Showing 60001 words to 63000 words out of 286946 words
sauri ta mike tsaye tana masa wani irin kallo kamar ta hade shi, ga wani shauki da mamakin sake ganinsa da tai yana cikata. Sai shi ma ya mike tsaye yana kallonta da murmushi a fuskarsa.
“Ina son ka sosai, ina yawan sauraren wakokinka lokacin da ina ji, ina son ka sosai kana burgewa ban taba mafarkin zan hadu da kai ba, kuma ban sake saka ran zan sake ganinka ina son ka sosai”
Ta karasa muryarta na rawa idonta kuma yana cika da kwalla irin na fan ya hadu da celebrity.
“Wow”
Ya fada still yana murmushi kamin ya kama hannunta.
“Zo muje”
Ba musu ya bishi yana rike da hannunta idonta suna kan fuskarsa, har ya zagaya da ita ya bude motar ya saka ta gidan gaba shi take kallo ji take kamar a mafarki ne. Rufe motar yai sannan ya je ya bude gate din ya dawo cikin motar yaja suka fita ya sake rufewa ya dawo ya rufe gate din sannan ya dawo cikin motar yaja suka fara tafiya.
Bata kallon komai sai fuskarsa wani abu mai kama da jindadi yana ratsata zuciyarta kamar zata fito waje akan bugawar da take da karfi, time to time yake kallonta sai ya dan sakar mata murmushi har suka isa wata kyakkyawar unguwar da tafi kama da GRA.
Horn yai ba bata lokaci aka bude masa katon gate din, sai da ya kalleta sannan ya ja motar suka shiga cikin katon gidan. Gaban entrance ya faka motarsa ya bude ya fita sannan ya zagayo ya bude mata ba tare da yace komai ba, ita ma din bata jira yace ba ya sauko da kafafuwanta ta fito. Kato gida ne mai kyau gaske an kawata ko'ina da flowers an masa kwaliyar zamani gwanin burgewa.
Hannunta ya rika ya fara takawa tana biye da shi har yasa key ya bude kofar ya shiga tare da ita. Tsaye tai bakin kofa ganin babu alamar mace tana rayuwa a cikin gidan, sai ya juyo ya kalleta, hakan ya bata damar janye hannunta daga rikon da yai mata. Sai ya dawo kusa da ita ya tsaya ita kuma ta daga kai tana kallonshi, ko bata fada masa ba ya san abun da take nufi wanda hakan kuma ba halinsa ba ne, ko ma halinsa ne shi me zai yi da teenager irinta. Yana kokarin yi mata magana wayarsa tai ringing, ciro wayar daga aljihun wandonsa ganin sunan Hajiya yasa shi daga kai masa ya sauke sannan yai picking.
“Sirleem ban isa da kai ba ne? Ban isa na maka magana ka ji ba?”
“Hajiya i swear to the seven heaven zan dawo gobe, ba gurin Mansura na je ba, wani aiki ya kai ni”
“Na ai dai fada maka karka wuce yau ko gobe, wato mallakar da take maka ta fara yawa har zaka bar garin Yola kaje gurinta ba tare da ka sanar da ni ba ko?”
Yayi shiru dan be san abunda zai ce mata ba kuma.
“To ya maka kyau ka cigaba da abun da kake karka fasa, taya dan albarka zai kula yarinyar da mahaifiyarsa bata so? Ka cigaba karka fasa”
Kit ta kashe wayar cike da fusata, sai ya sauke ajiyar zuciya ya busar da iskar bakinsa ya kalli Falmata.
“Ke ma mamarki na miki fada kamar ni?”
Ya rada mata a kunne, sai ta girgiza masa kai.
“Ni ba ni da Mama, Mamata ta rasu”
“Ayyyah... ”
Ya fada yana kallonta cike da tausayi, sannan ya cire talkamin kafarsa ya karasa cikin falon sai kuma ya juyo ya kalleta ya dago mata hannu.
“Karaso mana”
Ta girgiza masa kai.
“Look ni ba wani abu zan miki ba, za ki kwana nan ne gobe sai na maida ke gida”
Ya fada da muryar da zata ji yana ware hannayensa, sai tai saurin girgiza masa kai.
“A a ni ba zan koma ba, idan na koma Babana yanke ni zai yi”
“To shigo ki zauna”
A hankali ta fara takawa har ta iso cikin falon, ya nuna mata kujera sannan ya dauko remote ya kunna plasma dake falon, ya nuna mata wasu dakunan dake facing inda plasma take.
“Kin ga daki can idan zaki yi alwala da sallah ko fitsari, kuma a can zaki kwana, ni zan je masallaci yanzu”
Yana fadar hakan ya nufi hanyar fita, gaba sai tsoro ya kamata gidan ya mata girma ita kadai kuma tana ji a jiknta be kamata ta kebi da namiji duk kuwa da bata da tabbacin zai mata wata illar ko akasin haka. Sai da taji kara rufe kofar ta kara raina kanta sai ta zauna kusa da kujerar ta fara kuka a hankali tana tuna gidan, no matter irin wahalan da yake sha ta fi sakewa a can fiye da wani gurin, a yanzu ta kara nadamar guduwa da tai, tunawa da yace zai maida ta gida. Har yai sallah ya dawo tana nan a inda ya barta banbanci dazun da yanzu shine a yanzu rabe take jikin kujera tsakanin dazun da ya fita ya barta a tsaye. Be ce mata komai ba ya karasa inda take zaune ya rika hannunta ta mike tsaye sai ya nufi dayan dakin da ita.
“Dan Allah karka min komai dan Allah ka rufa min asiri”
“Waya fada miki idan na kebe da mace iskanci nake wai? Me zan yi da ke?”
Ya fada a tsawace duk ta wani hada mishi zafi, ga fadan da Hajiya take da shi ga fitar da Mansura tai da Yasir yanzu kuma tana son kara masa wani ciwon kan. Ba shiri Falmata ta sha jinin jikinta.
“Wuce kije ki yi sallah na ce”
Ya daka mata tsawa, da sauri ta wuce ta shiga dakin mai kama da na mata, an tsara komai an jera furniture ga wani kyakkyawan zanin zago an shimfida. After ta shiga ya karasa shiga ya kunna ac ya karasa gaban windows din ya dage labulayen sannan ya bude mata kofar bathroom. Ba tare da yace mata komai ba ya juya ya fice ya sakawa dakin key daga waje.
Zaunawa tai a kasa tana hawaye tana kallon dakin da bata taba mafarki wata rana zata kwana a irinsa ba, sai da ta ji ana kiran sallah isha'i sannan ta tashi ta shiga bandakin, sai ta rasa yadda zata kunna fanfon dan domin bata saba ganin irinsa ba bata taba amfani da irinsa ba. Har ta juya zata fita sai kuma ta dawo ta kai hannunta ta murda sai ta ga ruwa ya fara sauka.
Fisari ta fara yi sannan tai alwala ta kuma tara hannunta ta sha ruwan ta fito. Dankwalin da ke kanta ta cire ta shimfida ta fara rama sallolin da ake binta sannan ta gabatar da isha'i.
FADIME POV.
sai kusan magariba Fadime ta farka, gaba daya mafarkinta na abun da ya faru ne, duk mutumen dake shigowa suna Allah kyauta sai dai su ganta tsakar gidan tana sharar bachin wahala. Amo na aiki tana kallon Fadime da tunani kala kala wasu ranta, ita kanta a yanzu ta yarda Fadime ta hadu da iska da suka fi nata karfi to ga zahiri ta gani, bayan nan kuma ga wutar da ta saka mata an cire mata. Jin tai yatsanta na zafi kamar wutar, wanda hakan ke nuna alamar a cikin kuryoyin da take ajiya akwai wacce masu ita suka matsanta da addu'a da kuma neman taimako, kwayar da ke hannunta ta aje ta tashi daga gaban murhun ta nufi dakinta. Dukawa tai karkashin gado tsobuwar kwaryar da take ajiya a ciki ta bude ta dauko wani abu mai kama da laya tana dubawa, sai jin zafin tai yana shiga har cikin kanta, kan ta ankaro ta soma ganin daki na juya mata sai zafin ya game ilahirin jikinta, can cikin kanta ta soma jin wasu muryoyi na kiranta duk da bata san inda kiran ke fitowa ba amman sai son tafiya take. Da sauri ta fito waje ta nufi bandaki ta warware zaren ta daga yar tsokar marar kyau ganin a sama ta wurga iya karfinta, a maimakon ta fadi kasa ko ta fada wani guri sai ta zama yar tantaba yar karama tai sama sosai zuwa ga mai ita.
Daga ita sai ire-irenta suke iya ganin kurwar da ta kakareta ci.
Masai ta bude ta jefar da zaren ta fito tana jin wata rahama na sauko mata.
‘Lallai wannan kurwa ba ta ci ba ce’
Ta fada a ranta, a fili kuma maganin da Inna ta aje gaban Fadime take kallo, tana ganin Inna ta shige daki tai saurin isa gaban Fadime ta saka hannunta tana taba ganin, ba karamin dadi ta ji ba na samun sa'ar lalata aikinsa, daman can idan maye ya taba magani baya aiki komai aikinsa kuwa musamman idan na maganin mayu ne.
“Sha za ki yi Fulani?”
“Eh maganin mayu ne Inna tace min”
“Ai wlh kam sun yi yawa yanzu ko'ina Allah dai ya kyauta”
Ya mike tsaye ta karasa gaban murhu ta gyara wutar, sannan ta koma dakinta ta dauko hijabi mai kaloli ta saka ta fice da sauri daga gidan.
Bata yada zango a ko'ina ba sai gidan aminiyarta Lami, tana yi sallama Lami taja ta sukai cikin bukkarta dan kar kowa yaji abunda za su fada.
“Lahiya kike kau Amo”
“Ina lahiya Lami, kurwa nan da nace zan sai da miki na sake ta yau?”
“Saboda me?”
“Wallahi ina zaune na fara jin wuta da azaba, daga gani gurin wani babban malami suka kaita, dan har kirana yake, da asiri ya tonu ai kara na sakar musu kurwar ƴa”
“Kai kiken Amo baki da juriya Wallahi, ai da kin gwada rikewa ki gani, ba a saurin saki fa yanzu, ko kuma ki sassauta mata daurin ta samu lahiya suna barin gurin mai magani ki kawo min ita na yanke shegiya”
“To nikam na sani, ke ai kika maida abun wasa da kin bani kudi da yanzu na siyar miki ita, kuma Wallahi mai garita, daurin da na mata har wani naso take”
“Aikin gama ya gama tun da kin sake, amman Wallahi da kin sha kudi, kuma irin wannan cikin ruwa zaki ajenta saboda mai kitse kin san bata son zafi in dai ba yankawa za ayi ba, saboda gudun irin haka, kila kin aje ta guri mai zafi azaba ta yi ma macce yawa dole aje neman magani”
“Aa Wallahi cikin kwarya na aje ta, ni yanzu damuwa ta Fulani ce, an cire mata wuta?”
Lami ta rike baki.
“Dazun aka kawo min labari wai anganta da kan maciji”
A nan Amo ta kwashe labarin duk abunda ya faru ta fada mata.
“To ai ba gajiya ake ba, ki sake aika mata wutar idan kuma kika samu sa'a ki kame kurwar daddake mata kai hankali ya juye”
“Ai in bata ciwo gareni ba zata mutu, dan na samo mata wani miji mai kashe mata, ance duk mace da ta aureshi sai ta mutu ina tunanin shi ma maitar yake amman ta sayarwa dan ance kudi gareshi sosai, kin san masu saidawa sun fi arziki ba kamar mu ba”
“A ina? Kuma?”
A nan bata kowaye amiyar ta ta komai ba.
“Bari na yi sauri na koma na bar girki kan wuta”
“To ko kam kar Malam Jaure ya dawo ya fara nemanki, bari sai dare mu hade gurin rawa”
“A a yau ba ni fita tun da dakina yake, sai jibi”
Daga haka tai mata sallama ta dawo gidan a guje, ta shige cikin daki ta cire hijabin ta aje ta fito waje tana kallon kofin maganin da Fadime ta sha magani da shi. ta san ta sha ne kawai amman ba zai mata aiki ba tun da saka masa hannu.
Bayan sallah magariba Bappa ya shigo shi da wani abokinsa Malam Isuhu Inna ta shimfida musu tabarma aka kira Fadime ta fito daga bukkar Inna bayan ta kare sallah magariba ta zauna saman tabarmar.
“Kina da alwala?”
“Eh yanzu nai sallah”
Ta amsa tana kallon wata doguwar takadar da Malam Isuhu yake budewa.
“To Malam Bissimillah”
Malam Isuhu ya matso kusa da ita ya haska fitilarsa yana ya fara karanta mata ayoyin kona aljanu, tun da aka fara karatun Fadime take zaune guri daya tana saurare, idan ya karanta ya karanta sai yace
“Wanene?”
Sai Fadime tace
“Ni ce Fulani”
Tun yana yi yana tsayawa ya tambaye ta har ya gaji ya daina sai karatun kawai yake mata, da Fadime ta ga abun nasa ba mai karewa ba ne sai ta fara lankwashewa tana burkice ido kamar da gaske aljannu ne suka zo.
“Muna aljanu gamu nan mun zo, mu ne”
“Ku suwa?”
“Mu aljanu”
“Miye sunanka?”
Ta dan yi shiru tana tunanin sunan da zata fada, can kuma ta fadi sunan Bappa.
“Sunana Sama'ila”
“Miyasa kika shiga jikinta?”
Mutumen ya tambaya.
“Saboda.....saboda... Muna son mu bada magani”
“A ina kuka hadu da ita”
“A daji..... ”
“To ku fita daga jikinta ko na kona ku”
“Ba zamu fita ba”
Ta fada tana ta mulmula a kasa kamar wata mai aljanun gaske, sai mutumen ya cigaba da karatunsa da nufin kona su, Bappa kuma ya shiga dakinsa ya dauko bulalar dorina ya shada mata, a take tai saurin tashi ta zuba da gudu zuwa wajen shanun da suke gidan.
“Mun fita ba zamu sake dawowa ba”
Malamin yace.
“Karya suke haka suke idan suka ga ana kona su”
Bappa ya bita har can ya zuba nata wata bulalar yana fadin
“Ku fita daga jikinta yanzu nan”
“Bappa sun fita tun dazun ni ce dan Allah ka tsaya”
Ina Bappa be yarda Fadime bace sai auna mata bulalar yake, tun tana fadin sun tafi har ta fara kiran Inna ta ceceta.
“Inna nice Wallahi ni ce dan Allah ki zo kar Bapppa ya akashe ni”
Inna ta zo da sauri ta rike bulalar tana fadin.
“Sun fa tafi Fulani ce kake duka”
Sai a lokacin Bappa ya sarara mata bayan ta sha buloli da sunan aljannu.
HAJIYA BABBA POV.
Tsananin mamakin da yake fuskarta ya wuce misali, ta san Jarma ba zai mata karya ba, amman sam bata gane inda labarinsa ya dosa ba, Fadime Falmata Sardauna za su watse musu shiri?
“Wacace Fadime?”
Ta tambaya a fili tana kallon Jarma.
“Ni ma abunda na gagara sani kenan, balle kuma Falmata da Sardauna, amman ni ina ganin kamar Sardauna na Yola yake nufi”
“Sardauna ai yana da nisa da Sarautar nan, balle nai tunanin haka, idan na shi ne to su waye Falmata da Fadime?”
“Abun da na gagara sani kenan, kuma na yi wauta ko da yake tsoro ne a ya hanani tambayar ko me suke nufi, kuma ita Ammy ai Zainab ne sunanta ba Fatima ba balle nai tunanin ko ita ce....”
Be karasa ba Hajiya ta daga masa hannu alamar yai shiru sai dai har lokacin mamaki be bar fuskarta ba. Kwankwasar dakin da ake take saurari kamin ta ji muryar Nana.
“Hajiya Hajiya....”
“Daughter ke ce?”
“Ni ce”
Hajiya ta tashi da kanta ta bude mata dakin tana kokarin kirkiro murmushi.
“Daughter na ya aka yi?”
Ta tambaya tana rike da kofar dan bata son Nana ta hango Jarma a dakinta, duk da ta san ya saba shigowa sai dai rufe dakin da makulli da akai zai saka shakku a zuciya.
“Wayarki za ki bani sai na kira wanda na ce miki ina son ya zama driver na”
“To tsaya nan bari na dauko miki”
Hajiya ta rufe kofar ta dawo ta dauki wayar sannan ta koma gurin kofar ta bude ta mika mata.
“Tafi da ita can idan kin gama ki bawa Karima ta aje min”
“Okay”
Ta karba ta juya cike da jindadi, dan ta san Number AA na cikin wayar Hajiya, saboda ta ari wayar shi ta kira Hajiya da line, duk kuwa da bata da tabbacin number tana nan har yanzu ko an goge, ba dan zata iya ganewa number ba sai dan ta gwada sa'arta.
Bayan ta wuce Hajiya ta sake rufe dakin ta dawo ta zauna. Sai Jarma ya rage murya yace.
“Ashe Nana ta fara dan hali?”
Hajiya ta yi murmushi.
“Ai har abun da yafi dan hali sai Nana ta yi, matukar ina raye ƴaƴan Ammy ba za su taba albarka ba Wallahi har a abada kuwa, yadda take son ganin bakincikina ita sai na ga nata kukan”
Ta karasa tana wane kashe ido zuciyarta cike da kiyayyar Ammy.
*FULANI -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence to 08036126660 ƴan nijar za ku tura 500cf to +22790165991*
17
“Fulani ki jefar da tulun ta can sai ki gudu”
Cewar Inna cike da damuwa. Fadime ta girgiza kanta da ya kusa fashewa saboda ciwo, ga kukan da take idonta har ya kumbura.
“Aa sai na shiga gida”
Bappa ya nuna ta da sandar hannunsa.
“Wallahi baka kai min masizi cikin gidan, ka jafar da si ka gudu aka ce maka”
Ta kara fashewa da kuka, ta rasa yadda za tai su fahimce ta, gashi jikinta ya gama mutuwa ga wani uban zafi da take ji, kukan har ya fara zuwa mata ba hawaye, a lokacin ne ta fara yarda ta fara bankwana da duniya, ta sanj Bappa ba zai bari ta shiga gida da maciji ba, ita kuma ba zata sauke shi ya cutar da ita ba.
Har rana ta soma dagawa ana abu daya, ita ta ki ta jefar da tulu, Bappa kuma ya ce ba zata shiga gida da maciji ba, aka rasa mai taimakonta duk wanda ya tunkaro ta sai ya ga kan maciji kato ya sako masa ido.
“Ina ganin abun da yafi aje can garin su Ahmadu akwai wani mai majizai kira shi ya zo ya dauke mata wannan lalura”
Malam Adamu ya fada yana saka hannunsa ya kare fuskarsa daga hasken ranar da ke dukan su, domin rana ta bude sosai wanda hakan ke nuna biyu tayi ko ma ta gota. Fadime na zaune kasa har ta fara wata ramar wahala, muryarta har ta dakishe ga wani uban gumi da take. A yanzu kam Inna ta yarda da mafarkin da tace mata tana yi har ta fadawa Bappa.
A dole dai da aka isa har garin hayin fari, aka dauko wani mutum nai wasa da maciji akan ya zo ya dauke tulun.
A lokacin ne Fadime ta gane ashe tana da ragowar karfi, da mutumen ya tun karota sai ta mike tsaye ta fara tafiya wata hanyar tana kuka, hannunta daya na rike da tulun da ke saman kanta dayan kuma yana rike da zanenta daya kusan subucewa.
“Wallahi ba zan bayar ba,