Showing 57001 words to 60000 words out of 286946 words
hakan be hanata fadawa yan ajin su cewar ta hadu da M2 ba, most of them sun karyatata wasu na fadin dan dai tana son shi sosai ne yasa ta ga mai kama da shi.
Haka dai ta bar Islamiya cikin rashin jindadin yadda suka karyarta daman ta san ba za su yarda ba, ita ma dai a lokacin ta fara kwankwanto da gaske M2 ta gani ko mai kama da shi?
Ko da ta iso gida sai ta tararda wani tashin hankali, yaron da aka aiko yana tsaye yana jiran dawowarta Tumba kuma ta yi wani shegen zama tana rawa da kafa. Ta shigo da sallama Tumba ta hau ta da matsifa.
“Ashe Falmata zuwa kike kina cin bashin garin kwaki a shago da sunana?”
Dakan shida-shida gabana yai, ta sani yau asirinta ya tonu, tabbas tana zuwa karba kuma idan ta je Tumba take cewa saboda tana jin kunyar tace ita zai bawa bashin gari.
“Saboda asan ba a baki abinci ko kuma dan ki bata min suna ni da ubanki? To ya aiko yace a bashi kudinshi bari ubanki ya dawo sai kin fadi dalilinki na bata min suna”
Kamar an tureta haka ta fadi gaban Tumba kamar mai neman gafara hawaye sai sallama suke a fuskarta.
“Dan Allah dan darajar Annabi karki fadawa Baba Umma, ki rufa min asiri, zan samu kudinsa yanzu na bashi, ki yi hakuri Umma ba zan, idan na sake ki kashe ni, Umma wallahi yunwa take damuna shiyasa na ci bashin amman daga yanzu ko zan mutu ba zan sake ba, na rantse da Allah Umma, dan manzon Rahama ki rufa min asiri Umma ba zan sake ba har abada”
Tumba ta fisge kafarta tana kallon.
“Tafi idan Babanta ya dawo za a fada masa”
Yaron ya juya ya fice, sai Falmata ta mike tsaye da sauri.
“Na bani na lalace na shiga uku wayyo ni Allah na Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Ta furta ta karfi kuka na subuce mata, sai ta saka hannunta da sauri ta rufe bakinta, da gudu ta shiga dakinsu ta fada kan shimfidar da take kwana.
“Wayyo ni Allah na yau asiri na ya bonu, wayyo Mama Mama ina ma ni na mutu ba ke ba, Allah ka karbi raina kamin Baba ya dawo Allah na shiga uku”
Ta fada tana yarfe hannunta hawaye sai zubo mata suke kamar ba gobe.
ZAINAB POV.
Ta dan yi shiru sannan tace.
“Na ce mishi ya bari har na dawo daga tafiyar da zan yi”
Ammy ta kalleta.
“Ni fa ina tsoron lafiyar nan Zainab, kin san kasar ba wani tsoro kuma ki ce za ki je garin cikin mutanen da ake fadar basa saka tufafi? Kina ganin ma za su aminta ki dauke su hoto ne?”
“No ba wai kai tsaye zanje can ba, zan sauka garin dake kusa da su ne, nai magana da mutanen tukuna sai na isa garin, kuma ko ban samu zuwa can ba ai ance akwai manyan duwatsu a kusa da su da ruwa, kuma ance akwai Fulani irin masu yin bukka da gidan zana su zauna a kusa da su, ko da ban samu isa can ba na san ba zan sara abun dauka ba”
“To Allah dai ya tsare”
“Amin, Ammy dan Allah ki mata magana, ban zan abun da mutunen nan yai mata ba, ta ki ta saurare ni, ni kuma ina son shi, shi yanzu yace yana son ya turo kuma ya sanar a gidansu amman sai ya samu tabbaci daga gareni”
Ammy ta yi murmushi.
“Karki samu damuwa, zan yi magana da ita, idan ta aminta sai a sanarwa yan'uwan mahaifinki”
“Na gode Ammy”
Mikewa tai tsaye tana sanye da riga da wando English wears, kanta sanye da dankwalin nan da ake yayi blue.
“Bari na duba dakinta idan tana nan sai na turo miki ita”
Kai kawai Ammy ta daga mata, ta maida dubanta gurin tv dake dakinta, kallon kawai take amman hankalinta baya can, bata da damuwar da ta wuce ta Mai Martaba a yanzu, a iya tunaninta ta rasa gane abun da yake damunsa, gashi idan an gwada yi masa na hausa sai abu ya karu a maimakon raguwa. Kiran wayarta nd ya katse mata tunanin da take, sai ta mika hannu ta dauka.
“Assalamu Alaikum”
Ra'ees ya amsa daga dayan bangaren.
“Wa'alaiki-Assalam, Ammy barka da yamma”
“Yauwa Ra'ees ya gida”
Ta fada cike da kasaitar da ta zame mata jiki.
“Al-hamdulillah Ammy an samu wata, amman dai ba mu je, sai dai marikiyar yarinyar tace zata iya aura masa ita”
“Ka fada mata matsalar sa ne?”
“Eh ta ji komai, firar ma ta ji muna yi shine tace tana da ƴa zata ba shi, amman dai ba mu je ba tukuna”
“To yayi kyau, amman fa ba sai kun bayyana dan wane ba, kuma ka yi duk abun da ya dace, karka bari Shattima ya ji komai, sai an kammala yadda ba zai iya ce mana aa ba”
“In-Sha-Allah Ammy”
“Na gode Allah ya maka albarka”
“Ameen”
Tana kokarin aje wayar aka kwankwaso kofar dakin kamin a turo a shigo. Hajiya Balki ce Nana na biye da ita a baya, a baki kofa ta tsaya tana kallon Ammy sai cika take tana batsewa.
“Yanzu an kyauta kenan? Sai a dauke yarinya akaita gurin Waziri bayan kin san ita da Waziri ba jituwa suke ba?”
Ammy ta kalleta da mamaki kamar ba zata ce komai ba.
“An kaita gidan Waziri kamar wacce aka kai gidan yari? Kanen ubanta ne fa”
“Na san kanen ubanta ne ai, amman tun da bata son zuwa ai sai a kyaleta”
Ammy ta dauke kai bata sake ce mata komai ba. Ganin hakan yasa ta juya ta fita Nana kuma ta zauna saman kujera tana matsar yatsun hannunta tana kallon Ammy. Ko da wasa Ammy bata kalle inda take ba har ta gaji dan kanta tace.
“I'm sorry”
Ammy ta watsa mata wani mugun harara.
“Dakinki dai kike so ko? To gashi can idan kin mutu a haka rame a saka ki a ciki, tashi ki fata”
“Ammy ki yi hakuri....”
Bata karasa ba Ammy ta daka mata tsawa.
“Get out”
Ba shiri ta mike tsaye jikinta na rawa ta fice daga dakin tana fashewa da kuka.
_________________
Al-hamdulillah, a nan na kawo karshen free pages, duk mai son cigaban wannan labarin ya biya 300. Pages din da za su biyo bayan wannan na kudi ne ba kyauta ba, ko kun ganshi a waje na sata ne.
Patronize me if ku masoyana ne na gaskiya, show me that love.
Son so Fisabilillah.
*FULANI -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence to 08036126660 ƴan nijar za ku tura 500cf to +22790165991*
Wadanda ba su account za su iya turo mtn card ta 08036126660 bana karbar transfer.
16
A gaban wani madaidacin gate ya faka motar, budurwar ta bude ta fita sannan ta budewa Falmata tana mata alama da ta fito.
Cikin rashin kuzari Falmata ta sako da kafafuwanta sannan ta fito daga motar tana jin sanyin ace motar na saukar mata da mura, sai kokarin boye ledar hannunta take tana karewa na unguwar kallo, ba unguwar masu kudi bace haka kuma ba za a kirata da unguwar talakawa ba, irin unguwar nan ce mai kama da sabuwar unguwa wance mutane ba su gama dawowa ba, domin akwai gine gine da yawa da ba a karasa ba, ga kuma ciyawa da tai yawa a ko'ina, tsakanin wani gidan da wani kuma akwa tazara mai tsawo ta filayen wasu mutane. Hannu ta saka a jakarta ta ciro makulli tana kikarin sakawa sai gate din ya bude, ta dan bude ido da far'a sannan ta tura ta shiga.
“Shigo”
Bayan Falmata ta shiga ta rufe kofar gate din, arba da tai da wata hadaddiyar mota yasa murmushin fuskarta ya kara fadada da sauri ta nufi entrance har tana hadawa da gudu, hakan kuma ba karamin tsoro ya ba Falmata ba, tana a wani gari da ba na ta ba, a wata unguwa kuma a sabon gida da matar da bata sani ba.
“Karaso mana ko kina jin tsoro ne?”
Matar ta fada ganin Falmata ta tsaya daga can kusa da gate din tana karewa madaidacin gida kallo. Sai da ta tura kofar falon sannan Falmata ta karaso kusa da ita
“Shiga”
Cikin tsoro da fargaba ta nasa kafarta a cikin falon, bayan ita ma ta shiga ta maida kofar ta rufe.
“Zauna a nan”
Ta nuna mata kujera, cikin rashin natsuwa ta zauna saman kujerar dake kusa da kofa.
“Mansura daga ina kike?”
Budurwar ta juyo da sauri tana kallon kofar kitchen din. Sirleem ne tsaye jikin kofar rike da gorar ruwa yana kallonta. Cikin murna ta karasa kusa da shi ta rumgume shi.
“Oyoyo ban taba expecting zaka zo yau ba, what a surprise”
Ya dan kawar da fuskarsa daga kiss din da take kokarin yi masa yana kallon Falmata, juyawa ta yi ta kalleta sannan ta sake kallonsa tana kokarin kai hannu ta taba sajen fuskarsa, sai ya rike hannunta ya tureta gefe ya dawo falo ya zauna.
“Na hadu da ita ne a tasha, an kawo min sako daga kano shi ne na je karba sai na hadu da ita, tun cikin tasha tana kuka har waje da na tambaye ta sai tace bata san kowa ba a nan gudowa tai”
Tun da ta fara maganar yake kallon Falmata yana jin kamar ya taba ganin fuskarta but zai iya tuna a ina ba ne. Ya kalleta a natse irin kallon da ita ta san me yake nufi. Sai ta nufo shi tana cire Veil din kanta.
“You know idan na ga mutum a damuwa ina son na taimaka masa, because ni ma na taba shiga a irin wannan matsalar”
Ya sake kallon Falmata da tai mutuwar tsaye tana kallonsa. Shi din ne ko kum har yanzu idonta gizo yake mata? Ko kuma masu kama da shi ne take gani? Ai ta baro yola ya akai ta ganshi a nan?
“Me yasa ta gudu daga gidansu?”
Ta zauna daf tashi har jikinta na gogar nashi.
“Ya za a yi na sani yanzu yanzu fa na hadu da ita ban tambaye ta ba”
“And kika bata masauki, what if karya take? Kika san abun da ya rabota da gidan?”
“Ban sani ba, amman zan sauketa a nan zata zauna tare da ni, tana bukatar taimako”
“This is my own house not yours, hope kin san da wannan?”
“And that mean?”
“Ba zata zauna a nan ba”
Ya fada mata kai tsaye yana kallon cikin idonta, fuskarsa babu annuri.
“Fine idan baka son ta zauna tare da mu, zan sallame ta, amman rayuwarta zata iya fadawa a hadari ka sani”
Ya mike tsaye yana shafa kansa.
“Idan rayuwarta ta fada a hadari ina ruwanki? Kin santa ne? Idan kina tsoron ta fada a hadari then take her to her parents house”
“Amman ka san abun da yasa ta baro gidansu? Duk ba mu sani ba bata son zama kusa da kowa na ta that's why she run”
“Kin fi kowa sanin hali da mace take fadawa idan ta rubu da iyayenta, uhmmm?”
Ta yi shiru tana kallonshi.
“Lokacin da kika gudo daga gidan iyayenki da kika fada mugun hannu ba karuwanci kika fara ba? So on kika bata future dinki that's why Hajiya ta hana na aureki, kowa kallon karuwa yake miki kina son ki koma cikin familynki kin saka saboda kin lalata alakarki da su, look at her bata wuce 15 ba, and if you want to help her take her back to her parent house”
Hawaye ne masu zafi suka fara sauko mata, ta kalli Falmata a tsawa ce tace.
“Ke tashi ki fita”
Falmata ta kasa motsi balle ta mike tsaye ta fita kamar yadda ta umarta, bata ji duka kalmansu ba amman ta ji wannan tsawar kuma ta ji turancin da Sirleem yai mata a karshen maganarsa da ya karasa a fusace, and now hawaye Mansura take, hakan na nufin matsala ta samu da mijinta a dalilinta.
“As how? Ki kawo ta unguwar da bata san kowa ba kuma ki ce ta tashi ta tafi idan aka tambaye ina ta fito tace a nan gidan ko?”
“To ya kake son nai mata?”
Ta fada a tsawace tana hawaye, tass ya wanke mata fuska da mari.
“How dare you, dan ina son ki ba shi zai baki damar yin duk abunda kike so da ni ba, kamar yadda so na be hanaki kula wasu mazan ba”
Sai a yanzu ta gane fushinsa ba na shigowa da Falmata kawai ne ba, har na fitar da tai da Yasir, durkushewa tai a gurin ta fashe da kuka. Falmata dake rike da fuskarta sakamakon marin da akai wa Mansura ta mike tsaye ta sauri ta nufi kofa.
“Ke....”
Ya kirata a watsawa sai ta juyo jikinta na rawa ta fashe masa da kuka tana girgiza kai. Kallonta kawai yake kamin ya nuna mata kujera alamar ta zauna, sai ta dawo kusa da kujerar ta zauna a kasa tana hawaye. Ganin tana ta boyon hannu a hijab ga hawaye sai sauko mata suke yasa ya nufo inda take sai ta kara fashewa da kuka tana bashi hakuri.
“Dan Allah kai hakuri, dan Allah karka min komai”
Hannunsa ya kai ya daga hijabinta sai ta mike tsaye tai saurin sakin ledar hannunta shinkafar dake ciki ta fadi kasa. Kallon shimkafar yai kamin ya sake kallonta da fuskar dake nuna alamar ba wani abun zai mata ba, cikin tattausan lafazi ya ce.
“Daga ina kike?”
Bakinsa kawai take kallo kamin ta kalli fuskarsa da kwarjininsa ya cika mata ido.
“Bana ji sosai sai an yi kusa da kunnena ko an fada sosai”
Kallonta kawai yake for no reason, kamin ya kai hannanyensa ya dafa kafadarta ya zaunar da ita saman kujerar.
“Ya zaka taba ta, ina ruwanka da ita”
Ta fada tana mikewa tsaye ta nufo inda yake tsaye kusa da Falmata. Dan murmushi yai irin murmushin nan na mamaki daman ya san za tai magana, saboda Mansura tana kishinsa ko sunan wata macen ya fadi a gabanta sai ta nuna kishinta, amman ita ta kasa tsare masa kanta duk kuwa da irin kudirin da yake da shi na aurenta.
Falmata ta kalleta a tsorace gaba daya ta firgice ta rasa gane kansu yanzu, gashi ba komai take ta ji ba. Juyowa Sirleem yai ya kalleta sai ya nuna mata kofa alamar ta tashi ta fita, sannan ya juyo ya kalli Mansura.
“Me yake damunki ne Mansura?”
“Kai ba ka ga abun da kake ba?”
Be ce nata komai ba ya hade rai ya fara bin bayan Falmata sai ta riko rigarsa.
“Ina zaka je? Ina zaka kaita?”
“Ba zan ga wata mace zata aikata irin abunda kika aikata ba na kyaleta, sake min riga”
Ta saki ba dan ta so ba, sai dan ya karasa a tsawace yana kara hade rai kamar be taba dariya ba. A kujerar ta Falmata ta tashi Mansura ta zauna ta hade kai da hannu tana hawaye wani irin abu take ji a zuciyarta yana taso mata, ta san waye Sirleem bayan ita baya mu'amala da ko wace mace amman tana kishin ganinsa da mace ki da ko yar'uwarsa ce. And the most annoying part is duk abunda za tai ba zai saurareta ba a yanzu saboda ta fita tare da Yasir, da ace a gida tararda da ita, to zai saurari duk kalar haukar da zata masa saboda yana sonta shi ma.
Ya sauka entrance din yana kallon Falmata da ta kusa isa gate tana waigensa, motarsa ya shiga yai warming dinta sannan yai reverse ya isa gate din da Falmata ta kasa budewa, fitowa yai daga motar ya zagaya ta dayan bangaren ya bude mata front seat, da hannu yai mata alama da ta zo sai kawai ta fashe da kuka ta dukushe a gurin tana girgiza masa kai.
“Ba wani abun zan miki ba”
Ya fada cikin daga murya, sai dai ba irin muryar da zata ji ta tsorata ba, ni ta yadda zata ji shi.
“Aa bana so”
Ta fada hawaye na sauko mata, tana jin wata sabuwar nadama da dasani na barin garinsu da gidansu da ke cike da kuncin rayuwa, gaba daya ta tattara zancen da tunanin Sirleem ne ki ba shi ba ta aje a gurin daya, ta rayuwarta take. Ya rufe motar ya karasa inda ya risina yana kallon fuskarta da tsoro ya gama bayyana a kammaninta.
Dark skin dinta sai shining take duk da kasancewar kana ganinta kasan rayuwar wahala take, ga golden eyes dinta masu haske da take ta kallonsa da su. Kallonta kawai yake zuciyarsa na raya masa ya santa amman a ina? The first thing daya kamata yai shi shine ya gusar da tsoronsa da take ji a yanzu, ya kara matasawa kusa da ita sosai kamar zai tabe ta.
“Kin san ni?”
Ya rada mata da a kunne. Sai ta yi shiru tana ta kallon fuskarsa da sajensa da ya karawa fuskar kyau. Bata son tace eh ko aa tun da bata da tabbacin shi din ne Sirleem ko waninsa? Ko kuma gizo idonta ke mata.
“Kin taba jin wani Sirleem M2 mai waka? Ko ganinsa ko da a hoto ne?”
Nan ma shiru tai sai dai ta dan bude ido alamar wani abu ya zo a tunaninta. Ya dan kalli kofar falon sannan ya sake kallonta ya kai bakinsa kunnenta.
“Kin san shi?”
Ya gyada kai sai ya saka mata murmushi ya nuna kansa. Da wani irin karfi zuciyarta ta fara bugawa tana kallonsa.
“Ji nake kamar na sanki a ina na sanki?”
Kallonta take kamar ba zata ce komai ba, a yanzu ba kallon tsoro take masa ba na mamaki da tunani.
“Ka taba kade ni a mota”
Yayi shiru yana nazari, sai ya sake sakar mata murmushi.
“Yeah few days back ko? Har na baki fula? Amman ai a Yola ne”
Ta daga masa kai ba dan ta san abun da yake nufi da few days din ba, sai dan karasa mata maganar da yai da zancen bata fula ta kara tabbatar da shi din ne ba tantama. Sai ya dan bude ido yana kallon kyakkyawar fuskarta.
“Hakan na nufin ke yar garin mu ce”
Ta sake gyada kai tana nuna shi.
“Da gaske kai ne?”
“Ni ne mana”
Ya fada yana daga mata kai ba dan yana da tabbacin zata ji ba, tun da ta fada masa bata ji sosai kuma ya ga zahiri sai dai daga mata kan da yai ya isar da sakonsa. Da