kike yaya Ahmad ya mutu, a sukwane Yusuf ya miƙe yana faɗin "kai haidar ka dawo cikin hankalin ka, wani Ahmad ɗin? "wlh yaya Yusuf ina chikin hankalina yanzun nan muna zaune dashi a fada kawai ya fara tari, jini na fito kafin kache me ya faɗi, ai tun haidar bai kai karshen maganar ba Khalid ya saki hannu Zahra ya juya har suna karo da Yusuf wajen fita da gudu, Haidar kuwa ya nufi betroom ɗin Ammi, mikewa diyana hiyana zahra lamrat amrat sukayi suka bi bayan su Yusuf, tare Ammi da haidar suka fito suma suka nufi fada

Koda su Ammi suka isa fada gaba ɗaya family sun haɗu awajen suna tsaye chirko chirko da kaga fiskokin su kaga alamun tashin hankali musamman Khalid da Aiman na su tashin hankali banne,


BGS daune a tsakiyar fada ya ɗora kan yaya Ahmad kan chinyar sa yana zura hannun sa chikin rigan Ahmad, Abba Aryan Fahad Umar suna tsaye a kansu, Aiman da Khalid kam sun ma kasa kariso wa wajen saboda tashin hankali daga baya suka tsaya

, shiru gaba ɗaya su kayi suna sun zubawa BGS ido suna sauraron suji me zai che

.. Almost 5mnt san nan BGS ya ɗago green eyes nashi da suka sauya launi izuwa jaa sosai chikin wata iriyar voice mai kama da mara lfy ya furta "bai mutu ba suma yayi,ku bani ruwa mai sanyi sosai gaba ɗaya fada ta ɗauƙa da alhamdulliah san nan Khalid ya juya da sauri ya nufi katuwar freij dake cikin fadan ya ɗauko ruwa mai sanyi ya dawo ya miƙawa BGS, tsabar tashin hankali har ya manta ma ana buɗe robar ruwa..

...Ansan ruwan Aryan yayi da sauri ya buɗe bakin roban san nan ya mikawa BGS, hannu BGS ya mika wa Aryan alamun ya zuba masa ruwan, zaba masa kaɗan Aryan yayi a hannun nashi, a hankali BGS ya shafawa Ahmad ruwa a fuska

wani atishawa mai karfi gaske Ahmad yayi, ya fara tari da karfi karfi kamar makogoran sa zai fashe yana kokarin miƙewa, da sauri BGS ya rikosa yana faɗin "kubani ruwan, a hanzar che Aryan ya miƙa masa roban gaba ɗaya, ansa yayi ya ka fawa Ahmad a baki amma ina Ahmad yaki sha sai kokarin mikewa yake, gaba ɗaya ya sauya lokachi guda ya rame ya fita hayyachi sa,

Da karfi Ahmad ya fisge jikin sa daga na BGS zai mikewa, a'sukwane BGS ya tamke sa ya mai dashi ya zaunar gaba ɗaya fada hankalin su ya tashi ganin halin da Ahmad ke chiki

faɗa ne ya kaure tsakani BGS da Ahmad dan Ahmad ya dage sai ya tashi, shi kuma BGS ya hana shi,da BGS ya ga dai Ahmad ba zai sarrafu ta lalama ba sai ya mike, yasa karfi ya danne Ahmad a kasa ya haɗa hannayen sa dukka biyi ya taka da kafa ɗaya ya damki gashin kan sa ya ɗago da fiskar'sa ya kafa masa robar ruwan mai sanyi a baki, dan ruwan zata tai maka masa sabo da tarin da yake,

ba shiri Ahmad ya fara haɗiye ruwan, dan dole, kawar da kai Ammi da Ummi su kayi daga kallon Ahmad suna kwalla, da gudu Aunty mardiya ta juya ta bar fada tana kuka, bazata iya kallon halin da Ahmad ke chiki ba, kuka Aunty salma keyi sosai rungumeta Aunty farida tayi tana ɗan bubbuga bayan ta alamar rarrashi,ita ma dai Aunty farida hawaye take, shi kansa Khalid daure wa yake amma ji yake kamar zai yi kuka, sosai hiyana ke kuka kamar ranta zai fita daman ita sarkin tausayine, haidar Umar duk kwalla suke, Fahad ma idon sa ya chika tab da kwalla amma basu zubo ba, Abba kuwa idon sa ta sauya tayi jaa sosai, ga tashin hankali nan karara a bayyane a kan fuskar sa, Aiman kam ba'a magana dan yafi kowa shiga damuwa saboda tare suke komai da Ahmad ko Aryan da suke yan biyu bai shaku dashi kamar yadda ya shaku da Ahmad ba

Ganin yadda BGS ya taka hannun Ahmad yayi yawane dan har hannun nashi sun chanza izuwa jaa sun fara kunbura abunku da farar fata, yasa Aryan ɗukawa kasa yasa hannun'sa ya dan bubbuga kafar BGS alamar ya sassauta takun da yawa hannun, chire kafar sa yayi gaba ɗaya tare da chire roban ruwan daga bakin Ahmad din, ya zuba masa ido,

shiru Ahmad ya kwanta a kasan kamar mai tunani,wani abu hannu Aryan yasa ya ɗan tattaɓa kuma tunsa yana kiran su nan sa, shiru Ahmad bai amsaba kuma idon sa a buɗe ya na kallon su, ganin hakan yasa BGS mikewa tsaye sosai ya ɗauki Ahmad ɗin ya saɓashi a kafadar sa ya fiche dashi, daga fadan gaba ɗaya family suka bi bayan su

Kai tsaye ɗakin da suke jin yar duk wan da bai da lfy a gidan ne, dan in dai ba sun koma London ba, to ba wan da ake kai wa asibiti su suke duba kowa na gidan, dan babu abun da babu na jinyar ma jinyata a ɗakin

akan katafaren gadon da aka tanada dan marasa lfy BGS ya kwantar da Ahmad, har lokachin idon sa biyu yana bin su da kallo amma ya kasa magana, kayan aiki BGS ya ɗauko ya fara duba shi,

almost 30mnt BGS na kan Ahmad yana ɗuba shi,

Slowly ya juyo ya kalli su Abba da su kayi chirko chirko suna jiran suji meke damun Ahmad "Abba ni fa banga wani abun da yake damun Ahmad ba, nayi iya bin chike na banga komai ba . Amma Aiman Aryan kuma kuzo ku gwada mugani, ya karisa maganar yana kallon Aiman da Aryan dake tsaye waje guda, da kyar Aiman ya iya buɗe baki yace "bazan iya ba bazan iya ganin Ahmad chikin chiwo ba shiyasa na kasa karisawa inda yake, gaba ɗaya mutanen ɗakin sun tausaya wa Aiman dan kowa yasan duk inda kaga Aiman to fa Ahmad na wajen tare suke komai .

a hankali Aryan ya tako izuwa wajen gadon Ahmad, ya karbi na urorin dake hannun BGS ya fara nashi gwaje gwajen, shima almost 30mnt ya ɗauka san nan ya juyo a hankali yana kallon su Abba har bai san haɗa ido dasu "Aryan ka gano wani abu ne Abba ya tambaya a ruɗe, girgiza kai kawai Aryan yayi alamar a'a, dan ya kasa magana, jin hakan yasa Aiman juyawa da sauri ya bar ɗakin

shiru gaba ɗayansu su kayi kowa da abun da yake tunani almost 1h, san nan BGS ya juya ya ɗauki alluran barchi ya yiwa Ahmad, yana zare alluran ya ajiye ya fita dakin da sauri dan ji yake kamar zuchiyar sa zata fashe, dan yana matikar kaunar yan uwansa mu samman Aryan Aunty farida Khalid Aiman Ahmad Yusuf Son da yake musu na da ban ne "Abba muje mu kyalesa alluran barchi aka masa mu barshi ya huta chewar Aryan yana gama faɗin hakan ya nufi waje shima, gaba dayan su suka bi bayan Aryan su ma

YOLA


Dawani matsanan chin ihu buba ya farka daga doguwar sumar daya faɗa, har sai da ya tsorata su inna dake zaune awajen kowa ya miƙe zai gudu, ban da yaya bello dake zaune ko motsi bai yiba, zubur buba ya miƙe yana ko karin fita waje, da sauri malam yace "ku riƙe sa

a guje inna habiba da innar bubu su kayi waje saboda tsoro, yaya bello ne yayi ta maza ya riko buba sai kokarin fiskage buba keyi, malam daya ga abun tayi yawa sai ya che da yaya Bello "a ɗaure sa da igiya domin kuwa tun lokachin da kuka kawo sa na fahimchi ya bugu a kai sosai kuma hakan ya taɓa masa ƙwaƙwalwa gaskiya, yanzu dai sai dai a barshi a ɗaure ana masa magani idan da rabon samun sauki to Allah ya sauwaka, idan ku kache zaku sa kesa to ina tabbatar muku bola bola zai fara bi, wasu hawayen masu zafi na tausayin ɗan uwan sa yaya Bello ke yi, haka nan ya nufi wajen da malam ke ɗaure mahaukata ya sa karfi ya danne buba ya ɗaure sa, a zuchiyarsa yana tunanin "duk abun da ya faru da kai buba kai kaja ma kan ka, da kan ka, ka kun tatawa marayu, bayin Allah basu jiba basu gani ba basu maka komai ba ka takurawa rayuwar su ka addabe su ai daman alhakin su bazai taba barin ku ba,

Sosai ya ɗaure buba, sai ihu buban ke yi yana surutai, miƙewa malam yayi ya nufo su hannun sa riƙe da kwarya mai ɗauke da magani, "kai bello riƙemin kanshi mu bashi maganin nan zata tai maka masa chewar malam, da kyar suka iya ɗurawa buba maganin san nan yaya bello ya sake sa ya fito daga bukkar, a bakin kofa ya samu inna habiba da innar bubu sai sare ido suke "kai bello ya ake chiki? innar buba ta tambaya tana ɗan leƙa ɗakin, haushi kamar yaya Bello ya shaƙeta ta mutu ya keji wai ɗan da kika haifa a chikin ki, ki ke gudu dan ya kamu da wata laluran ba duk ku kuka ɗorasa a kan gurɓatattiyar hanya ba

banza yaya Bello yayi dasu bai tanka suba dan haushi, chikin tsiwa inna habiba tace "kai mara kunya, mara albarka ba da kai muke magana ba ne da zaka mana shiru, zaka faɗa mana ya jikin bubane ko sai na kwakkwaɗa maka mar

rabawa ta gefen su yaya bello yayi ya wuche ba tare da yace da su komai ba, wani dogon salati inna habiba tayi tana faɗin "a lallai bello ka girma to ko zaka yiwa innar bubu rashin kunya ai ni ba zaka min ba ko? tun da ni kanwar uban ne, shi dai yaya bello tafiyar sa yayi yana jin inna na surutai amma ko ajikin sa yanufi hanyar gonarsa chikin zuchiyar sa yana tunanin diyana "ya take shin chiwon nata ya warke ne Allah sarki bayin Allah, ɗayan ban garen zuchiyar sa kuwa tunano masa irin kyan da diyana tayi yake, tayi wani fresh da ita daman diyana ba baya ba wajen son kwalliya wow ga kyanta ya kara fitowa, sosai yake tunanin ta oh ni Bello Allah ka bani diyana a'matsayin mata aure, da sauri kuma ya kawar da tunanin damun diyana a matsayin mata dan yasan yanzu kam tafi karfin sa

Zama yayi chikin gonar tashi sai tunani yake yama rasa meke masa daɗi


Kano

gaba ɗaya family Abba suna zaune a babban palon sa sunyi jugum jugum daka gansu kaga alamar tashin hankali a kan fiskokin su

"my daughter jirgin ku fa karfe 4:30 zai tashi yanzu kuma 4 tayi ya kamata ki tafi chewar Abba yayi maganar yana kallon Aunty farida "aa Abba ba zan iya tafiya ba sai naga yadda zata kasan che zan jira farka warsa, mugani "aa my daughter ya kamata ki koma tun da akoi waya zamu kira ki idan ya farka koma me ake chiki zaki ji "Abba Allah bazan iya tafiya na bar ɗan uwana a haka ba wlh Abba idan na tafi nasan zuchiya ta zata iya bugawa pls my Abba ka bari dai zuwa gobe, ta karisa maganar kamar zata fashe da kuka "to shike nan my daughter Allah ya kaimu Allah yasa idan ya farka ya dawo dai dai, gaba ɗaya palon suka amsa da amin, shiru palon yayi bakajin komai sai shesshekar kukan hiyana dan ita ta kasa yin shiru, tana da tausayi sosai, bare ma idan ta tuno lokachin da BGS ya haɗe hannun yaya Ahmad ya take a kasa sai ta sake rushe wa da kuka

......alama Ammi ta mata da hannu akan tazo da sauri ta miƙe ta nufi Ammi riko hannunta Ammi tayi ta zaunar da ita saman sofar da suke zaune ita da BGS, hiyana da BGS su ka sa Ammi a tsakiya kwantar da hiyana Ammi tayi kan chinyar ta tana ɗan bubbuga bayan ta kasa kasa tafara magana "kiyi shiru hiyana kukan ya isa haka kinji zai samu lfy ki masa addu'a,

jin Ammi na magana kasa kasa ne yasa BGS ɗan wai gowa ganin yadda Ammi ta kwantar da hiyana a kan kafar tane, yasa shi sauri kawai da kai yana jan tsaki a zuchiyarsa yana faɗin "nikam ban san ya Ammi take san mai da yaran nan ba, yanzu wan nan abun zata wani kwantar da ita a kan kafar ta, gaskiya ni dole ma yaran nan su bar gidan nan ko kuma ni na koma gida na Abj dan bazan iya kallan abun haushi ba "BGS time ɗin farka wan Ahmad yayi fa chewar Aryan

Gaba ɗayan su, suka mike da sauri suka fito suka nufi ɗakin da Ahmad ke kwanche,


Koda suka shiga already Ahmad ya farka, idon sa a buɗe dan ya kai 5mnt da farkawa, da sauri BGS da Aryan suka kariso bakin gadon, hannun Ahmad BGS ya rike kasa kasa ya kira su nan shi "Ahmad, shiru bai amsa ba kuma dai idon sa a buɗe, kariso wa wajen gadon Aiman yayi cikin dashewar murya ya fara magana "Ahmad pls wake up ba zan iya juran ganin ka a haka ba, wlh idan baka tashi ba zuchiya ta zata iya bugawa pls my blood, kuka Aiman yake kamar karamin yaro yana Magana, ko motsi Ahmad bai yi ba kuma dai still many manya fararen idon nan nashi a buɗe, jijjiga shi Aiman ya farayi da karfi karfi yana faɗin "Ahmad pls wake up, ko motsi Ahmad bayyi ba ganin Aiman zai iya illata Ahmad yadda yake jijjiga shin nan yasa BGS riƙe hannun sa yana girgiza masa alamar ya dai na jijjiga shin, rungume BGS Aiman yayi chikin kuka yace "why, why, chiwon bata kama Ni ba takama Ahmad pls kuche chiwon ya dawo jiki na ya kyale min dan uwa na,ganin Aiman fa ya fita hayyachin surutai kawai yake hakan yasa.

....BGS juyowa ya kalli Aryan,ba tare da yayi magana ba, chikin sauri Aryan ya juya ya ɗauko allura ya haɗa ba tare da Aiman ya Ankara ba Aryan ya tsira masa alluran nan take yayi shiru difff kamar an ɗauke wuta sai kuma ya sake wa BGS dukkan jikin sa alamun yayi barchi, ɗaukan sa BGS yayi chak ya saɓa sa a kafaɗa ya nufi waje da shi

Hannu Aryan yasa ya ɗago Ahmad daga kwanchiyar da yake ya zaunar dashi ya sa masa fillo a bayan da ya jingina shi da jikin bango yana kallon face nashi, ban da ido ba abun da ke iya motsi a jikin Ahmad, juyawa Khalid yayi ya bar ɗakin dan zuchiyar sa ta gama karaya dab yake da fashewa da kuka

Aunty salma Aunty farida Aunty Mardiya hiyana sun fi kowa kuka a ɗakin shi kan shi Abba daure wa kawai yake, jiyake kamar yayi kukan shima ko zai samu sassauchi a zuchiyarsa, Ammi da Ummi sai sharan kwalla suke Aunty amarya kam bata wani damu sosai ba, dan ko kwallin hawaye bata yiba, sosai Aunty Maryam ma ta shiga damuwa dan itama har chikin zuchiyar ta tana son yan uwan ta, su hiyana ne dai bata so, Fahad ma daurewa kawai yake amma shima idon sa ta chika tab da kwalla, Haidar Umar sai kwalla suma suƙe dan gaba ɗaya ƴaƴan Abba suna matikar kau nar junan su, shiru Yusuf ya zauna dan shi tsabar tashin hankali ko hawayen ya gagara fita

"Hauwa'u ki tattara su gaba ɗaya ku tafi kowa ta tafi ban garen ta kuyi shiru kukan ya isa haka, addu'a zaku masa chewar Abba yayi maganar yana kallon Ummi, jiki ba kwari dukka matan suka fita ya rage mazan

da sallam BGS ya dawo ɗakin kusa da Abba yaje ya zauna suka zubawa Ahmad ido shima dai Ahmad ɗin su yake kallon kamar zai yi magana amma ya kasa, cikin tsawa BGS yace "kai ku mana shiru yayi maganar yana kallon haidar da Umar, nan take suka goge kwallan idon su suka nitsu,

.....Dawo da kallan sa kan Abba BGS yayi kafin yace "Abba yanzu menen abun yi dogon numfashi Abba yaja kafin yafara magana "ina ganin mu fitar da shi waje kawai mu kai shi Us ko UK ko india tun da suna da kwararrun likitochi "aa Abba dan uwana ya fi karfin yaje wata gasa jinya sai dai ita kasar tazo ta same sa a nan, likitan wani kasa kake son yazo ya du bashi, zanyi waya koma wani irin likitane kake so gobe zai zo, "to ka kira likita daga India dan sunfi kwararrun likitochi chan "ok kawai BGS ya faɗa san nan ya mike ya nufi waje, mikewa Abba ma yayi yana faɗin "Aryan ka kwantar da Ahmad muje ko mu kwalesa ya huta, yana gama faɗin hakan ya nufi waje, juyawa Yusuf da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login