Showing 243001 words to 246000 words out of 363274 words

Chapter 82 - Duk Karfin Izzata Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

3222

kowa ya gane su shi ya sanya ya saka kayan hausawa tun da nan ba wan da ya taɓa ganin sa da kayan hausawa zai yi wuya a gane sa

Bayan an kawo kusu takeaway hiyana ta ansa suka fice daga wajen suka koma mota chikin daji ya nufa da su yana tuki chikin kwanchiyar hankali
bakin wani katon dutse mai dubar da ruwa yayi parking na motar ya fito ya zauna saman bayan motar fitowa tayi itama bin wajen ta farayi da kallon wow wajen ha haɗu iya haɗuwa wajen kewaye yake da dogayen furanni masu kyau launin fari da kuma yellow daga gefe katon dutsene wadda ruwa ke zuba daga chikin sa kamar faffo yana taruwa akansa kamar rafi ga dogayen bishiyoyi koraye shar shar kewaye da dutsen wajen shiru baka jin kokai sai sautin kukan tsuntsaye
dawo da kallon ta tayi kansa ya chire face mark nashi ya ajiye a gefe yana kallon ta "yaya Prince wajen nan yana da kyau sosai" shiru yayi yana kallon bai yi magana ba takawa tayi a hankali ta karisa wajen dutse dake zubar da ruwa hannu ta sanya ta tara ruwar da mamakin ta sai ta ji ruwan da zafi kamar an sa a wuta kasa kasa taji sexy voice nashi yana faɗin "yinwa nake ji" da sauri ta juyo ta dawo wajen motar ta ɗauko musu abinchi ta kawo masa dirowa kasa yayi daga saman motar ya ɗauke ta chak ya ɗaurata saman bayan motar kafin shima ya haura ya zauna a tare suka chi abincin gwanin ban sha'awa sosai yau Bgs yaci abinci har mamaki hiyana keyi bata taɓa ganin sa yaci abinci mai yawan wanna ba suna gama chi ta diro kasa ta kwashe kayan abincin ta zubar ta koma wajen dutse ta tsaya tana kallon ruwan ta zubawa tsuntsayen dake zuwa shan ruwan awajen ido ji take kamar ta shiga ruwan tayi wanka tayi nisa chikin tunanin sai jin sa tayi ya rungumota ta baya ya kwantar da kan sa saman kafaɗarta ya zuro hannun sa saman kugun ta kasa kasa yace "zaki shiga ruwan ne?" Hannu ta ta ɗaura saman hannun sa dake kan kugun ta tana shafawa chikin shagwaɓa tace "eh zan shiga kai ma zaka shgane? Juyo da ita yayi suna fuskantar juna "ba yadda zan yi in shaga chikin ruwan nan da kayan jiki na ɗin nan" kallon sa tayi da kyau kwafa tayi a ranta tace zaka shigane ma ai na san me zan maka sakin sa tayi ta faɗa chikin ruwan tare da sakin ihu dan duk tunanin ta ruwan dake taruwa a kasan dutse bai da zurfi sai ta ji akansin haka dumin kuwa ruwan ya haɗiye ta gaba ɗaya gashi bata iya ruwa ba diyana ta fita iyawa ko a garin su ita bata shiga rafi diyana ce mai shiga yana tsaye yana kallon yadda take shan ruwa sai mulewa kasa take tana ɗagowa sama sai da ya barta ta jigata sannan ya chire agogon hannun sa da wayar sa tare da hulan kan sa ya ajiye ya faɗa chikin ruwan kamota yayi ya daurata saman kirjin sa yana kallon face nata langwaɓar da kai tayi a kafaɗar sa tana jan numfashi "kin kyau ta da kika jika mu yanzu dame zamu koma gida? Kankame sa tayi ta kasa magana domin tasha ruwa sosai takawa yayi zuwa in da ruwan ke zuba kamar fanfo ya tsaya a dai dai wajen, ruwan na zubo musu daga kai "har yanzu baki dawo dai dai ba kenan? Sai lokacin ta ɗago kai da kyar ta iya chewa "yaya Prince dan Allah ka fitar da Ni" matso da face nashi yayi dab da nata "no ai tun da kika sani na shigo ruwan nan tofa sai ki shirya ɗaukan duk abun da zan yi" chizon sa tayi a saman lallausan lips nashi chikin shagwaɓa tace "yaya Prince wlh bana numfashi sosai ka fitar da ni daga ruwan nan kar na mutu" lasan lips nashi in da ta chijesa yayi kafin yace "kina so kenan" bai jira amsar ta ba ya haɗe bakin su waje guda ga ruwa na zuba musu daga kai yana jikasu almost 10mins suna haka kafin ya zame bakin sa daga nata yana kallon face nata yana kokarin yin magana wayar sa ta fara ringing kai kallon sa in da ya ajiye wayar yayi kafin ya dawo da kallon sa kanta gaba ɗaya ta jiggata da kyar take iya buɗe ido zame mata ɗan karamin hijabin kan ta yayi ya shiga watsa mata gashin kan ta ruwa na jika gashin kwantar da kanta tayi saman kafaɗar sa tana numfashi da kyar da kyar juyo da face na shi yayi yana kallon ta wani irin yanayi mai daɗi da annashuwa ke ratsa shi ya shagala da kallon ta bai ankara ba sai ji yayi tana kokarin sume masa a sukwane ya juya da ita ya fice daga chikin ruwan wajen motar su ya koma ya jinkina da jikin motar ya fara kiran sunan ta kasa kasa "Sister sister" da kyar ta iya waro idon ta da suka sauya daga blue zuwa jaa sosai,waro ido yayi yana kallon ta bai ɗauka ta jigata haka ba ta sha ruwa sosai buɗe gidan baya na motar yayi ya kwantar da ita dukkan su sai ɗigan ruwa suke

guntun tsaki yaja ya koma wajen da ya ajiye wayar sa ya dauko tare da agogon sa ya dawo kusa da ita kunna wayar yayi ya shiga latsawa da alama wani sakon yake turawa bayan ya gama ya duba miss call Aryan ne ya kira shi,kiran layin Aryan ɗin yayi bugu ɗaya Aryan ya ɗaga manna wayar tayi a kunnen sa daga ɗayan ɓangaren Aryan yace "blood ina ka bar wayar? Tsaki yaja kafin tace "menene?" "Na gama aikin da ka sani yanzu shigowar ka kawai nake jira amma akoi wata yar matsala" "matsalar me? "Har yanzu bai iya gane ɗan leken asirin dake chikin muba na binciki sojojin mu dukka ban samu ba" "No karka damu da wanan ni dai nace maka karka yarda da kowa idan na shigo zan kama koma wanenne yanzu dai zamuyi waya anjima yanzu akoi abun da nake" "ok to ina sister na take? Juyowa yayi yana kallon ta da kyar da kyar take numfashi sai rawan sanyi take "ban san in da take ba" dariya Aryan yayi kafin tace "amma Bgs kai fa ɗan duniya ne ka gama yiwa yar mutane mugun ta jiya instead of yau ka zauna ka bata kulawa amma sai kayi fitar ka ko? Allah dai yana kallon ka...bai bari Aryan ya gama maganar sa ba ya katse kiran yana kallon ta kawar da kansa gefe yayi yana ɗan jan tsaki ajiye wayar yayi chikin motar ya harɗe hannun sa ya kirji yana kallon sama kamar mai tunani

Almost 10mins suna haka sai ga Abdol ya danno hanchin motar sa wajen kusa motar su yayi parking sanna ya fito chikin sauri hannun sa rike da jaka mikawa Bgs jakar yayi sanna ya shiga motar sa ya juya ya koma buɗe jakar Bgs yayi ya fito da duguwar riga abaya ce baki kayan jikin ta ya fara chire mata sauri sauri ya sauya mata doguwar rigar sai rawan sanyi take yana kokarin chire nashi kayan yar karamar nauran dake gaban motar sa ta fara kara chikin sauri ya fasa chire kayar na shi ya rufe kofar baya na motar ya buɗe gidan gaba ya shiga ya kunna motar da gudun gaske ya bar wajen kai tsaye gida ya wuce dan sai rawan sanyi hiyana ke yi shi kan shi kayan jikin sa sun takura masa

Yana shiga gida bai ɓata lokacin ba ya fito ya ɗauke ta chak ya shiga chikin gida kai tsaye bedroom nasu ya wuce saman gado ya shinfiɗe ta ya wuce toilet wanka yayi da ruwa mai zafi sosai ya fito ya shirya chikin kayan sanyi dan shima daɗewar da jikakken kayan sukayi a jikin sa ya sanya yana jin zazzaɓi kayan sanyin sa ya ɗauko mata tare da safa da hula ya sanya mata tana kwance tayi shiru sosai ya shirya ta chikin kayan sanyin sa ganin har yanzu sai rawan sanyi take ya sanya ya kunna na'uran ɗumama ɗaki ya jona hand dryer da kansa ya busar mata da gashin kanta bayan ya gama komai ya duba time 2pm alwala yayi ya fito ya gabatar da sallah ya miƙe ya hauro saman gadon duba time ya sake yi 3pm saura 1h jirgin su ya ɗaga kwamciya yayi saman gadon ya jawota jikin sa ya jawo bargo mai laushi ya rufesu sosai ta shige jikin sa tana shan ɗumin jikin sa kasa kasa da murya kamar mai raɗa yace "sister are you okay now?" gyaɗa masa kai tayi alamar eh shafa kan ta ya fara yi suka yi shiru kowa da abun da yake tunani

To masu karatu sai mun haɗe gobe a Naija zamuga ya wasan zata kaya akoi fa shagali akoi sharholiya yanzu zaa fara buga asalin game ɗin mu damalmale da ku gobe zamuga wazaiyi winning 💃💃


💖The talent troupe writer's 💖




💋Duk Karfin Izzata 💋29

By Star Lady







Page 30


Uk

Barci mai matukar daɗi ne ya kwashe su yana rungume da ita a jikin sa. yana tsaka da barci wayar sa ta fara kara da kyar ya iya waro idon sa waje kusan tare suka farka da shi da ita ɗauko wayar yayi daga saman drawer sunan Khalid ne ya bayya na a kan screen ɗin duba time yayi 3:55pm tsaki yaja tare da kai kallon sa kan kyakkyawar face nata dai dai lokacin ta waro blue eyes nata a kan kyakkyawar face nashi da kyar ya iya futa "are you okay? Gyaɗa masa kai tayi kafin tace "yaya Prince ya muka dawo gida? Ya baka kai ni yawo sosai ba? "Eh duk da munyi fitar sirri akoi wayan da suka bi bayan mu ne shi ya sanya muka dawo gida yanzu dai tashi mu wuche lokacin tafiya yayi" yana kai karshen maganar ya miƙe ya sauko daga gadon.
kasa tashi tayi dan yana miƙewa wani mugun sanyi ta ji ya rufe ta,har ya kai bakin kofa ya juyo yana kalle ta tana kwance kamar yadda ya barta "sister ba zakai je Nigeria bane? Shagwaɓe fuska tayi kamar zatayi kuka ta fara magana "yaya Prince sanyi nake ji kuma na kasa tashi" dawowa yayi chikin ɗakin ya ɗauke ta chak ya fice da ita sai rawan sanyi take har ya kai palo sai kuma ya juyo ya dawo ya ɗauki ɗan karamin trolley sa daya shirya tana kwance saman kafaɗar sa kai tsaye waje harabar gidan suka nufa.

Already su Khalid sun fito kowa ya shiga motar sa tare matar sa Hisham da Ilham suna tsaye a harabar gidan suna musu bye bye ganin Bgs ɗauke da Hiyana ba karamin mamaki ya basu ba tunani Khalid ya shigayi anya Bgs ba wani abun yayiwa sister ba da ta sanya yau tun safe yake ta ɗaukan ta kai da biyu wlh ba haka nan ba. Ilham kuwa matsowa tayi kusa da kunnen Hisham tace "baby wai haka ogan kunnan yake? Baya barin matar sa ta tafi da kafar ta kai gaskiya ya iya soyayya da kula da mata" harara Hisham ya watsa mata kafin yace "ki dai iya bakin ki wlh idan ya jiki ba mai iya tare miki.

da gudu Abdol ya buɗe ma Bgs mota ya sauke ta a gidan baya sanna ya juyo yana kallon Hisham ba tare da yayi magana ba chikin sauri Hisham ya tako ya kariso gaban sa hannu Bgs ya miƙa masa Hisham har jikin sa na rawa ya bawa Bgs hannu sukayi mu sabaha chikin nitsuwa Bgs ya fara magana "to Hisham ka dawo mu kuma zamu tafi amma 2 weeks zamuyi ka kula da aikin ka sai mun dawo" yana kai karshen maganar ba tare da ya jira amsar Hisham ba ya saki hannun sa ya shige chikin mota sosai Hisham ya musu fatan alkhari da fatan adawo lfy sai murmushi yake.

Bayan tafiyar motocin su Bgs Ilham ta matso kusa da Hisham ta fara magana "baby me ya faru? Naga kana ta murmushi da baka taɓa yin irin sa ba" "my wife kin san matsayin Brigadier general kuwa? Bgs yana gaba da mu nesa ba kusa ba ina murmushi ne saboda yau na gaisa da shi hannu da hannu tare muka taso da su amma ban taɓa gaisawa da shi hannu da hannu ba ke ko baki da baki ma idan kika gaishe sa ba amsawa yake ba bare hannu da hannu shi idan kin gansa yana magana to umarni yake badawa idan za'a tafi filin yaki banaji awajen Aikin mu akoi wan da zai che miki ya san kalar voice nashi akoi manya manyan sojoji ma da basu taɓa jin voice na shiba duk yadda zan faɗa miki wanene Bgs ba zaki fahimta ba ni dai ina farinciki yau" a kule Ilham tace "to baya kula ka me ya sa zamu zo gidan su mu zauna? " "My wife ki sani nifa mun taso tare ne amma su Khalid ne abokai na ko Aryan ban kai matsayin da zanyi abota da shi ba tare Bgs ina ga baki san me kike faɗe ba ne kin san miliyoyin mutane nawa ne ke neman irin daman da na samu wasu sojojin ma nema suke ko a masu sharan gida ya ɗauke su su dai suga suna kusa da Brigadier general Safras amma ke shine kike wata magana" ajiyar zuchiya ta sauke kafin tace "tom shike nan muje mu shirya muje yawo" hannun ta ya riko suka wauce chikin gida.

A ɓangaren su Bgs kuwa lokacin da suka isa Airport an gama shirya musu komai suna isa ba tare da ɓata lokacin ba suka fito daga mota suka shiga katafaren jet ɗin Bgs mai ɗauke da tambarin sunan sa da manyan baki PRINCE SAFRAS zama yayi saman haɗaɗiyar kujerar jet ɗin hiyana ta zauna kusa da shi bawani ɓata lokacin su Khalid kowa tare da matar sa ya zauna har jirgin su ya ɗaga hiyana bata dawo dai dai ba. sanyi zazzaɓi take ji sosai chikin rawar murya da kakkarwan sanyi ta fara magana
"Yaya Prince sanyi nake ji sosai" kallon ta yayi da kyau kafin ya nuna mata saman chinyar sa da hannu ba tare da yayi magana ba da kyar ta miƙe ta dawo saman chikinyar sa ta zauna buɗe zip ɗin jaket ɗin jikin sa yayi ya kwantar da kan ta saman faffaɗar kirjin sa ya rufeta da jaket ɗin iya kan ta kawai ya bari awaje shiru ta lafe a jikin sa tana mai da numfashi. "Are you okay now? Ya tambayeta yana kallon face nata sai lokacin ta ɗago ido tana kallon kyakkyawar face nashi ɗan kwanto da kai sa yayi ta gefe yana kallon chikin idon ta girgiza mata kai yayi ya ɗaga gera ɗaya alamar lfy kike kallo na cool murmushi ta saki kafin tace "kamin kyau sosai ne shi ya sanya nake kallon ka" kawar da kansa gefe yayi yana murnushin gefen fuska.

Kallon Yusuf Khalid ke yi yayin da shima Yusuf ɗin ke kallon sa suna son yin gulma amma suna tsoro yau suna ganin ikon Allah domin idan ba ikon Allah ba ba abun da zai sauya Bgs haka wai har da kawar da fuska yana ɗan murmushi lallai sister ta chiri tuta lallai yau hakuri yayi rana daman duk wanda yayi hakuri zai yi nasara a rayuwan sa. waya Khalid ya chiro ya fara yi musu video ba tare da sanin su ba a ɓangaren Yusuf ma hakane waya ya chiro ya fara ɗaukan Romeo and Juliet ɗin nan ba tare da sanin su ba sai hira hiyana ke zuba masa shiko ya zuba mata manya manyan green eyes nashi yana kallon face nata a haka har barci ya ɗauke ta kasa ɗauke ido yayi da kallon ta gyara mata kwanciya yayi da kyau a jikin sa yana kallon face nata wani irin nishaɗi da farinciki ne ya dira a zuciyar sa lokaci guda. Shafa kan sa yayi ya furzar da iska mai zafi chikin ran sa yana tunanin "why? duk lokacin da nake kallon face ɗin yarinyar nan nake jin nishaɗi da farinciki ne why? Ko da yaushe nake son kallon face nata? why Nake jin ta har chikin raina? why Yanzu nake tunanin ta sosai?" ɗayan ɓangaren zuciyar sa ne ta bashi amsa da cewa "so mana son ta kake" da sauri ya girgiza kai yace "no so kuma ni? Ina never babu wanna wajen a rayuwata dogon tsaki yaja tare da kawar da kansa gefe ya fito da wayar sa ya fara latsawa. Mamaki ne ya kama su Khalid murmushi Khalid yayi a ransa yace "ai kaɗan ma ka gani in dai mace ce ai baka fara magana kai kaɗai bama yanzu ne zaka fara wlh inaga sai sister ta sa ka zama kamar mahaukaci muje zuwa yanzu wasan ya fara.

9:30pm jirgin su yayi landing A malam Aminu Kano International Airport Kano har lokacin hiyana barci take ga jikin ta yayi zafi sosai

Ako da yaushe Bgs shine na farko fita idan jirgin su ya sauka dan shi baya son ɓata lokacin amma awan nan karon su Khalid sun fita sun barshi yana tunanin ya zaiyi da hiyana dake barci a jikin sa baya son tashin ta dan tana jin zazzaɓi kuma bai san ɗaukan ta ya fita da ita dan sojojin da yan sanda ga manya manyan yan siyasa awaje, Airport ɗin a chike yake da jama'a so baya son kowa ya san yana tare da mace kusa da shi. Almost 30mins yana zaune ya kasa motsawa ga dubbanni jama'a na waje suna jiran fitowar sa ga taron yan jarida Aryan na zaune a cikin mota shi da jiddan sa shiru shiru Bgs bai fitoba buɗe mota Aryan yayi ya fito ya nufi cikin jet ɗin diyana na son fita ta bishi amma ya riga yayi nisa tana tsoron jibga jibgan sojojin dake


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login