Showing 240001 words to 243000 words out of 286946 words
silar ciwon Hajiya Babba. Dauke kai tai ba tare da ta amsa ba ta cigaba da kallon Hajiya Babba.
“An fadawa Ammy kuwa? ”
“Aa ban kira ba ina ganin suna gurin gaisuwa, kuma ko na kirata ai dadi kawai zata ji”
“Wani irin dadi kuma Kausar?”
“To son Hajiya take yi balle”
“Ki daina wannan maganar, abun da ke tsakanin Hajiya da Ammy dabam babu ruwanki a ciki”
Har zata sake magana sai dai ganin Hajiya ta motsa yasa duk suka maida hankali gurinta suna kallonta, ta dade tana motsin sannan ta bude ido tana kallonsu.
“Sannu Hajiya”
Kausar ta fada, sai ta daga mata kai ta amsa daker
“Yauwa su waye ku?”
Daga Sirleem har kasar kallon juna su kai da mamaki, ga bakinta yana nan kamar da be dawo daidai ba, sai dai wanna karon ta samu damar magana yunkurawa tai ta tashi tana karewa dakin kallo.
“Hajiya ni fa Kausar”
“Kausar kuma? Wace Kausar din? Ko. Ke ce mu ka je tare da ke gurin bokan nan?”
Ba shiri Kausar ta bude baki idonta na cika da kwalla.
“Hajiya ta yi losing memory ta Ya ya”
Kamin Sirleem da ke tsaye yace komai Hajiya ta girgiza kai.
“Aa ke ce dai ban san waye ke ba, Shi ai Sirleem ne dana ko?”
Sirleem ya daga mata kai cike da nauyin bakin da ya kasa barinsa ya amsa. Sai ta kama rigarta tana wasa da ita kamar wata yar yarinyar tana turo bakinta dake gefe gaba.
“Ina Falmata? Daman ance yarinyar nan zata lalata mana komai, da Falmata da Fadime, da Sardauna, kuma sun lalata, babu abun da ban saka ayi ma Falmata ma amman bokan nan sai cewa yake wai na yi latti, daga nan muka tashi muka tafi Katsina ni da Hajiya Talatu da Jarma da Juwairiyya, saboda kawai abubuwa su daidaita amman komai be mana kyau ba, har sata an laka mata amman sai da ta lalata mana shiri”
“Kausar je ki kira likita”
Sirleem ya fada zuciyarsa na bugawa da mugun karfi, da gudu Kausar ta tashi ta fice daga dakin tana kuka, Sirleem ya zauna kusa da Hajiya Babba yana kallonta cikin tsananin damuwa, sai ta kalleshi tana kokarin fashewa da kuka irin yadda shagwababbin yara suke yi.
“Ka ga sun fada mana akwai tafiyar da ba dawowa ashe Talba ne zai mutu”
Sai kuma tai shiru kamin likita ya shigo ta sa ke cewa.
“Kuma na sake sa an yi ma yarinyar Fadime aiki fa, na kira aljani aka mata magani ta bata, da muka je can garin Garuk ma na fadawa wacan bokan ya nisanta ka da Falmata ya saka maka son Nana, kuma Nana ta lalace, a kashe min Shattima da Mai Martaba saboda na samu Talba ya hau sarauta amman duk na yi a banza...”
Sirleem ya mike tsaye da sauri yana jin kunnuwansa kamar ba za su iya daukar abun da Hajiya take fada ba, da gaske ta aikata ko kuwa dai fitar hankaline ya saka ta haka? Runtse ido yai yana jin duniyar na juya masa, likitan na shigowa sai yai saurin daga kansa sama domin hana hawayen da suka cika idonsa zuba.
_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
58
Ina mata wadan da suke son sayen kaya kamar su laces, atamfa, materials,shadda lace, normal shadda, atamfa lace, veil's, shoes and bags, da sauransu kuzo ga MAMAN AHMAD tazo dan tashare hawayenku kudai kunemeta ta wannan number 08032350261 banan kadai tatsayaba tanada kayan order kama dana kitchen,tufafi,kuma order ta Bata dadewa ,tana saida kayan gyara kamar su Al'ajabu,shu'umar humra wannan inbakida aure Bama saida maki,hadin kaza me yasin,akwai na mallaka wanda wannan ana rubuta shi atafin hannu ke zakiyi wannan,turaren wuta,kulacca,da sauransu
Mazauninsu nanan a samaru Gusau Zamfara state
Muna aika kaya kowace jaha da wajen kasar nan cikin aminci da yardar Allah kunememu kusha mamaki
https://wa.me/qr/MYY56BH3RMFDG1
*Khadeeja Candy*
*BAN YARDA KOWA YA DORA MIN LITTAFI A YOUTUBE CHANNEL BA TARE DA IZININA BA, YIN HAKAN ZAI IYA JEFA CHANNEL DIN CIKIN MATSALA, DOMIN BA ZAN KYALE BA. DON HAKA AKIYAYE!*
Kuka take sosai daker Momy ta shigo da ita cikin falonta.
“Yaushe kuka yi aure?”
Momy ta tambaya cike da mamaki, sai dai Falmata ba ta iya amsawa ba saboda kukan da take, Momy ta zauna kusa da ita ta dafa ta.
“Ki daina kuka kuka ba zai miki maganin komai ba, da kuka yana magani da ya miki magana tun a lokacin da kike matsala”
Iyakar kokari Falmata ta yi na ganin ta daina kukan amman abun ya garara domin zuciyarta ta ki aminta cewar Sirleem ya bar ta kenan a lokacin da take tsananin bukatarsa.
“Ina takardar da ya baki? Ko da baki ya furta miki?”
Falmata ta girgiza kai alamar aa ta nuna ma Momy upstairs, Momy dake tsaye ta nufi upstairs din ta shiga dakin Ameer tana dubawa sai tai arba da takardar a kasa, dukawa tai ta dauka ta bude tana karantawa.
‘Ban abun da na aikata kuskure ba ne sai a yanzu da mahaifiyata ta shiga damuwa saboda ni, Na san kina tsananin bukatata, kuma na san rabuwar mu zai jefa ni a matsala fiye da ke, sai dai ba zan iya kin bin umarnin Hajiya ba, matukar ta bukaci na sake ki zan aikata hakan ko kuwa hakan na nufin karshen rayuwata ne, idan har ta zabi na sake ki, zan aikata haka zan aiko miki ta takardar sakin ba za sake dawowa gareki ba’
“Ta ya akai Sirleem ya auri yarinyar nan? Yaushe? Miyasa ya boye min?”
Momy ta tambaya sannan ta juyo ta fito daga dakin.
“Wannan ai ba saki ba ne”
Momy ta fadi hakan a yayinda take saukowa daga stairs din, sai Falmata ta dago da sauri tana kallonta tare da mikewa tsaye.
“To minene?”
Momy ta karasa kusa da ita ta karanta mata abun da ke rubuce a cikin takardar, sai Falmata ta shaye hawayenta tana jin sanyi a ranta. Momy kam kallonta kawai take irin kallon na na babba da yaro, ko ba a fada ba ta san Sirleem ya kai a so shi amman Falmata ta haukaci tana kuka ya bata mamaki domin a tunanin Momy Falmata bata san wani abu so ba.
“Zauna”
Momy ta fada sai Falmata ta zauna ta sunkuyar da kai kasa. Momy ma ta zauna tana kallonta.
“Yaushe akai auren? Ya akai ya aurenki?”
“Ni ma ban san shi ne mijina ba har sai daren da aka daura auren... ”
Sai ta labartawa Momy abubuwan da ta sani har zuwa yau. Ba karamin mamaki Momy tai ba, so that's mean tun a lokacin da tai masa maganar Ameer kenan yana da wannan plan din ko kuwa daga baya ne? Shiyasa ya ki yarda da Ameer ya aureta? Momy ta sake kallon Falmata tana murmushi.
“Ko da ace Sirleem ya sake ki, na tabbata zai dawo gareki, kin san saboda me?”
Falmata ta girgiza kai alamar aa.
“Saboda yana sonki kuma so ba na wasa ba, duk namijin da zai yarda ya auri mace ba tare da sanin kowa na shi ba kuma auren fari ba dan komai ba sai dan ya taimake ta, to hakika wannan namijin ba karamin sonta yake ba, ko da makoci kike da shi ya damu da ke, za ki jidadi balle wanda ya zabi dauke ke kacokan daga wacan duniyar marar dadi a saka ki a wata rayuwar mai cike da daula da farinciki, kamin ke Sileem yana soyayyah da wata Mansura, amman be duba halin da zata shiga ba, shi ma be damu da duk irin abun da Hajiya da mu yan'uwan mahaifinsa za mu masa ba, ya runtse ido baya ganin kowa sai ke da damuwarki, duk da kasancewar ba ki yi boko ba, kuma ke ba yar wani mai arziki ba ce, Sirleem yana sonki sosai Falmata”
Falmata ta dago ta kalli Momy sai Momy ta kama hannunta ta rike.
“Na jidadin da ba ki auri Ameer ba, da yanzu dan'uwanki kika aura kenan? Kuma na jidadin da zuciya bata saka ni na aikata kuskure ba, da yanzu ban san da wane idon zan kalleki ba ke da dan'uwanki, Na miki alkawari Falmata Sirleem ba zai taba sakinki ba, ba zan bar shi ya sake jefaki a matsala ba, domin ba Hajiya kadai take da iko da shi ba, ni ma muna da iko da shi, kuma Allah be ce a bi uwaye a tsaba masa ba, ki kwantar da hankalinki kin ji?”
Falmata ta daga kai wasu hawayen masu kama da na farinciki da alhini na sauko mata. Momy ta tashi ta shiga kicin ta sake hada mata wani tea tana da godiya ga Allah da be saka ta aikata dashen da kawarta Umaima ta zugata tai ba, kenan da ta yi mata dashe da kwan mijin mahaifiyarta kuma mahaifin yayanta. Falmata ta saka hannu biyu ta karbi kofin tea, tana sha a hankali kalaman da Momy tai mata suna ta mata yawo a kwakwalwa, upstairs Momy ta nufa after like 30 min ta sauko rike da jakarta da makullin motarta.
“Zan tafi gurin aiki”
“Allah ya tsare Momy ya dawo da ke Lafiya”
“Ameen”
Momy ta amsa tana kallonsa sannan ta nufi kofar fita ta fice. Sai da ta ji tashin motar Momy sannan ta aje kofin tea da ta gagara shanyewa ta kwanta kan 3 seater din tana sauke numfashi a hankali, idonta sai ciwo suke. Tana kwance a gurin har aka sallah azahar, sannan ta tashi ta shiga dakin Ameer tai sallah, ta hau gadon ta kwanta tana ta kallon hoton mahaifiyarta, sai kusan uku da yan kintuna Momy ta dawo, sanin ta bar Falmata a gida yasa ta biya tai musu takeaway, da key dinta ta bude kofar falon ta shigo, sai da ta da ta shiga dakinta ta aje jakarta da kayan hannunta sannan ta dauko leda daya ta nufo dakin Ameer inda Falmata take, ta tura kofar dakin a hankali domin a tunanin ko Falmata tana bachi ne sai ta ganta farke tana kwance saman gadon idonta na kan hoton mahaifiyarta hawaye sai sauko mata. Momy ta karasa kusa da ita ta aje mata ledar.
“Tashi ki ci abinci na san ba ki ci komai ba ni ma kuma na dawo a gajiye shiyasa na yi mana takeaway be zama lallai na iya dafawa ba”
Falmata ta yi saurin boye fuskarta tana amsawa Momy.
“To na gode”
Momy ba ta ce mata komai ta nufi gurin da hoton yake ta juya shi, sannan ta fice dakin. Sai da ta fita sannan Falmata ta tashi ta share hawayenta ta sauko kasa ta bude abincin ta fara ci, turashi kawai take ba dan tana jin dadinsa ba, kamar yadda bata jin yunwa haka ma bata jin koshi, damuwar dake ranta ta saka ta ji bata bukatar komai, domin har a yanzu tana sauraren aiken Sirleem na takardar saki kamar yadda ya fada, a iya ganinta mawuyacin abu ne Hajiya ta barshi da aurenta.
Tana cikin dakin akai la'asar, ta shiga bandakin ta sake yin alwala ta fito ta gabatar da sallah, sannan ta daga hannayenta ta roki Allah ya zaba mata abun da ya fi zama alheri a rayuwarta, kuma ya saka komai ya zo mata da sauki kana ya sassauta mata abun da take ji a zuciyarta da kuma wanda take hangowa. Kamar wanda aka kulle haka ta sake zama cikin dakin har aka kira sallah magariba, sannan ta sake shiga bandakin tai alwala, kamin ta fito ta ji lokacin da aka turo kofar dakin aka shigo, sai dai a zatonta Momy ce ta shigo yin wani abu ko fada mata wani abu, hakan yasa tai hanzarin fitowa sai tai arba da Sirleem zaune gafen gadon yana kallon kofar bandakin, tsaye tai cak tana kallon fuskarsa da rama ta samu muhalli a gurin, zuciyarta na bugawa da mugun karfi. Sai ya mike tsaye ya miko mata hannunsa, kallon hannun tai sannan tai je gareshi da sauri ta saka masa nata hannun, sai ya rike gam ya jata zuwa jikinsa yai mata masauki da kirjinsa, kamkamshi tai hawaye na sauko mata, shi kuma ya daga kansa sama yana jin yadda hawaye suke bankwana da idonsa, ashe wani abun ya fi gaban kuka, duk wani abun da za ayi ma hawaye ko kuka mai sauki ne, domin a yanzu shi kasan be san inda hawayensa suke ba.
‘Na gode Allah da na aureki, na gode Allah da ban auri Nana ba, na gode Allah da ban sake ki ba, na gode Allah da gaskiya ta bayyana’
Ya fada a ransa yana tunanin abubuwan da mahaifiyarsa ta fada, taya zai iya labartawa wani cewar mahaifiyarsa ta so kashe mijin da take aure saboda abun duniya? Ta ya zai bar wani ya san kanwarsa ta jini da ita aka hada baki a kashe mahaifinta? Lallai Allah yayi gaskiya domin ya fada a cikin yayanku da matanyenku akwai makiyanku! I can't believe da sa hannun Hajiya a lalacewar Nana, me Shattima ya tare mata har take son a kashe shi? Why all this? Ashe daman akwai manufa a aurensa da Nana? A yanzu auren Falmata ya bayyanar da komai, duk kuwa da kasancewar ba dan auren ne kawai ya saka ta shiga hali ba, ya tabbatar har da alhaki na cutar da innocent people.
IYA POV.
Duk wanda ke gurin tsoron taba ta yayi, saboda tartsatsin wutar da jikin ke fitarwa, ga shi ta saka hannu sai tisgar naman jikinta take saboda zafin yankan da take jin mutanen da ta cinye ma kurwa suna mata ta ko'ina, tun tana yi abun na hankali har ta fara ihu tana fadin ayi mata rai.
“Dan Allah kui min rai! Jama'a wai ba ku ganin abun da nake gani? Ba ku ganin yadda suke yankana?”
Babu wanda yace mata uffan sai kallonta ake, ganin wasu sun fara fito da wayarsu suna daukarta yasa Baba Waziri ya rufe kofafin, ba dan komai ba sai dan mutuncin Mai Martaba.
“Wannan bala'in yayi min yawa, wadannan kaya ina za ninda su?”
Ta fada tana faduwa kasa sai tisgar naman jikinta take tana ihu, sai ta fara mulmula tana jin nauyin dazun yana dawo mata.
“Ku fita waje ku sama manyan sanduna”
Baba Waziri ya fadawa mazan da suke dakin sai uku daga cikinsu suka fita da sauri abun nema ya samu, ba su dade ba suka dawo, Baba Waziri ya ba su izini suka fara labtawa Iya iya karfinsu, wani irin uhu tai sai zabar ta zame mata hudu ga na mutanen da take gani ga yankan da suke mata ga kankarar maitar dake ta mata yawo a ciki tana sakar mata nauyi, ga kuma dukan da take ji ta ko'ina da bata san ta ina yake zo mata ba, dukanta suke duka bana wasa ba.
“Kar a asheta Waziri kar a kasheta”
Ammy ta fada tana hawaye.
“Ba kasheta za ayi ba, ubanta za a ci ta yadda idan akai mata magana za ta ji”
Shine amsar da Baba Waziri ya bawa Ammy, su kam matasan suka saka Iya gaba da duka har sai da suka fitar mata da jini a jiki. Wani abun mamaki ana dukanta tartsatsin wuta na tashi a jikinta, sai da suka kusan kasheta har ta kai bata iya motsi sannan Baba Waziri yace su dakata. Ya motsa kusa da ita ya kira sunanta sai ta kasa amsawa.
“Me zaki yi da kurwar Mai Martaba da kika kama?”
Muryar kawai take ji amman iyakar ganinta bata ganin komai da kowa sai mutanen da ta ci ciki har da mahaifiyarta. Baba Waziri ya sake maimaitawa amman ta gagara amsawa, har sai da ya maimaita sauko kusan hudu.
“Saboda... Na aurawa Shattima Zainab, sai na kashe sarkin sai Shattima ya gaji sarautar su haifa min jika”
Ammy ta dora hannu saman kai tana kalmar shahada, kowa na gurin sai da ya cika da tsananin mamaki, Baba Waziri ya girgiza kai.
“Azzaluma, ke da baki da gadonmu amman kin san ki yi kwadayin sarautar ku? Bayan duk hallacin da akai miki”
Ta motsa daker tana fadin.
“Suna ta yankana”
“Su waye?”
“Wadanda na cinyewa kurwa, ga su sun tsare ni suna ta yankana”
Ta shiga zana sunayensu a wahalce.
“Allah yasa su kashe ki, Azzaluma macuciya, macijiyar soshiya”
Baba Waziri ya fada cikin bakinciki da bacin rai.
“A ina kika rufe kurwar Mai Martaba?”
“Tana gida”
Ta fada kamar wanda ta kusa mutuwa muryar tai mata nisa.
“Tashi muje ki kwance ta”
“Ba kafa, kankarar maita ta min nauyi a ciki”
Ta fada daker tana numfashi a wahale. Sai Baba Waziri yasa mutanen da suka mata duka su jata a kasa, bayan ya bada umarnin a shigo da mota har gurin kofar falon Hajiya Talatu.
Baba Waziri ya saka a ka dauko bargo kato aka rufa mata saboda feshin wutar da take, janta suka fara yi amman suka kasa janta sakamakon wani uban nauyi da tai kamar dutse, sai da suka hada karfinsu suka hadu su biyar sannan suka iya daukarta suka fito da ita waje shi ma daker, a cikin wata hilos aka saka ta Baba Waziri da wasu muhimman mutane suka shiga wata motar, Ammy ta shiga motar ta ita da driver ta sai da suna daf da fita sannan Baba Waziri ya kira Shattima ya labarta masa halin da ake ciki domin tun da akai jana'izarta akai gaisuwa 2pm tai sai ya bar gurin ya koma gidansa. Ko kamin su isa gidan Zainab da ke million quarters Shattima ya