Showing 96001 words to 99000 words out of 286946 words
masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
25
*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt bank, then send the evidence to 08036126660*
FADIME POV.
Sai da ta saka ruwa ta wanke bakinta sannan ta kama hanyar gida tana tafe tana kuka kamar wata yar 6 years, ta yi wa Liya Allah ya isa ya fi a kirga tana tafe tana tofar da yawun da jini be gama mata zuba ba. Sai da ta iso kofar gidansu sai ta kara bata fuska tana son saka sabon kuka, sai dai jiyo muryar Amo da tai yasa ta manta da wani ciwo da taji a baki, sanda ta fara yi kamar wanda zata sa ci wani abu ta leka cikin gidan, Amo ce tsaye bakin kofar bandakin ta rike ciki sai tsalle take jini na fita bakinta.
“Wuta jama'a wuta a cikina, jama'a ku taimaka min wuta”
Inna dai na tsaye bakin bukkarta tana kallon ikon Allah, Amo kam sai yawo take cikin gida tana fadin.
“Wuta a cikina jama'a wuta a cikina wayyo ni Allah ya na shiga uku Fulani ki yafe min, mutuwa zan yi”
Wani irin tsalle ta daka ta dire kasa ta mulmula tana kuka, idan tai tari babu abun da ke fita bakinta sai jini, kana ganinta kasan bata cikin hayyacinta. Tashi tai zaune ta cire rigarta ta kwance zanen ta koma daga ita sai under skirt, ta rike cikin sai ihu take. Da sauri Fadime ta juyo ta dawo daga waje ta tsaya tana zaro ido kamar za su fito waje.
“Kenan ita ce mayyar? Ashe da gaske ne da mutanen nan suka ce ta kama musu da?”
Ta sake bude baki mamaki ya gama kasheta, sam bata dauka idan ta dawo gida Amo zata tarar a matsayin matar da Wasim ya daka ba. Jin ihun Amo yasa ta sake lekawa, sai ta hangota tana ta rawa.
“Wuta a cikina ki taimaka min Aisha wuta a cikina, yau na ga bala'i na hadu da da ukuba, yau na ga wanda ya fi karfina, Fulani ki yafe min dan Allah, Allah ka yafe min ka taimake ni na tuba ba Allah”
Ta nufi gurin Inna tana dafe da ciki sai kuka take irin kukan na azaba na fitar hayyaci wanda ya wuce ayi masa hawaye ita kadai ta san irin azabar wutar da take ji a cikinta gidan ma daker da sudin goshi ta kawo balle kuma yanzu da take jin abun kamar yana kara mata. Tana matsawa Inna ta kara matsawa gefe tana mata kallon tsoro domin ita sam bata ma gama fahimtar abun da Amo take ba, daga shiga bandaki ta fito sai ta fara rawa tana fadin wuta a cikinta. Kan kace kwabo gidan ya fara cika da mutane saboda irin ihun da take tana fadin wuta a cikinta.
“Ki yafe min Aisha, watan tonon asirina ya kama, yau duk wanda na ci sai na amaryar da sunansa, Wallahi wuta ce a cikina dan Allah ku min rai ku yafe min, yau na shiga uku na ga bone bone ta gan ni”
Wani irin numfashin wahala take tana dafe da ciki gaba daya ta kasa natsuwa jin take duniyar na juya mata ta ma kasa gane inda take.
“Fulani ki yafe min dan Allah Wallahi ba zan kara ba, na shiga uku wuta a cikina jama'a wuta wuta wuta”
Fadime najin ta sake ambatar sunanta ta auna nesa da kofar gidan dan kar ma Amo ta ji kamshinta. Cikin gidan be wadatar da ita ba ta nufo waje rike da cikin kamar wata mahaukaciya.
“Wuta a cikina jama'a, ku taimaka min”
Haka ta nufi mutanen dake tsaye kofar gidan tana fadi, kowa yai chirko chirko yana kallonta, sai wadanda suka shiri da ita ne suka nufota suna fadin lafiya.
“Ba lafiya, ba lafiya wuta a cikina, na ci Shamsu na ci Maniru, ku ce Zainabu ta yafe min yaron nan shi kadai ta haifa kuma ni na ci shi Wallahi...”
Tsayawa sukai cak kamin su juya da sauri kowa ya koma baya sun kallonta, ita kuma ta mike tsaye tana kallon Inna wacce ta fito rike da zane zata daura mata ta ce.
“Aisha ki yafe min, Wallahi ni na cinye ƴaƴanki, ɗa tara ni na cinye su, wasu sun ba su zo duniya ba, wasu kuma sai sun zo, Fulani ce kawai ta gagareni, shanun Malam da suke mutuwa idan Fulani ta fita da su kiwo Wallahi duk ni ce, yau na shiga uku yau komai sai na fada, jama'a wuta a cikin cikina”
Inna tsaye tai a gurin kamar a datasa, idonta ya cika da hawaye zuciyarta kuma ta cika da mamaki da tsoro.
“Ni na cinye yayanki, na ci ɗa tara, idan dare yayi ni ake hawa saman rufin dakinki ko na Fulani nai rawa, har makota ina lekawa, wata rana tare da Laraba muke, ita ma ta ci na ci, na hada kai da ita saboda na samu kama kurwar Fulani amman innaaaaa abun ya gagara yau na jawa kaina bala'i, Wallahi wuta ce a ciki yau na shiga uku”
Ta buga hannunta a kasa tana tarin da yake kokarin hanata magana.
“Yaron daga ya kawo ni a babur na cinye shi, na kama kurwa wata mata daga hawan mota tana can na aje a dakina, na cinye dan makocinmu Dahiru na cinye kanensa tun be zo duniya ba, duk barin da Aisha tai da yayanta da suka mutu ni ce Wallahi ni ce nake cinye su”
Ta mike tsaye tana ta rawa, ba rawa ta jindadi ko murna ba, irin rawar nan ta azabar ciwo domin ita kadai tasan abun da take ji a cikinta, kamar an zuba fetur an kunna wuta haka take jin cikin mata, yadda take fadar abubuwan da take ita kanta bata san tana yi ba, domin idan wutar ta motsa mata ta laso mata zuciya sai tai ta barin zance.
“Ku ce wacan mutumen ya yafe min dan Allah, Wallahi ba zan sake ba, jama'a wuta a cikina, na ci Tanin na ci Murja yar gidan Almajiri, daga na aike ta na tankwashi kanta na kama kurwarta na cinye ta, na ci yar gidan Hajiya Ayawa ta birni na kama mai gadinsu, kurwarsa na cikin dakina”
Kusan duk wanda ta ci ko ta kama sai da ta fada, ta saka hannu biyu ta dafe cikinta sai kuka take, idan tai yunkuri kuma sai aman jinin. Sosai mutanen da take fadar ta ci yayansu suka so afka mata da duka Dattijawan da suke gurin suka hana, Wani makocinsu ne ya hau babur dinsa dan zuwa fadawa Bappa halin da ake ciki. Ba iya mutanen da ta ci ba har mutanen da suke maitar tare sai da Amo ta fada. Hajjo na tsaye ta rasa inda zata saka kanta sai kuka take.
“Kaka ta bawa uwata Maitar nan, uwata ta ba ni, ni kuma na bawa tun da ban haifa ba? Yau na yi leke na ga mugun abu, wuta ce a cikin tana ta ci kun ganta”
Sai nunawa mutane cikinta take tana ta tarin jini, kowa sai matsawa yake nesa da ita.
“Ina zama mage ina zama doki har kadangare ina zama, ina zama jaki ina zama bakin kare, idan dare yayi a filin can nake rawa, jama'a wuta a cikina”
Ta karasa a galabaice. Inna dai na tsaye tana kallon ikon Allah hawaye sai zuba suke mata, bata jin dacin wata magana kamar wacce ta ji daga bakin Amo ba a yau, ta cinye mata ɗa tara, saboda ita bata taba haihuwa ba bata san zafin haihuwa ba, ka dauki ciki wata tara ka haihu, wasu ta yi rainonsu wasu kuma tun suna kanana suke mutuwa, ko da rana daya Amo bata tausaya mata ba Fadime ma dan ta gagareta ci ne.
Juyawa Inna tai ta koma cikin gida tana jin wani irin zafi da bakinciki a ranta, uwa ce kadai kan iya labarta yadda bakinciki rasa da yake, balle ita data rasa yara har tara, zaunawa tai a kujerar dake tsakar gidan ta fashe da wani irin kuka, ta sani ko da zata yanka Amo a yanzu ta gasa namanta, ta soyata ba yaranta ba za su dawo ba, kuma ba zai goge bakincikin dake ranta ba. Tun ba yau Inna ta dade tana zargin Amo da maita tun a wani lokacin da suna fira take fada mata suna da maita gado ga kuma mafarkai da take kala-kala akan amman bata taba tabbatarwa ba sai a yau da idonta ya gani zahiri, hannu ta saka ta dafe zuciyarta tana jin wani irin zafi a kirjinta, ta haifi yara goma sai Fadime ce ta tsaya, kuka sosai Inna take tana ayyana yadda wasu yaran suke mutuwa a hannunta da irin azabar da suke sha kamin su mutu, da kuma ita ma irin wahalar da take da wasu. Shigowar wasu makotan ne yasa ta tsagaita kukan da take tana jin wani irin son Fadime na kara fadada a kirjinta ganin ita kadai ta rage mata a rayuwa.
“Ki yi hakuri Allah ya saka miki Allah ya isar miki”
Shi ne mafi yawan abun da mutanen ke fada, ita kam ta kasa ce musu komai, kukan kawai take hawaye na mata zuba domin ita kadai tasan zafin da take ji a ranta. Da yamma lis, Bappa ya iso, shi ya riko Amo ya shigo da ita cikin gidan, kana ganin fuskarsa kasan babu walwala a tare da shi, domin ko baka son mace baka son ta fita waje daga ita sai dan kanfai balle matarka ta sunna ga kuma tonon asirin da take ta yi ma kanta. A tsakar gidan ta fadi tana ta ihu har lokacin ta kasa dawowa hayyacinta tana ta faman rikon ciki tana fadin wuta, har kamo hannun Hajjo take tana kaiwa a cikin nata.
“Allah ka yafe min na tuba Allah, ba zan kara ba, wayyo wuta wuta a cikina na shiga uku, Fulani ki yafe min ki ce masa na bari”
Babu irin tambayar da Bappa be mata ba ina ta samo ciwon me ke damunta? Amman ta kasa bashi amsa sai fadin take wuta a cikinta domin bata cikin hayyacinta. Can ya koma gurin Fadime ganin tana ta ambatar sunanta.
“Ke kin san wani abu ne?”
Fadime ta yi saurin daga hannunta sama.
“Aa ni ban san komai ba, Allah ya tsare”
Yadda tai da ido sai ka rantse da Allah bata san komai ba, bayan labarin na kasan halshenta, sai dai tana tsoron fada kar ta sha duka gurin Bappa.
Bappa fita yai daga gidan gaba daya ya koma can gefe ya kira wani Kawunta bugu biyu ya dauka.
“Assalamu Alaikum Kawu Manu”
“Wa'alaikassalam, Sama'ila ya gidan ya kowa?”
“To Alhamdulillah, Kawo ina bukatar ganinka yanzu idan kana da dama ka zo dan Allah”
“Lafiya dai?”
“Lafiya amman ba lau ba ka daure ka zo dan Allah”
“Dare ya fara yanzu haka na yi alwala sallah magariba, indai ba wata matsala ce babba ba ka bari har gobe biyo mota na zo”
“Aa ka zo dai yanzu Kawu”
“To shikenan idan mun gama sallah zan kamo hanya yanzu”
“To Allah kawo ku lafiya”
Bappa ya sauke wayar daga kunnensa tare da sauke ajiyar zuciya, sam be ji dadin abunda ya faru ba sai dai be isa ya hana komai ba, ba tun yau Inna ta dade tana masa maganar zargin da take na Amo shi kansa ya dade da sanin abun da take sai dan gudun kar ya budewa Inna da take kishiyarta da kuma sauran mutane damar fada ko aikata wani abu yasa be taba nuna yana zarginta ba idan ma Inna tai sai ya kwatsuleta saboda be taba gani da idonsa ba, sai dai irin tonon asirin da tai wa kanta a yau da kuma fadar irin mutanen da ta ci ya canja masa tunani, an labarta masa komai tun kamin ya iso bayan ya iso kuma ya ga komai a idonsa. Dawowa yai cikin gidan a lokacin Inna na tsugune tana alwala Fadime kuma na zaune gefen bukkar Inna ta rafka uban tagumi tana kallon Amo dake ta dalalar da jini a baki ta rike ciki sai kuka take muryarta ma bata fita. Inna sai da ta gama alwalarta sannan ta zubawa Bapppa ruwa a butar ta kawo gabansa ta aje, fuskarta kawai yake kallo yadda idonta ya kumbura kana ganin kasan ba karamin kuka ta sha ba.
Shi kansa da yake uba abun be masa dadi ba balle kuma ita da take uwa ta san zafin daukar ciki da haihuwa. Bukkarta ta shiga ta dauko tabarma ta shimfida waje ta saka hijabinta ta fara sallah magariba. Fadime na ganin haka ta tashi itama ta dauki wata karamar buta tai alwala ta shiga bukkarta ta dauko hijabinta ta saka ta tsaya kusa da Inna ta kabbarta sallah.
Daga garin Dan-isa zuwa garin Bandalo tafiyar awa daya ce har da yan mintuna a mota, balle kuma su Kawu Manu da suka hau babur din dansa suka kamo hanya saboda babu motar da zata je garin Bandalo a yanzu. Tara saura kwata suka iso garin, ba shi da aka kawo ba har dansa daya goyosa a babur din zullum abun da za su ji ko su tarar yake, sun sani duk abun da zai saka Bappa ya nemi ganinsa ba karamin abu ba ne a matsayinsa na uban daya rage ma Amo a yanzu. Ko da suka iso Bappa na tsaye bakin kofar gidan tare da wasu abokaninsa biyu, sai da ya mika musu hannu suka gaisa sannan yai musu iso.
“Kawo Manu Bismillah”
Bappa ne a gaba Kawu Manu na bayansa tare da dansa suka shiga cikin gidan, tun kan Bappa ya labarta masa komai ya fahimci ba lafiya ba, ganin Amo a tsakar gidan Hajjo na gafenta tana kuka, Inna da Fadime kuma suna kan tabarma zaune fitilar aci balbal na gafensu. Amo na ganin Kawu Manu tai saurin mikewa tsaye ta nufo inda yake tana fadin.
“Kawu ka fada ma Fulani ta fada masa na daina dan Allah ta cire min wutar nan, ba zan sake maitar ba zan daina Wallahi”
A take gumi ya karyo masa, ya juya ya kalli Bappa sai kuma ya saka hannunsa aljihu ya haska Amo, gaba daya ta fita daga kamaninta ta canja kamar ba ita ba ga wata uwar ramar wahala da tai har lokacin kuma idan tai tarin sai jini ya fito ta bakinta, sai wani leko halshe take waje tana zaro ido kamar sabuwar mahaukaciya, tun da take a rayuwarta bata taba shan wahala ko shiga jalala irin wannan ba. A tsanake Bappa ya labarta Kawu Manu komai sannan ya dora da cewar.
“Ban san abun da ya faru ba, Aisha ta fada min cewar daga bandaki ta fito wahale tana ta aman jini tana ihun wuta a cikinta kamin ta fara tonawa kanta asiri, daman kuma ba tun ba na dade da fahimtar abun da Amo take yi, sai dai ba ni da hujjar fadin hakan saboda ban gata ido da ido ba, amman yanzu ita da kanta ta tonawa kanta asiri”
Kawu Manu ya gyara tsayuwarsa yana kallon Amo kamin ya haske Fadime da fitilarsa mai shegen haske.
“To ita wannan da take ambatar sunanta bata san komai ba?”
Inna kamar tana jira ta mike tsaye tana nuna shi da yatsa.
“Kurwar Fulani kur Wallahi sai dai ku ci kanku, kuma duk abun da Amo tai min na bar ta da Allah shi zai saka min”
Inna ta karasa cikin kuka tana jin wani irin zafin a ranta, wani murmushi Kawu Manu yai ya tabe baki har lokacin fitilarsa na haska Fadime.
“Inna ki yi shiru, Allah shi zai saka miki Allah ya isar miki”
Fadime ta fada tana sharewa Inna hawayenta, ita kuma tana wasu hawayen ganin zubar hawayen Inna yasa ta ji wani irin no matter how mother is ɗa ko ƴa baya son ganin kukan uwarsa, ganin yadda yake ta kallon Fadime yasa Inna ta mai ita bayanta.
“Fulani bata ciyuwa Wallahi sai gani sai bari, kurwarta kur mugun abu ya bi dare ku ga abun ku a kanku”
Wani dogon numfashi Kawu Manu ya sauke sannan ya juyo yana kallon Bappa.
“To yanzu ya ake ciki? Kai kana ganin wannan abun da take yin kanta ne?”
“Kawu ga zahiri kana gani, shiyasa na kiraka ka zo ka tafi da ita”
Cewar Bappa, sai Kawu Manu yai wani murmushin takaici.
“Ka kyauta Sama'ila, duk yadda ake ka yi, Allah ya saka maka da alheri, ke kuma ki jira sakamakonki”
Ya karasa yana haska Inna d Fadime, sannan ya kama hannun Amo.
“Ba ni da sakamako sai alheri, sherinka ya bika, ka ga mugun abu kai da yarka can mukan alheri zamu gani da yardar Allah”
Uffan be sake ce mata ba, yana dai rike da hannun Amon har suka fita, sai da dansa ya fara hawan babur din sannan ya dora Amo a baya, hajjo ta hau sannan shi ma ya hau a baya suka kama hanyar garin Dan-Isa.
FALMATA POV.
Sai da suka yi bachi sannan ta fito daga dakinsu, a falo ta samu Ammy da Jekadiya da kuma wata bakuwar suna gaisawa, har inda Ammy Falmata ta karasa ta risina kasa ta kwashi gaisuwa sannan ta mike tsaye ba tare da ta ji amsawarta ba, daman ba amsarwa take jira ba ita dai muradinta ta gaishesu ta tafi gida ganin dare ya soma yi sosai gashi a kafa zata je, sai ta fito waje ta kara tsinkewa ganin hadari ya hada ko'ina a garin iska sai kadawa yake. Cira kafa tai tana kallon sama gabanta ya fadi yadda hadarin ya hadu yana da wahala ta iya isa gida ba a sako ruwa ba. Ta baro gate din gidan sai ta tsinci kanta ita kadai a unguwar sai wata mota dake can gefen titi a fake, arzikinta daya unguwar manyan mutane ce ko'ina a haskake yake kamar wani gurin taro. Daga nesa aka dallo mata fitilar motar dake fake har sai da ta tsaya cak sai kuma aka kashe, aka sake dallo mata aka kashe sosai hakan ya firgitata wanda ya saka har ta juyawa ta waiga bayanta tunanin komawa take a masarautar, ganin hakan yasa Sirleem ya bude motar ya fito ya nufo inda take tsaye, tun kan ya