Showing 222001 words to 225000 words out of 286946 words

Chapter 75 - Fulani Book 1 Hausa Novel Complete

20 Dec 2024

920

abun da Iya take aikatawa amman bata fadawa kowa ba, ta bar mahaufiyarta tana aikata abubuwan da ba su dace ba, ciki har da cutar da shi da yayansa.
Ko kadan be ji ya gundura da tsayuwar ba balle har ya nemi gurin zama, yana tsaye sai safa da marwa yake yana tuna wasu abubuwan da su kai ta faruwa da shi, sai a yanzu ya gane hikimar Ammy na korar Iya a gidan tare da Zainab saboda ta talaka mata auren Zainab din, a yanzu kam jin yake da sanin Zainab Iya tai masa tayin auren saboda ta auri yarta.
Kamar dazun a yanzu ma nesa da shi suka aje motar Jekadiya ta saka Zainab dake sanye da rigar bachi ta dora bakar riga sama, ita kanta yadda ta hango fuskar Shattima sai da gabanta ya fadi, tana ta tunanin dalilin kiran duk da ta san ba zai wuce akan Fadine ba, sai dai bata ga ta inda ta hada da batan Fadime ba bayan ita bata masarautar.
Gabansa ta karasa ta dan risina masa tana gaishe shi.

“Me kika ce a fada min?”

Ta maimaita irin abun da Wasim ya fada mata.

“Hakan na nufin kin san wani abun akan batanta kenan?”

“Aa ban san komai ba”

“Ban gadi daidai ba kenan?”

“Aa ban ce haka ba, ka gafarce ni amman baka fahimce ba, bana ni hannun a batan ta kuma ban san komai ba ka yarda da ni?”

Shattima ya kura mata ido yana mata wani kalar kallo da be taba mata irinsa ba, gaba daya sai ya ji tsanarta ta cika masa zuciya.

“Ta ya zan yarda da ke? Kina da wani abu ne da zai saka na yarda da ke? Na san ki za ki iya yin komai dan ki cutar da yarinyar nan saboda ta tona muku asiri”

Sakaka Zainab tai tana kallonsa, wani kalar muzanci da na kusantantar ta.

“Ko dai ki nemo inda wannan yaron yake ya kawo Fatima ko kuma ke ki fadi inda take ko kuma a tafi da ke gidan horo yanzu nan”

Zainab ta kasa cewa komai sai hawaye take.

“Jekadiya”

Jekadiya ta matso da sauri tana kara daga masa hannu.

“Ranka ya dade”

“A fadawa Alkali ya akai ta gidan horo”

“An gama ranka ya dade”

Jekadiya ta fada tana mikewa tsaye.

Zainab ta nuna kanta, hawaye na sauko mata.

“Ni... Shattima?”

Wani kallo ya watsa mata daga sama zuwa masa.

“Ke din wacece?”

Da sauri ta rufe ido tana jin kamar ya soketa da mashi.

“Saboda an bude miki hannu an miki gata an miki maraba har ya saka kike jin cewar ke din wata ce a masarautar nan? Wani ya fada miki magana yace ki fada min ba ki ji za ki iya fada ba har sai da aka aika neman yarinyar? Na saka a miki hukunci ki nuna kanki kina tambaya ta wai ke?”

“Tuba take ranka ya dade a yafe mata ta tuba”

Jekadiya ta fada, Zainab kuma ta hade wasu kalar yawu masu daci da suka tsaya mata a makoshi. Shattima ya juya a fusace ya nufi hanyar da zata sada shi da kofar fadar Ammy ta waje. Jekadiya kuma ta saka Zainab gaba zuwa wani bangare na gidan, Zainab na tafe hawaye na sauko mata.


FADIME POV.

Ataa bata taba ta ba har Aliyu ya dawo, yana ganinta zaune a falon ya san ba lafiya ba.

“Are you okay”

Ta daga masa kai tana labarta masa abun da ya faru. Karasa yai kusa da Fadime ya duka yana kallonta kuka take sosai tana kallon silin dakin kamar tana gani.

“Sannu”

Ta fada mata, sai ta kasa amsawa ta kasa ce masa komai.

“Zo ki kamata”

Daker da addu'a Ataa ta rika hannunta domin ta tsorata sosai da halin da ta ganta a dazun. Aliyu ne ya shige gaba ya bude mata kofar dakin bakin Ataa ta shiga ta ita, Aliyu ya mika mata ledar maganin ya fita ya dauko ruwa sannan ta balla maganin ta bata, ta bata ruwa sai dai komai sai ta ce mata ta yi take iya yi. A dakin Fadime ta kwana a sai da ko da wasa bachi be kusanci idonta ba, tana zaune shiruuuu idan ta gaji da zaman sai ta kwanta, idan jikinta yai mata tsami sai ta tashi, wani irin yanayi take ji mai wuyar fassara, komai ya ki mata dadi a duniya. Misalin 9 na safe Muhseen ya iso gidan sakamakon kiran da Aliyu yai masa, sai da suka yi magana da shi sannan ya shiga dakin ya dakin a hankali. Can karshen dakin ya hango ta zaune, ta abincin karyawarta na gefe bata taba komai ba ta kurawa silin ido idonta har sun fara wani fari fari alamar amakantar na son kamata. Kusa da ita Muhseen ya karasa yana kallonta can kuma ya taba jikinta sai ya ji shi da sanyi.

“Ina ina jina?”

Ta dawo da dubanta ta inda take jiyo sautin muryarsa.

“Yi magana fada min sunanki”

“Ina son na san sunana ina son na san ni wace irin halittace, ina son na daina ganin wannan duhun, ina son na daina jin abubuwan da na ke ji, ka taimaka min....”

Ta fada tana wani irin rirrike shi kamar zata shige a jikinsa sai kuka take ma ban tausayi. Juyowa yai ya kalli Aliyu.

“Zan tafi da ita asibiti”

Aliyu ya daga kafadarsa alamar ba matsala. Daman can ba wani son shigowarsa yake a gidan ba sai idan ta kama dole saboda Ataa a ganinsa har yanzu yana nan da sonta a ransa kamar da. Mikewa yai tsaye sai ita ma ta mike tsaye da sauri ta rike shi gam tana jin kamar ta taba rike wani makamancin haka, a kokarinta na tunawa ta ji kalar dariyar jiya, da muryar yara ana ta mata dariyar cikin kwakwalwa, take ta sake shi ta dafe kan tana ihu.

“Wayyo kaina wayyo ni kaina.... Ku taimaka min..... Dariya na ke ji cikin kaina.... Wayyo ni kaina...”

Ta fada tana wani irin kuka mai ban tausayi hawaye sai sauko mata suke.



_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number  09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
54

Ina mata wadan da suke son sayen kaya kamar su laces, atamfa, materials,shadda lace, normal shadda, atamfa lace, veil's, shoes and bags, da sauransu kuzo ga MAMAN AHMAD tazo dan tashare hawayenku kudai kunemeta ta wannan number 08032350261 banan kadai tatsayaba tanada kayan order kama dana kitchen,tufafi,kuma order ta Bata dadewa, akwai turaren wuta,kulacca,da sauransu

https://wa.me/qr/MYY56BH3RMFDG1



*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*



“Abun kamar na Iska”

Ataa ta fada.

“Damuwa ma na saka haka”

Cewar Muhseen yana kai hannayensa biyu ya rika kanta, sai tai tsit kamar ba ita ba.

“Kina na saurarena?”

Ta yi shiru.

“Idan kina ji ki daga min kai ba sai kin yi magana ba”

Sai ta daga masa kai idonta a rufe.

“Ki daina kokarin tuna komai kin ji?”

Nana ma kam ta daga.

“Ki dauka wacan matar da mijinta da suka tsince ki yan'uwanki ne, ni Sunana Muhseen likita ne ni, zan rika kula da ke ina baki magani, so kina son ki dauke ni a matsayin yayanki and daga yau sunanki ....Yasmin”

Ya fada bayan dogon nazari.

“Da zarar kin ji ance Yasmin to da ke ake sai ki amsa, kin ji? Kuma idonki ma zai bude kin ji?”

Ta daga masa kai a hankali tana kokarin kwantar da hankalinta.

“Yasmin”

Ya kirata murya kasa kasa, da farko sai ta ji kamar ba da ita yake ba, can kuma sai ta amsa.

“Na'am...”

“Good girl”

Ya juya ya kalli Aliyu da Ataa dake tsaye bakin kofar dakin.

“Zan tafi da ita asibitin idan ta kama a kwantar da ita zan kwantar da ita a can, idan kuma dawowa zan zan dawo da ita nan”

“No ka kaita gidan Mama Fulani kawai”

Aliyu ya fada, sai Muhseen ya hanye hannunsa daga rikon kanta da yake, ya kama hannunta. Ya fito da ita dakin zuwa motarsa, har gurin motar Aliyu ya bi shi ya fada masa.

“Duk abun da ake bukata ka fada”

Muhseen dai be ce komai ba ya bude mata gidan gaba ta shiga sannan ya zagaya ya shiga mazauninsa yaja motar. Daga gidan be tsaya da ita ko'ina ba sai asibiti, farkon abun da ya fara bincika shi ne kwakwalwarta, a tunanin idam hankalinta y dawo zata iya bayanin yadda akai ta rasa idon ko kuma irin maganin da take kai. Hotuna ya rubuta mata har guda hudu kuma masu tsada ya saka wani ya kaita aka dauki hoton abun da ke cikin kanta, akai mata gwaje gwaje, at first what he thought is ko ta yi hadari ne ta rasa tunaninta da idanuwanta domin hatsari babu abun da be saka wa, daga ya fara tunanin ko an dura mata kokin ne, kamin ya fara tunanin wata kila damuwa ce tai mata yawa.
Sai dai abun da ya bashi mamaki a duk hotunan da aka dauka da kuma bincike da yai be ga wani abu da zai iya sakata haka ba, komai na kanta kalau yake.
Amman saboda ya tabbatar yasa yai magana da wani kwararen likitan kwakwalwa, sai dai be samu dubata a ranar kasancewar yamma ta yi sosai, ya dai yi alkawarin dubata gobe idan ya shigo asibitin. Sai da Muhseen ya gama komai da yake a cikin asibitin sannan ya sakata mota ya nufi gidan Mama Fulani da ita. Gidan yana nan a yadda yake kamar da a tsari da fasali, sai dai an canja fenti da furnitures. A harabar gidan yai fakin sannan ya bude motar ya fito ya zagayo ta bangaren da Fadime ta ke ya bude mata ya fito da ita.

“Yauwa ya ma sunanki?”

“Yasmin”

Ta fada a hankali.

“Yauwa na kawo ki gurin Mamana kuma mamankin daga yau ita ce mamanki, kuma a nan gidan za ki zauna kamin ki samu lafiya kin ji ko?”

“Too”

Ya riko hannunta suka nufi kofar shiga falon Mama Fulani. Door bell din falon ya danna, babu bata lokaci mai aikin ta bude masa kofa.

“Baaba”

“Na'am Alhaji an shigo”

Tsohuwar ta fada tana yar dariya.

“Eh me kika girka mana?”

“Aa ban girka da kai ba, ban san zaka zo ba ai”

“Mama na ciki?”

“Tana sama ina ga ko bachi take ne”

Ya shigo cikin falon yana rike da hannun Fadime, karasawa yai da ita gurin da set din Kujerun falon ya zaunar da ita.

“Baaba a kawo mata abinci da abun sha, idan ta gama a fada mata yadda za ta yi sallah please, sai dai bata gani”

“To Likita yanzu kuwa”

Baaba ta fada tana kallon Fadime. Muhseen ya nufi dakin Mama Fulani yana cire rigarsa suit dinta. Sai da ya kwankwasa sannan ya tura ya shiga, zaune ya same ta gaban laptop idonta sanye da farin gilashi tana duba wasu laces na manyan mutane. Shigowar Muhseen yasa ta cire gilashin ta kalleshi tana murmushi.

“Yau kuma?”

Ta tambaya domin ta manta when last su shigo gidanta da sunan sun dawo aiki shi da Aliyu, ba kamar da ba da kullum suna nan.

“Bakuwa na kawo miki”

“Bakuwa kuma?”

“Yes danki ne ya tsintota kin san shi da tsince tsince, kuma ya laka min ita”

Ya fada yana kokarin zama.

“Aliyu kuma? Ban gane ba”

A natse Muhseen ya fada mata komai, sai ta cika da tausayinta kamar ba Mama Fulani ba.

“Allah sarki ai ba a wulakanta mutum, baka san ko shi waye ba, wani lokacin ma har shi zai taimake ka, ina yarinyar take?”

“Tana kasa, gobe za a kaita asibiti ko ban biyo ta nan ba zan kira sai ki saka a mota direba ya kaita”

“To ba matsala, Allah sarki...”

Ta fada tana sauka daga kan gadon ta nufi kofar fita, Muhseen ya mike tsaye ya shiga bathroom, ita kuma ta sauko kasa tana kallon Fadime dake zaune a kasa Baaba na bata abinci a baki.

“Hajiya an sauko”

“Eh abinci ake bata ne?”

Mama Fulani ta amsa ma Baaba tana zaunawa.

“Eh na ga zata bata jikin ne shiyasa na soma bata da kaina”

“Allah sarki baiwar Allah ya sunanki?”

“Yasmin, wannan yace na Yasmin ne sunana kuma yace ke ce Mamana”

Mama Fulani ta rausayar da kai tanawa da Ataa.

“Eh haka ne ai da na kowa ne, sannu Yasmin sannu kin ji Allah ya baki lafiya”

Fadime ta daga kai tana tauna abinci. Sai da ta ci ta koshi sannan Baaba ta dauke plates din ta bata ruwa ta sha, ta kama hannunta suka shiga dakinta ta zuba ruwa a buta tai mata alwala ta yadda zata fi fahimta sannan ta saka ta tace tai da kanta, da ido rufe ta kokarta ta yi yadda Baaba tai mata tana ta son ta tuna minene alwala sai ta soma jin abun irin na dazun, take ta kawar da tunanin kamar yadda Muhseen ya fada mata. A gurin sallah kam Baaba daga mata hannu take tana nuna mata yadda za ta kabbatarta sallah, a gurin ruku'i kuma sai ta rikata ta lakwasa yadda zata gane.



BAPPA POV.

Tun da Bappa ya doro gidan ba tare da Fadime ba, Inna ta gane akwai abun da ya faru, sai dai bata masa magana ba duk kuwa da son ganin Fadime da take, sai da ta ba shi abinci ya ci ya koshi ta ba shi ruwa ya sha ta zuba masa wani yai wanka ya gabatar da sallah la'asar sannan ta zauna a inda ya gama sallah tana ta kallonsa kamar ta tambaya ina yarta kuma tana fargabar irin abun da zata ji. Bappa na ganin irin zaman da tai ya san cike take da son ta ji labarin komai. Tunanin ta inda zai fara bata kabarin ya fara, daman ya tafi ya barta ba dan lafiya ta ishe ta yanzu kuma idan ya labarta mata abun da ya faru ya za ta ji?

“Ko dai wani abun ya same ta n Malam?”

Sai da Bappa ya tattaro dukan kuzarinsa sannan ya iya labartawa Inna abun da ya faru, take ta fashe da kuka tana masa magana da yalshen fulatanci.

“Ka ce min kawai na rasa Fulani, damn ita kadai ta tsaya a cikin yayan yanzu kuma na rasata...”

Kuka ta saka sosai wanda ya saka jikin Bappa sanyi wanda har ya ji ina ma ya tsaya a can a bincika ko za a ganta, shi kansa ba wai baya son Fadime ba ne, bacin rai ne ya saka shi haka bacin rai da har yanzu be bar zuciyarsa ba.

“Sai da na ce maka karka je, wata kila zuwan ku ne ya saka ya dauke ta ya kaita wani gurin, babu yadda ban yi da kai ba akan karka je garin nan amman baka ji ba, yanzu ga shi nan ka saka ya sake dauketa wa san inda zai sake jefata? Gashi ba gani take ba”

Bappa ya ja tsaki.

“Ai duk laifinta ne, yarinya bata jin magana kom...”

Be kai karshe ba Inna ta rufe shi da fada tana mikewa tsaye.

“Eh kullum ai daga ni sai ita ne masu laifi a gidan nan, kullum cikin fada kake da ita, dan abu kadan ka ce zaka dake ta, shiyasa har take boye maka bata fadar komai saboda ta san dukanta za ka yi, ni Wallahi sai ka nemo min ita, ka tashi ka tafi garin mutanen nan ka nemi Wasim ka bashi hakuri ya kawo min Fulani, wollahi in ba haka ba sai da na abar maka gidanka, ban zama gidan babu da babu jika, wacan bakar mata ta cinye yayan yanzu kuma yar wannan da ta rage za ka ce ta bata wollahi ni kam ban yadda...”

Bappa ya daga kai yana kallon iko Allah, shi be dora mata laifi ba sai ita ce zata dora masa laifi.

“Aradun Allah ba ni kai kaina ga halaka, sai dai ki tahi duk inda za ki, amman ba ni zuwa wacan gari in mutu”

Ta fada cikin fusata har yana cire rawanin dake wuyansa, Inna kuma ta fashe da kuka mai karfi tana jin kamar ta rasa Fadime ne gaba daya.


IYA POV.

Shiru shiru Zainab bata dawo ba, tun tana sauraren dawowar Zainab har ta gaji ta kwanta da tunani kala kala. Zuciyarta ta fi raya mata cewar an ga Fadime wata kila ta fadi wani abu akan wanda hakan yasa aka kirata.
Bata yi wani bachi kirki ba ko kadan hankalinta be kwanta ba, saboda tunanin tafiyar da akai da Zainab daman tsakanin uwa da da sai Allah. Washe gari tun da ta tashi ta wanke baki bata damu tai sallah ba ta shiga kicin, daman can sallah bata dame ta tana kokarin yi ne kawai idan ta ga idom mutane, musamman a lokacin da take a masarautar saboda ayi mata kallon mutuniyar kirki.
Dumamen shimkafar da ta dafa jiya tai ta fito falo ta zauna tana turawa ba dan tana jin son cin ba domin gaba daya hankalinta ba a kwance yake ba, kadan ta ci ta aje plate din ta mike tsaye ta nufi dakinta hannunta ta wanke sannan ta cire tufafin jikinta ta dauko wasu ta saka ta saka hijabinta ta dauki jakarta ta dauki makullinta ta rufe dakinta ta fito ta leka dakin Zainab, sannan ta nufi kofar fita. Sai da ta kai bakin gate sannan ta kira mai gadin.

“Mun fita, karka budewa kowa gidan nan ya shigo ka ji ko”

“To Hajiya Allah ya tsare”

“To Ameen”

Ya bude mata gate din ta fice, tafiya tai mai nisa kamin ta samu abun hawa, daman sabuwar unguwa irin wannan ba a ciki samun abun hawa da wuri ba. Sai da ta fada masa inda zai kaita sannan ta hau. Suna daf da isa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login