Showing 45001 words to 48000 words out of 286946 words

Chapter 16 - Fulani Book 1 Hausa Novel Complete

20 Dec 2024

903

sunana Wallahi”

Ta fada a fusace sannan ta shige dakinta, shi kuma yai murmushi ya fice daga gidan.



HAJIYA KARAMA POV.

“Abun da kike yi be dace ba Zainab, taya Shattima zai yi magana ki musa masa, a iya tunani Shattima ko cewa yai ki dauki wuka ki yanka ni za ki iya”

Da mugun mamaki Zainab ta kalli Iya.

“Iya kin san abunda kike fada kuwa?”

“Na sani, biyaya ya kama ace kina musu ta kowane hali kamin ki gina kanki”

“Ba ki wulakanci da akai miki ba ne”

“Wannan duk mai wucewa ne, ki koyo juriya da hakuri Zainab ki koyi kaskantarda kai sannan za ki samu nasara a komai, shakarata talatin a gidan nan na san ko waye Shattima kuma na san waye Ammy”

“Ba fa siyasa na ke ba, balle ace na nemi soyayyar wasu, abun da akai miki be kamata ba sam”

“Idan har kin ji zafin abun da aka min ya kamata ki fara kishin mahaifiyarki ki taya ta yakin da take, har mu ci nasara, kuma ki fara tunanin gina kanki, ban yarda ki yi ma Shattima rashin kunya ba domin shi din wata rana shugabanki ne”

“Na fara tunanin gina kai na Iya, tabbas zan yi aure na bar gidan nan”

Ta karasa tana kara zare manyan idanuwanta, Iya ta girgiza kai domin ba haka take son ji ba. Zainab ta mike tsaye ta isa gaban madubi inda wayarta take aje tana ringing ta dauka ta kai kunne.

“Hello Ra'ees”

“Na'am Hajiya ya kike?”

“Lafiya Kalau ya ake ciki?”

“Komai kalau, MBS ne suka shigar da gasa, suna son hoto da zai dace da kamfaninsu a week din nan”

“Miye hadina da kamfanin MBS?”

“Sun bada damar photographers su turo hoton da suke ganin ya dace ya hau, idan kai nasara kai za su bawa ambassador na kamfanin na shekararar na kuam kin san ba kana nan kudi za a samu ba”

“Zan yi tunani a kai”

“Na turo miki komai ta whatsapp idan kin hau za ki gani”

“Okay”

Cike da gadara ta aje wayar ta ja stool din madubin ta zauna tana kallon kanta. Iya ce ta zo bayanta ta tsaya tana kallon irin kyau da yarta take da shi.

“A yadda kike da kyau nan, kamata yai ace Sarki ne ya auri ki, ba mijin kawa ba”

“Mijin kawar nake so Iya, ba zan iya auren tsoho ba”

“Ni ma ban ce ki auri tsoho ba, amman kina iya auren mutumen da za ku tsufa kuna cin moriyarku”

“Shiyasa na ke son na auri Auwal ai....”

“Kashiiiii kin kasa ganewa”

“Babu fa abun da zan gane Iya, ni shi nake so kuma aurensa zan yi”

“Allah ya taimaka ya kai mu lokacin”

Iya ta fada fuskarta ba yabo ba fallasa, sai Zainab ta juyo ta kalleta tana murmushin jindadi.

“Yauwa yanzu na ji magana, Amin thank you”

Dan murmushi kadan Iya tai mata sannan ta ce.

“An jima ki samu Shattima ki ba shi hakuri”

“Zan yi hakan In-Sha-Allah”

Iya ta gyada mata kai sannan ta juya ta fice daga dakin.



NANA POV.

Tun da ta dawo school tana cikin dakinta bata fito ba sai la'asar, duk mutanen da ke zuwa gaisuwa sai dai su lekota ko kuma su tambayi lafiyarta Ammy tace musu tana ciki.
Tana fitowa daga dakinta ta nufi dakin Ammy, kai tsaye ta tura dakin ta shiga babu ko sallama, Shattima na zauna saman kujera Zainab na gefensa ita ma zaune, shigowarta yasa ya dago ya kalleta Zainab ta miko mata hannu.

“Hey Baby zo nan...”

Nana ta karasa kusa da ita ta tsaya, dan ba zaman take son yi ba, Ammy dake bandaki take jiran ta fito.

“Waya taba ki?”

“Ni bana son School bus tana kai ni makaranta”

Ta fada a shagwabe, tana dan satar kallon Shattima da yaki ya sake kallonta. Kamin Zainab tace komai Ammy ta fito daba bathroom din fuskarta jike da ruwa. Kallo daya tai ma Nana ta dauke kai ta karasa bakin gadonta ta zauna, sai Nana ta matsa kusa da gadon tana turo baki domin kwata kwata yau bata jidadin yadda aka kaita makarantar ba aka dawo da ita.

“Ammy ni bana son school bus tana kai ni makaranta”

Kallonta kawai Ammy take.

“Nana wai me yake damunki, tunanin ki dabam, ki duba yarinyar da take zuwa gyara dakin yaran can ba ta wuce warinki ba, amman aiki take zuwa nan, kina tunanin ita bata son gata nan? Ko bata son karatu? Me kika nema kika rasa ne? Tun da kika dawo school kika shige daki kika zauna duk masu shigowa sai tambayarki ake amman kin zauna a can kamar ba ki san rashi mu kai ba? Abinci ma ba ki fito kin ci ba, what is wrong with you?”

Ta yi shiru bata ce komai ba, domin bata da abun cewa ita dai karatun ne bata so.

“Driver na ke son a daukar min”

“To ba za a dauka ba, kuma dole ki je makaranta, Islamiya ma yaushe rabonki da zuwa?”

Ammy ta amsa mata kai tsaye. Sai ta kara bata fuska.

“Wallahi ba zan karatun ba, indai ba a daukar min driver ba ba zan sake zuwa makaranta ba”

“Idan kin yi karatun ni zan karu ko ke? Shashasha, ba ki son a fada miki gaskiya, kin fi son a barki ki yi ta hauka, kuma Wallahi kika ki zuwa makaranta sai na sa sarkin bulala ya zane miki jiki”

“Ai daman ba so na kike ba, shiyasa kika saka Baba Waziri ya kwashe komai na dakina....”

“Eh bana son ki, je ki nemi wata uwar da take son ki, idan ba ki bata min rai ba hankalinki ba zai kwanta ba, idan so kike na miki ba ki wata rana zan miki, duk ranar da bana raye sai ki nemi mai fada miki gaskiya ki rasa, sakaryar kawai nai kukan ciwon Mahaifinki na yi na ki...”

Ammy ta karasa cikin fada hawaye na sauko mata, da sauri ta tashi ta koma bandakin. Nana na juyowa Shattima ya wanke mata fuska da mari.

“Stupid girl, wuce ki je ki hada kayanki yanzu nan driver zai kai ki gidan Baba Waziri”

Fashewa tai da kuka ta fice dakin da gudu. Zainab ta mike tsaye tana kallon yadda ran Shattima ya bace.

“Shattima ka rika daga mata kafa yarinya ce”

“Ta fara wuce gona da iri, abun ta gaba yake ba baya, i hate nonsense”

Ya amsa a fusace sannan shi ma ya fice daga dakin. Ko kadan Zainab bata jidadin abunda ya faru ba, amman ita tana kallon Nana da kurciya ne da kuma shagwaba, a gurin ta aje wayarta ta fice zuwa dakin Nana.
*🐄🐄 FULANI 🐄🐄*


By Khadeeja Candy


*13*

Tun ranar da Fadime ta ji ga mutumen nan mai busa bata sake ganinsa ba, hakan kuma be saka ta fasa zuwa gurin manyan duwatsun ba a kullum tana leka ko zata ganshi.
Kuma tun ranar bata sake jin busar ba, bata sake mafarkinsa ba, a lokacin ne ta fara rayawa a ranta cewar aljani ta gani kuma shi take mafarki.
Kasancewar yau friday da safe ta fito da shanun kiwo, daman duk Friday da safe take kiwon kasancewar jumma'a kurarren lokaci ne. Shanunta na gaba tana biye da su, kanta sanye da malfar saƙa, ta daura zare a wuyanta da gaban goshinta, dan karamin kare na binta hannunta rike da sandar korar shanu bata fasa wakewaken da Inna take hanata ba.
Sai da suka isa bankin rafi sai ta nufi inda ta saba zama, ta zauna tana hango wasu shannun da wani bafullatani dake can nesa da ita yake kiwo.
Kanne ido daya tai ta fara kirga masa shanu daga inda take zaune, sannan ta dawo kirga nata.

“Nawa sauran 37, idan wata ta sake mutuwa yau sauran 36 idan wata ta kara mutuwa sauran 35...”

Bata karasa kirgen ba ta soma jiyo busar sarewar tana karade dajin. Bude baki tai ta zaro ido ta fara dukuduku ta ratsa cikin marar sannan ta mike tsaye tana leken inda ta fi jin busar na fitowa, sai kuma tai dukuduku ta dawo ta haye saman dutsen ta mike tsaye. Hangoshi da tai a saman wani dutsen zaune yasa ta kara gwale idon.

“Kai...........”

Sai ta ji muryarta ta amsa duka dajin da kiran da tai masa.

“Laaaaaaa”

Ta yi dariya, wani dadi taji yadda ta ji muryarta ya gwauraye dajin, a yanzu ta gano dajin ne ke da daukar sauti. Saukowa tai saman dutsen da sauri ta fara gudu tana daga kanta sama tana hango dutsen da yake zaune, kamar wacce aka koro haka take yankan dajin tana gudu har ta isa gaban katon dutsen a lokacin ne ta ji sautin busar sarewar sosai a kunnenta, labewa tai jikin dutsen tana dariya marar sauti tana kara zaro ido.

Gaba daya ta manta da wani zancen aljani ne ko mutum, sai ta dan lekesa ta sake boyewa tana dariya har da su kyakyatawa kadan ta rufe bakinta. 
      Zaune tai a gurin tana ta sauraren fusar sarewar dake shiga kunneta, har da wani lumshe ido take tana budewa. Lokaci daya ta daina jin busar saurara tai na dan lokaci ta ji ko za a cigaba, shirun da ta ji ne yasa ta tashi ta leka sai ta ga babu shi a gurin, hakan yasa ta fito gaba daya tana kallon dutsen.

“Ina yaje?”

Ta tambayi kanta tana tare hasken ranar dake haskata da hannunta, domin malfar dake kanta ta fado bayanta igiyar malfar ce kawai a wuyanta, kara natsawa tai tana rabon ido, sai ta hangoshi yana saukowa saman dutsen. Saurin komawa tai ta boye tana yarfar da hannunta tana dariya da jindadin ganinsa da tai. Amman da yake saukowa ina zai je? Gurinta ko wani guri? Ta dan zaro ido kamin ta kara shan jinin jikinta jikin dutsen tana saurare ko zata ji takun tafiyarsa ko motsin wani abu, amman sai ta ji shiru hakan yasa ta fara takawa kadan kadan ta leka sai ta ganshi tsaye yana kallon inda take kamar daman can jiran yake ta leko ya ganta, da sauri ta koma sai a lokacin ne tsoro ya fara kamata.

“Wayyo Bapppa.....”

Ihun da tai ne yasa ya karaso kusa da ita yana kallonta, hannunsa rike da sarewa, sai dan walkin dake daure a kugunsa, fari ne sol kuma kyakkyawa gashin kansa ya kwanta luf kamar bafulatani idonsa ma fari kal kamar madara ga dogon hancin daya kara kawata fuskarsa. Dukewa Fadime tai kasa ta rufe ido tana kuka.

“Bapppa.....”

Bappan kawai take kira kamar ance mata zai ji ta daga inda take, tasa hannayenta ta rufe fuskarta sai rusar kuka take kukan da ba hawaye. Shi dai kallonta kawai yake cike da burgewa ba yau ya fara ganinta ba, kusan a duk lokacin da ya bar gulbin dake kusa da garinsu ya iso wannan dan yi wwanka ko yin wani abu sai ya ganta ta zo kiwo ko deban ruwa, sai dai ita bata taba kula da shi ba sai a yanzu da yake busar kusa da inda take ji.
Jin be mata komai ba yasa ta dago ta kalleshi kadan ta runtse ido, gabanta sai dukan tara tara yake.

“Bapppa”

Ta kira sunan Babanta da kuka, sai kuma ta sake bude ido ta kalleshi yanzu kuma so take ta tantace mutum ne ko aljani.

“Ban maka komai ba, ni ban maka komai ba, ni mutum ce ni ka yi hakuri ba zan sake ba”

Bayan kallonta babu abun da yake, matsawa tai baya tana yi tana kallon gefensa inda hanya take sai kuma ta kallesa, cikin wayo ta zo da mugun gudu ta taba shi da yatsanta ta daka wani uban tsalle tana son ta ranta a na kare, sai yai hanzare cafko hannun nata ya rike gam. Wani irin shidewa tai ta dawo ta bude ido sosai tana kallon hannunsa da ya rike ta da shi tana bude baki kamar zata kwala ihu kuma ba tai ihun ba, sai ta sulele kasa tana wani jan numfashi, so take ta suma kuma suman be zo mata ba. Dayan hannunsa yasa ya rikota ya jinginar da ita jikin dutsen tana kallonta.

“Bapppa...”

Ta sake kwala masa kira. Uffan be ce mata ba sai kallonta yake duk ganinta da yake bata taba burge shi ba irin yau, he never thought haka take da wauta sai yau and he like it.

“Bapppaa Na...... ”

“Wuta na binki ba ki gani ba....?”

Ya fada cikin siriyar muryarsa mai dadin sauraro yana daga mata kai alamar ta duba. Cikin wani irin tsoro marar misaltuwa Fadime ta waiga kasanta.

“Ba wuta dutse ne”

Ta fada numfashinta na rawa domin a yanzu kam da gaske tsoro take ji. Matsowa da ita yai kusa da shi kamar zai rumgume ta dan filin dake tsakanin bayanta da dutsen yai wani abu da hannunsa kamar zai kama abu ya cafke hannunsa ya jimke sai ga wutar tana ci a cikin hannunsa.
Kadan Fadime ta juya ta ga wutar sai ta kara bude ido ta kwala ihu. Shi kam kallonta kawai yake har tai ta gama sannan ya juya ya fara tafiya.

“Kai a aljanine?”

Ya girgiza mata kai alamar a'a.

“Kai ka saka min wutar?”

Nan ma kan ya girgiza.

“Ya akai ka ga wutar waya saka min wutar?”

Daga inda take tsaye take aiko masa tambayoyin cikin daga murya ta yadda zai ji ta, sai a lokacin ya juyo ya kalleta sai tai saurin rufe fuskarta da hannayenta.

“Wutar maita ce, mayu suke sakawa mutun ita, idan mutum yana da baiwa sai su kwashe ta su saka masa wuta, komai ya rika ko ya taba ba zai yi albarka ba, ba zai amfane shi ba, idan suka kasa cin kurwarsa sai su daddanketa mutum ya koma wawa ko mahaukaci ko musaki, akwai wanda ke bibiyarki”

Yana fada mata haka ya juya ya cigaba da tafiyarsa yana murmushi, fitowa tai tana kallonsa har ya haye saman dutsen yai tsaye yana kallonta, daga inda take tsaye ta daga masa hannu shi ma ya dago mata sannan ya gangara ya sauka ta arewa da dutsen.
A lokacin ne ta samu kafafuwan gudu ta dawo gurin kiwon shanunta ta zauna tana ta tunanin abunda ya fada mata. Har ta gama kiwonta nagge ko daya bata mutu ba, cikin jindadi ta kora shannun suka nufi gida, kamin su isa gida duk ta matsu, suna isa bata ko tsaya saka hannun ciki gida ba, ta shige Bukkarta ta dauko littafinta ta fara rubuta abun da ya faru, sai da ta rubuce komai tsaf sannan ta fito waje tana neman Inna ta labarta mata.

FALMATA POV.

Tana cikin wanke wanke ta ji Tumba a bayanta tsaye, juyawa tai da sauri ta kalleta, sai Tumba ta risino daidai kunnenta tana fadin

“Wai ke Falmata ba ki da irin samarin nan masu yi ma budurwa anko? Kullum suka zo ba su da abun yi sai kawo miki abu a leda ko su baki yan kudi a hannu, haba Falmata ki rika sakin jiki mana”

Cike da damuwa Falmata ta sanda kanta kasa, ta fahimci inda Tumba da dosa a yanzu.

“Ke baki ga sauran yan mata yadda suke ba? Ki rika sake musu jiki da fuska kinji kina far'a samari suna son mace mai far'a”

“To”

“Yauwa yau duk wanda ya zo ki ce ya baki dubu uku ko biyar, in dai kina kawo min kudi haka zan rika miki komai”

“To”

Ta sake amsawa a ranta tana mamakin yadda Tumba take son ta zama, ta rasa me ta tare mata a dubiyar da bata son farincikinta, yau kwana uku kullum sai dare ya raba take satar kafa ta fita taje shago ta ci bashin garin kwaki ta saka a cikinta, sakamakon abincin da ba a bata a gidan.
Yanzu kuma tana nuna mata wani mugun hali wanda ba halinta ba. Tana wanke wanke tana hawaye, sai ta share ba tare da ta bari Tumba ta gani ba, haka tai aikin cikin rashin kuzari sannan ta fara shara, ta bi ko'ina na gidan ta masa tas, ta dawo ta zuba ruwa a bokiti ta shiga bandaki, ta nan ta samu damar kuka iya son ranta tana tuna irin gargadin da Mama ta yi mata kamin rasuwarta.

“Wannan farin jinin na ki kar ya kai ki ga halaka Fulani, tun kina yar jaririya Allah ya saka miki farin jinin jama'a yanzu kuma kin tasa samari sun fara miki sallama, bana son zuwa firar nan karki sake fita duk wanda ke son ki da gaske ya aiko gurin mahaifinki, kuma kin ga kin fara al'ada ko hannunki kika bari namiji ya rike za ki iya samun ciki, dan zai ja a wuce guri, karki kuskura bari a rike hannunki”

Fashewa tai da kuka ta rufe bakinta dan kar kukan ya fito, farar fita zance da samari da take, bayan mutuwar mahafiyarta ne, wanda Tumba take bata umarni, tun tana jin kunya tana boya tana rasa abun fada har ta waye, ta iya magana da tarbar wanda ya zo gurinta. Yanzu kuma tana nuna mata hanyar da ba mai bullewa ba ce, taya za ta ce a bata kudi mai yawa haka?
Cikin rashin kuzari ta gama wankan ta fito ta shiga dakinsu ta shirya cikin wani farin yadi ta saka hijabinta ta fito tsakar gida.

“Na tafi”

“To Allah ya tsare yar albarka”

Tumba ta fada cikin daga muryar tana washe mata hakora, Falmata ta dauke kai ta fara tafiya kamar bata son zuwan ta fice daga gidan zuwa gurin aikinta.

“Na rasa yadda zan yi da yarinyar nan, komai nai mata kamar ban yi ba, kowa nai ma ya kama ban da ita, ban san me shegiyar uwar nan ta bata ba, kudi kawai na ke kashi a banza”

Tumba ta fada tana rafka uban tagumi, tana tuna abunda Malam na zaure ya fada mata game da Falmata.

“Idan ba ki yi da gaske ba, yarinyar sai ta gawurta, ina ji miki tsoron abun da zata zama nan gaba”

Wani dogon ajiyar zuciya ta ja ta sauke.

“Na rasa yadda zan yi da yarinyar nan idan nai wannan a banza, wacan a banza”

Ta furta cike da jin zafin irin kudin da ta kashe akan Falmata amman har yanzu shiru, farinjinin da take son ya gushe ba daina ba, abu ma kamar ƙaruwa yake.
Falmata na tafe tana tunanin maganganun Tumba, wace karya zata mata ta tsira? Idan ma bata kawo mata kudin ba zata iya dukanta ko ta mata wani sharin. Bata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login