Showing 105001 words to 108000 words out of 286946 words
ba right?”
“Eh da naje na dauko hotunan maybe gobe ma na dawo”
“To zai fi da ace ki dawo baki yi komai ba, ko kin dawo ai ba warkar da shi zaki yi ba, police din da zasu raka ki suna waje suna jiranki sun kira ni yanzu”
“Okay thank Youu”
Ta sauke wayar zuciyarta na raya mata wani abu marar dadi da bata san minene ba, a rayuwarta bata taba samun namijin ta dake so a dabi'a da mu'amala ba kamar Auwal komai nasa ya mata, natsuwarsa kudinsa kyaunsa da komai ma, ya kwanta mata a rai sosai b kamar sauran mzan da idan ta ji tana sonsu yau ba gobe ta ji bata so ba. Haka nan ta mike tsaye ba dan ta so ba sai dan maganar da Shattima yai mata ta dauki jakar kayan aikinta ta fice daga dakin, sai da ta shiga tai ma Hajiyar gidan sallama sannan ta fito harabar gidan inda ta hango police din su biyu tsaye jikin wata 406 suna jiranta. Karasawa tai suka gaisa sannan dayan ya karbi jakarta ya saka a back seat ita ma ta shiga ya rufe motar ya koma gaba, ya tashi motar aka bude musu gate. Kamin su kama hanya ta fito da wayarta aikawa da Auwal sako.
“Ina ta kira baka picking how are you feeling now? Get well soon pls i love you...”
Tana aika sakon idonta ya cika da hawaye for no reason, sai ta maida dubanta gurin titi yana sauke numfashi a hankali.
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
27
*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt bank, then send the evidence to 08036126660*
FADIME POV.
Sai da ta cika tulun ya dorata sannan ta kalleshi tana murmushi.
“Na gode”
Murmushi yai mata as respond yana ta kallonta har ta fara tafiya, tana yi tana gaigensa sai murmushi yake mata har ta daina hangosa, wani kalar dadi take ji tun da ya fada mata babu wanda ya isa ya taba ta yana raye ya bata lasisin yin ma kowa yadda take so kenan. Hango mota fake a kofar gidansu na kara da police biyu yasa ta tsaya cak sai kuma ta dan koma baya ta boya, a tunanin ko Amo ce ta dauko mata police din, domin ta manta da zancen da tai da Xainab, har sai da ta hangota.
“Oh ashe ita ce”
Ta fada tana washe hakora, abun ka da mutumen kauye yayi arba da n birni, sosai ta cira kafa ta karasa kusa da motar yana kallon Zainab baki har kunne.
“Ke ce...!”
Zainab ta mata wani kallo from head to toe, sai wani kallon zanar take kamar mai kyankyami.
“Eh”
Ta amsa kamar wacce bata son magana.
“Ina zuwa”
Fadime ta fada sannan ta shiga cikin gidan da sauri, tsakanin sauke tulun kanta da labartawa Inna abun da ya kawo Zainab ba zaka iya fadar wanda ya riga wani ba. Mamaki ne ya cika Inna ta san Fadime ba dai wauta ba kam, in ba shi ba daga haduwa da mace a birni ki fada mata inda zata same ki bayan baki san ta ba baki san inda ta fito ba.
“Kin san idan Bappan ki yaji sai ya miki doka ko? Irin wannan shisshigin ya rabaki da shi Fulani amman baki jin magana”
“Ai ba zai ji ba, ba zaki fada ba, kuma fa ita daukar hoto kawai zata yi”
Fadime ta fada tan dafa Inna kamin Inna tace komai Zainab tai sallama ta shigo cikin gidan. Inna da Fadime suka hada baki gurin amsa mata, cikin karamci da girmamawa irin n Fulani Inna ta shiga bukkatarta ta dauko mata sabuwar tabarmarta ta shimfida ma, Zainab ba adan ta so ba ta zauna domin har ga Allah kyankyaminsu take.
“Sannu baiwar Allah”
Cewar Inna tana aje mata kwanon kokon data dama.
“Yauwa ya gida ya aiki?”
“Fatar kun iso lafiya”
“Alhamdulillah, am sunana Zainab ni photographer ce ma'a mai daukar hoto, ina daukar hoton duk wani abu da na san zai kawo min cigaba a sana'a ta, da kuma abun da zai kawo min daukaka, wannan shi ne katin shaida ta”
Ta mikawa Inna id card dinta, cikin hanzari Fulani ta kai hannu ta karba ta soma karantawa.
“Kamin mu shigo nan sai da na fara biyawa gurin mai garin garin nan na yi magana da shi sannan na karaso nan, mun hadu da wannan yarinyar a Katsina few days back ta fada min gidansu da yadda zan same ta zata min jagora na yi aikina, ba a nan har a garin Garuk...”
“Garuk?”
Inna ta fada tana dafa kirjinta. Cikin hanzari Fadime ta kashewa Zainab ido daya tana mata alama da tai shiru.
“Aa b ni zan kai ta can ba fa, ni wa na sani a can, ita tace zata je tare da police ko?”
“Eh akwai wadanda za su min jagora zuwa can, a nan zan dauki hotuna ne kawai”
Fadime ta mike tsaye da sauri ta nufi gurin garken shanunsu.
“To zo ki fara”
Zainab ta mike tsaye ta nufi kofar fita, sai da ta fice sannan Inna ta kira Fadime tana mata gargadi.
“Ke wa kika sani a garin Garuk? Kin san yadda ake fadin garin nan ko? Fadime ki kama kanki ban son janye-janye”
“Ba ni zan kaita ba, ni ma fa tsoron garin nake, ai ban je ba”
“Na dai fada miki”
“Tau”
Ta amsa da baki, zuciyarta kuma cike da son zuwa daman tana neman dalilin zuwa garin. Shigowar Zainab yasa Inna ta mike tsaye ta koma bukkarta, Fadime kuma ta tsaya jikin shannun har sai da Zainab ta gama gyara camera ta soma daukar hoto da ma gidan gaba daya. Suna fitowa waje abun ka da mutane kauye sai aka musu taro ana ta kallonsu, tun daga kan gidaje har gonaki sai da Zainab ta dauka, ba laifi garin ya burgeta ita kanta ba zata iya shaidar when last taga inda ake gidajen zana kamar a nan ba. Sai da ta gama sannan ta janyo Fadime gefe tana tambayarta.
“Yanzu ya za'ayi muje garin?”
“Bari naje ma fara dubawa idan yana nan”
“Okay karki dade”
Da sauri Fadime ta sace kafa a cikin taron mutane ta zagaya zuwa inda zata ga Wasim, sai da taje ta duba ta dan jira na lokaci bata ganshi ba, ta dawo ta sanar mata, ko kadan Zainab bata jidadin hakan ba domin ta kwallafawa ranta zuwa garin, domin hotunan can da za su dauka zai fi daukar hankali fiye da na garinsu Fadime, ita kanta a yadda aka bata labarin mutane tana tsoron zuwa garin, ba dan tana neman suna da kuma daukaka ba babu abun da zai sakata tai wannan kasadar.
A garin da wuni har yamma after every one hour sai Fadime taje ta duba ko zata ga Wasim amman shiru, duk yadda Inna ta so Zainab ta ci abincinta bata ci ba, ita wai kyankyami take, sai police din aka bawa ita kuma aka siyo mata biscuits da lemun roba ta sha. Sai da yamma lis Fadime ta koma dajin tun kan ta karasa ta ji busarsa saita dawo da gudunta ta sanarwa Zainab.
“Ya zo, na ji busarsa”
“Da gaske?”
Zainab ta tambaya gabanta na dan faduwa domin har ga Allah tsoro take ji kawai karfin hali ne irin na ɗan maye.
“Amman yanzu zan fadawa Inna cewar zan rakaki rijiya mai gaba dubu ki dauki hoto, sai ki sa police din nan su kori yaran nan kar su bi mu”
“Okay”
Ta amsa mata tana gyada kai, domin da kamar rada suke maganar dan kar Inna ta ji. Sai Fadime ta kalli Inna dake wanke-wanke tace.
“Inna wai zan rakata rijiya mai gaba dubu ta dauki hoto”
Inna ta yi ma Fadime wani wawan kallo ta shiga mata fada da yaren fulatanci.
“Fulani wai baki da hankali, taya zaki je rijiya mai gaba dubu da yamma haka? So kike ki kwaso wani abun kuma”
A maimakon Fulani ta maida mata da yaren sai tai da hausa saboda Zainab ta ji.
“Ai ba zuwa zan yi kusa da rijiyar ba, nuna mata kawai zan yi n dawo”
“Dan Allah ki taimaka min, shine kawai abun da ya rage min, sai n a koma in ya so gobe sai na dawo naje can garin Garuk din”
Zainab ta fada da siffar magiya. Sai Fadime ta zaro ido kamar gaske.
“Ahaa har da can zaki je? Ni tsoro nake ji”
“Ba da ke zanje ba, ba man zan biyo ta nan ba, yanzu dai muje ki rakani na dauki hoton”
Fadime ta kalli Inna da ta tsayar da wanke wanke da take tana kallonta.
“Inna na raka ta? Ba zan matsa kusa da rijiyar ba na miki alkawari”
Ba kasafai Fadime take requesting abu a gurin Inna ta kasa mata ba, ba dan komai ba sai dan tana son ta sosai da kuma ganin ita kadai ta rage mata a duniya.
“Karki dade”
“Tau”
Fadime ta amsa tana washe baki, Zainab ta mike tsaye da sauri suka fita. Ko da suka fito ma babu mutane a waje sai police din dake zaune karkashin wata bushiyar dogon yaro, kai tsaye Zainab ta nufi inda suke ta sanar musu inda zata je tare da Fadime sannan ta bi bayan Fadime dake tafiya. Hanyar da zata ta sadasu da rijiyar Fadime ta bi sai da su kai nisa sannan ta karya kwana ta dauki hanyar da zata sadata ta bakin dutsen. Suna tafe tana tunanin abun da Wasim ya fada mata dazun, daman abun ya tsaya mata a rai.
“Wai idan mutum yace maka i like you yana nufin so kenan?”
Ta tambayi Zainab tana kallonta, a maimakon Zainab ta amsa mata sai tai mata banza, ba dan bata ji ta ba sai dan tana ganin Fadime ba ajinta ba ce da zata tsaya tana magana da ita, ba dan ma tana neman abu a gurinta ba da ko kallo bata isheta ba. Banza da Zainab tai mata sai yasa ta ji ba dadi sai dai bata nuna ba bata kuma sake ce mata komai ba har suka nisa cikin dajin. Busar sarewar Wasim ne abun da ya fara sauka a kunnuwan Zainab, daman Fadime ta saba da jin busar b tun yau ba, ita kam a gurinta ba bakon abu ne ba, wani irin natsuwa da shauki ne suka ziyarci Zainab, busar sarewar irin busar nan ce mai shiga zuciya da jini ta kwantar da hankali mai saurarenta, irin busar dake dacewa da ko wane kalar yanayi, a take ta ji ta kagara tai arba da mai busar, a rayuwarta bata taba arba sa wani abu mai burgewa da daukar hankali kamar haka ba, indai haka al'adar mutanen garin take tabbas zata burge kowa.
“Wow.... ”
Ta furta jin yadda suke kara dorar inda busar ke fitowa, ita kuma tana jindadin busar na karuwa a kunnenta, babu tsoron komai take ta ratsawa cikin gonar masarar tana ta son arba da mai busar. Fadime na gaba Zainab na binta a baya har suka haura saman dutsen, zaune yake ya basu baya ya saka sarewarsa a gaba sai busa yake, Fadime ta taka har kusa da shi sai ya mike tsaye ya juyo yana murmushi.
Wani irin faduwa gaban Zainab yai kwarjininsa da haibarsa suka tsaya mata cak a zuciya, ta saba ganin maza babu riga a jikinsu, gaisa da namiji taba jikinsa ko zama kusa da shi duk ba bakon abu bane a gurinta, amman a yau tana jin ta wata iri ta dabam ganin Wasim da irin kirar da ba ko wane namiji ke samu ba, komai na fatarsa Jikinsa a jere yake, fatar jikinsa jata ba kamar ita b da take fara fol, ga jiknsa all his muscle ya fito gwanin sha'awa, wani abun daya kara masa kyau walkin dake daure a kugunsa ko ba komai ya dabbaka al'adarsa, ga kuma kyau fuska a dogon hanci da fararen idanuwa da suka kara masa kwarji da haiba.
“Wow....”
Wannan karon a ranta a furta tana ta kallonsa irin kallon nan na burgewa. Shi kam kallo daya yai mata ya dauke kansa ya maida hankalinsa gurin Fadime.
“Tun dazun nake ta zuwa ban ganka ba, wannan matar tana daukar hoto ne kuma tana zon zuwa garin ku na fada mata zaka kai ta”
A take murmushin dake fuskarsa ya gushe, ya saka hannunsa biyu ya dafa kafadar Fadime.
“ A garin mu ba a yarda da duk wani abu na cigaban zamani ba, kamar waya camara da sauransu, kuma ba kasafai ake karbar baki ba sai da wani dalili, idan nace zan kai ku zaki jefa ni a matsala”
Fadime ta turo baki ta bata fuska.
“Ni dai n riga na ce mata zaka kaita fa...”
Bakinsa ya cikawa iska ya busar ya maida dubansa gurin Zainab, matsowa tai kusa da shi ta mika masa hannunta ba tare da tunanin komai ba.
“Hi sunana Zainab...”
Kallon hannunta yai kamin ya kalli fuskarta, sannan ya mika mata nashi hannun yana kallon cikin idonta, wanda hakan be yi ma Fadime dadi ba sai ta ji wani iri zuciyarta ta sosu.
“Ke jinin Iya ce...”
Wani irin dauke numfashi Zainab tai tana kallon Wasim idonta kamar za su fito, tambayarta yake ko kuma fada mata yake? Tsoro ne ya kamata.
“Ka santa ne...?”
Ta tambaya murya na rawa, be bata amsa ba yanje hannunsa yana kallon Fadime data kara bata fuska saboda ya gaisa da Zainab, shi kuma a zatonsa saboda yace ba zai kai su ba ne.
“Shikenan...”
Sai kuma yai shuru yana nazari. Zainab kam mamaki ya kusa kasheta, wata kila ya sani ne saboda shi matsafi ne ai zai iya karantar komai a tare da ita, sai a lokacin ta kara gasgata abun da ake fada a game da mutanen garin.
“Zan kai ku amman ba yau ba, ko kuma na tafi da ita kawai ke ki zauna”
Ya fada yana kallon Fadime sai ta makkale kafada kamar wata yarinya.
“Aa ni ma ina son na ga garin ai”
Zainab ta dora da.
“Ni ma yau kawai na ke da dama, gobe zan koma garin mu”
“Ina ne garinku?”
Fadime ta tambaya sai Wasim ya amsa mata.
“Yola”
“Eh Yola...”
Zainab ta maimaita cikin tsananin mamaki.
“Ka san garin ne?”
Nan ma be ce mata komai ba ya rika fuskar Fadime dake ta mamaki ace tun daga kasar Yola ta zo nan dan kawai daukar hoto.
“Komai aka baki karki ci, ki min alkawari ko minene aka baki ba zaki ci ba?”
“Na yi”
Ta fada tana daga hannu.
“Ko da nama ne”
Ta bude baki tana yar dariya.
“Kai har da Nama?”
“Eh”
Ya amsa mata da fuskar dake nuna ba da wasa yake ba. Sai tai yar siririyar dariya ta kawar da kai.
“Tau”
“Ni fa...?”
Zainab ta tambaya ganin ita be ce mata komai ba.
“Ki ci”
Ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba, yana cigaba da kallon Fadime ya ce
“Zan je na samo muku tufafin da za ku canja”
“Har sai mun canja tufafi? Ni gaskiya tsoro nake ji ko dai mu bar shi, Inna ma bata san zan je ba”
Fadime ta fada da iyakar gaskiyarta domin tsoron ya fara ratsata tunawa da gargadin da Inna tai mata. Zainab ta fisgota da karfi.
“Wallahi baki iya ba, sai da muka samu dama zaki ce a fasa...”
Bata karasa ba, Wasim ya daka mata tsawa yana nunata da yatsa.
“Karki sake...”
Shan jinin jikinta tai ta make a gurin kamar babu mutum domin b karamin razana tai ba.
FALMATA POV.
Babu wanda ya san abun da ya samu goshinta har sai da garin Allah ya waye, ganin Baba n tsaye yasa Tumba ta nuna damuwarta kamar gaske.
“Ke miya samu goshinki?”
Ta tambaya cikin daga murya da nuna tashin hankali kamar da gaske ta damu.
“A gidan da nake aiki ne na bugu da kofar ban lura ba”
Falmata ta amsa tana tana goshin nata daya kumbura yana mata ciwo.
“Ayyah sannu”
“Yauwa”
Ta amsa tana kallon Tumba domin ta san ba dan Allah take mata sannun ba. Sai da risina har kasa ta gaishe da mahaifinta sannan ta kalli Tumba tace.
“Zan wuce aikin”
“To Allah ya tsare”
A natse ta nufi kofar fita tana tafiya da sauri sauri, domin jin take kamar da ta isa ne Sirleem zai kaita gurin gyaran kunne, babu abun da take so a yanzu kamar jinta ya dawo daidai. Kusan tun da ta fara aikin bata taba jin tana son zuwa ba kamar yau, duk wani nisa da gajiya da take ji idan zata ji sai ta neme shi ta rasa a yau, ko da ta isa masarautar 7:39am. Kai tsaye ta nufi bangaren Ammy kamar yadda ta saba, tana kokarin shiga gate din ta ji an tabota, sai ta juyo da sauri, hadinar data taba ta ta nuna mata Jurry, daga inda Jurry take tsaye ta daga mata hannu alamar ta wuce, sai ta sanda kanta kasa ta shige gate din b tare da tunanin komai ba. Sai da ta isa kofar falon Ammy ya danna door bell din sannan zuciyarta ta raya mata cewar wata kila bangaren da matar take shi ne bangaren Sirleem.
A yau ma Jekafiya ce ta bude mata kofar, Falmata ta risina har kasa ta gaisheta sannan ta fada mata bukatarta.
“Dan Allah ina nemn izini misalin 3pm zan je asibiti”
“To za a sanarwar Ammy”
Jekadiya ta amsa mata da karfin sanin cewar bata ji sosai sai an yi da karfin. A natse