Showing 42001 words to 45000 words out of 209297 words
suna shaƙuwa da juna.
Widad sam tun haihuwarta, rayuwarta tafi a ƙasar waje, idan sunzo Nigeria to hutu sukazo ko kuma ziyara, gashi Huda ba wani Hausa takeji ba, tama jin Husa amma ba sosai ba, dan haka wasu abubuwan duk Widad bata sansu ba.
Nasir ya haɗa kai da wasu 'yan china, suka buɗe wata katafariyar ma' aikatar harkar kwangila, na gine ginen tituna, da shigo da kayan gini, ya jawo matasa sosai cikin harkar, bayan wancan kamfanin ƙarafa da yake dasu, da sauran manyan kadarorinsa na mamaki, dan har rijiyar mai Daula ya mallaka, kullum Arziƙinsa gaba yake, baya baya, gashi ba wani babba ba a a wannan lokacin, amma ya tara Arziki da shahara.
Shekarun Widad bakwai a duniya, har Huda sun fidda ran samun wani ɗan, kawai ta tashi da matsanancin ciwon ciki, tayi zaton ɓacin cikine kawai, amma ta wuni a kwance, hakan yasa Daula ya ɗauketa zuwa Asibiti, a nan aka tabattar masa da tama ɗauke da juna biyu.
Daula ya rasa inda zesa kansa dan farinciki, sunyi murna sosai da samun wannan cikin, nan ya ƙara ririta Huda fiye da yadda yake yi a baya.
Da tayi motsi se yace "me unborn ɗina yake sone, har Widad ta fara kishi tace "Daddy, wai yanzu kafin son unborn ɗin nan ne dani?"
"wane ni, ga gimbiyata ince nafison wani dake, ai you are my forever Queen, babu wanda ze rusamin fadarki, kiyi yadda kike so Gimbiyar Daula'
Ire iren wannan kirarin, da soyayyar da mahaifinta ke mata suke fasa mata kai, Widad bata taɓa kukan babu ba, bata san ta nemi abu ta rasa shi ba, haka ta taso cikin zunzurutun jin daɗi da dukiya ta ban mamaki.
Tun Widad tana ƙarama take bada kyauta, idan Daula ya ga dama, se yace "Ran Gimbiyata ya daɗe, ga wane me kike so a bashi?"
Duk abunda ta faɗa ta zauna, se an bawa mutum, Huda taita mita tama ya fiye sangarta Widad, shi kuma ya kance idan banyiwa Widad abunda takeso ba se yaushe? Idan na mutu bata mori dukiyar mahaifinta bafa?"
Ya sai kadarori da sunayen Widad, kadarorin daya siya da sunanta basu da adadi, Widad komai yi mata akeyi, suna da nanny.
A hankali Huda taga idan ta biyewa Daula, to Widad zata tashi a sangarce, dan haka take ɗan koya mata waus abubuwan, kamar gyaran ɗakin data kwanta, ɗauke kwanon Abinci, da shara daidai wadda zata iya.
Katsam bayan tenure Musa ta farko, yana ƙoƙarin ya koma, labarin irin almundahanar da Musa yayi ta iske Daula, abun yayi masa ciwo, ya goyawa macuci baya ya jagoranci al'umma, amma ƙarshe ya zalunce su, Daula da kansa ya kai Musa EFCC yace su tuhume shi, a bincike shi ya fito da haƙƙin mutane.
Abun ya bawa mutane mamaki, ganin shiya kawo Musa Siyasa, amma da kansa ya kaishi gurin hukuma, sannan yace bashi bashi, kuma duk hukuncin daya dace ayi masa.
Gaba ɗaya siyasar Musa, da mutuncinsa ya zube a idon mutane, dama farin jinin saboda Daula ne, mutane suka juya masa baya.
Ƙarshe da kyar ya sha a hannun EFCC, dan seda aka kaishi prison a ƙasƙance, aka ƙwace wasu daga kadarorin da ya mallaka, a wannan lokacin abubuwa basu taɓarɓare kamar yanzu ba, da ƙyara wasu daga 'yan siyasa suka dinga shiga suna fita, seda Musa yayi watanni shida a prison, sannan aka sako shi da kyar, shima se da aka ƙwace masa passport, dan gwamnatin lokacin ba tasu bace.
Wannan dalilin yasa Musa ƙulattar Daula, ya manta duk alkhairin da Daula yayi masa, ya manta yadda ya tsamoshi daga ƙangin talauci da shaye2, yayi aniyar rama abunda Daula yayi masa kota halin ƙaƙa, yayi Alƙawarin tozarta shi da wulaƙa ta shi, kamar yadda yayi masa, yayi alwashin ɗanɗanawa Daula baƙin ciki mafi muni a rayuwarsa, tunda ya ɓata masa suma ya lalata masa siyasarsa.....
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: .LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
68_69
Cikin Huda ya ci gaba da girma, yayin da gefe ɗaya Daula ya fara tara maƙiya da mahassada, danshi duk abunda zeyi be yadda da cuta ko ha'inci ba, komai nasa tsakani da Allah yake yinsa, ga gefe guda mutanen daya ƙwacewa kasuwar wasu abubuwan, suma suka sako shi gaba suna jin haushinsa.
Wata gidan Talabijin yayi hira da Daula, akan yadda akayi ya fara kasuwanci, nasarorin daya samu da kuma ƙalubale, duk ya dinga bada amsa, gashi duk hirar da za'ayi dashi se yayi zancen Yayansa Yusuf, se yayi musu addu'a, duk inda me Suna Yusuf yake Nasir kamar ze duƙa masa saboda girmamawa, komai ƙanƙantar Yaro indai yana da wannan sunan, to tabbas yana da ƙima a idon Nasir.
Babban abunda ya daɗa ja masa baƙin jini shine, yadda yakewa al'umma hidima, yake facaka da dukiyarsa gurin hidimtawa al'umma da addini, wanda sauran abikan kasuwancinsa basa yi, hakan yasa ya ƙara samun masoya ta kowane fanni.
A cikin hirar da'ake dashine ya bayyanawa 'yan jarida cewar, shifa ainihin kuɗin daya fara kasuwanci dasu bashi aka bashi, kuma be biya bashin ba, ya sanar dasu cewa wanda ya bashi bashin ya gaya masa me kuɗin yana nam zuwa ya karɓi wannan kuɗi, dan haka gundarin dukiyar da yake juyawa yana samun riba akwai me ita, kuma duk sanda lokaci yayi indai me dukiyar ya bayyana to tabbas shi keda kaso bakwai cikin goma na dukiyar daya mallaka, ya ƙara da cewa a hirar nan da suke, tuni ya ware wannan dukiyar guri guda, ko bayan ransa duk wanda yasa hannu akan wasiyyar daya bari da takaddun dukiyar daya ware, to tabbas wannan dukiya tasace, ko waye yasa hannu akai tasa ce "
Wannan hira da Daula yayi ba ƙaramin cecekuce ta janyo ba a cikin al'umma, wasu suna jinjinawa amanarsa, wasu suna ganin wautarsa suna inama zasuga inda tajaddun suke su saka hannu su karɓe kuɗaɗen, wanda suke da hannun jari a kamfanunnukansa suka shiga zullumi, akwai dukiyarsu a cikin kuɗaɗen Daula, kuma muddin ya janye daga kasuwancin to tabbas zasu talauce, dan haka suka shiga tunanin nemawa kansu mafita.
Katsam akayiwa Huda scanning, aka tabattaf da cewa tana ɗauke da ɗa namijine a cikin ta, ana gayawa Daula ya zube yayi sujjadar godiya ga Allah, bakinsa yaƙi rufuwa, farincikinsa yakasa ɓuya.
Sunyi murna sosai da wannan kyauta da Allah yayi musu, Kasancewar Daula ya daɗe yana kuma neman haihuwa yasa shi, ya shiga gayawa abokansa ai Madam ta samu rabo, kuma anyi scanning ance zata haifi namiji, zatonsa duk masuyi masa dariyar nan masoyansa ne, zasu taya shi farinciki, ashe abunda be sani ba ta ciki na cikine kawai, dan gaba ɗaya ba ƙaunarsa suke ba, dukda da yawa su, Daula shine silar Arziƙinsu.
Watarana suna zaune suna hira da abokansa, suke bugun cikinsa Haruna yace "Yanzu kai Daula, gashi ga abunda kace akan cewa akwai me kaso bakwai na dukiyarka, yanzu idan ba'a samu wanda yasa hannun bafa? Sannan meyasa me dukiyar baze zo ya karɓa ba"
Daula yace "me kuɗin, yayana ne da matarsa da Allah yayi musu rasuwa, kuma shi ya gayamin akwai wanda ze karɓi wannan kuɗin, dan haka nayi a rubuce ko bayan raina idan mesu bezoba, a rabawa al'umma su, ko kuma a gina abunda al'umma zasu amfana"
Haruna yace "duk wannan uwar dukiyar, kace a rabar?"
Nasir yace "eh mana, haka shine yakamata ai, har wasiyya nayi yadda na kasafta dukiyar"
"to yanzu a ina suke, balle mesu ɗin yasa hannu ya karɓa?"
Daula yace "idan har me dukiyar nan yazo, no matter how hard seya karɓi abarsa, babu wanda yasan inda suke, se Allah seni, nayi bayanin komai a video wasiyyar dana bari, na danƙashi a hannun 'yata Widad"
Munir yace "Widad kuma? Wannan jaririyar yarinyar?"
Daula yai murmushi yace "wannan Yarinyar, yadda kanta yake lissafi naka bayayi, a hakan tayi min alƙawarin zata adana wasiyyata kamar yadda zata adana Ranta daza ta ganshi"
Haka sukayi ta bugun cikin Daula, wani abun ya gaya musu, wani abun ya waske shi duk a ganinsa an zama ɗaya, har yake labarta musu ai matarsa namiji zata haifa.
Cikin Huda yana da watanni bakwai, ta dage tace ita seta koma Nigeria a can take son ta haihu, Daula ya kaɗa ya raya tace ita Nigeria takeson ta koma, yanzu zaman nan ya isheta.
Haka Daula ya tattara ya dawo Nigeria, dama akwai katafaren gidansa me girman gaske, inda suke sauka idan sunzo, akwai ma'aikata a gidan saboda girmansa, dukda babu kowa a gidan akwai megadin gidan Bala, Sojane shiyake kula da shuke shuke da sauran al'amauran gidan idan basa nan, gidane har gida katafaren gaske me matuƙar girma da yalwa.
Suka koma Nigeria suka sauka a wannan gidan, lokacin da cikin Huda ya shiga watanni takwas tafiya ta kama Nasir ta gaggawa, Huda haka nan taji bata son ya tafi, ta dinga masa Shagwaɓa harda kuka ita karya tafi.
Widad ganin Mamanta na kuka, hadda shagwaɓa yasa tace "da nice da yanzu Ammi kin koreni kince na fiye takura, shine kikewa Daddy kuka ko? Daddy ka ƙyale Ammi shagwaɓabiya"
Nasir yayi murmushi yace "my princess gayamata dai, kalli tana kuka kaman baby"
Widad suka haɗu ita da Babanta suka dinga tsokanar Huda suna dariya, akwai kyakkyawar fahimta da ƙaunar juna a tsakaninsu, haka yaita rarrashin Huda, harta haƙura ta ƙyaleshi ya tafi, ita dama tsoromta bata son ya tafi daga ita se Widad a gida ga tsohon ciki.
Kwana biyu da tafiyar Daula, cikin dare sun tsaka da bacci, Widad ta tashi ta shiga kiran "Ammi, Ammi ki tashi"
Cikin bacci Ammin Widad ta farka tace "lovely lafiya kuwa?"
"Ammi yunwa nakeji"
"Widad yunwa cikin daren nan kuma?"
Widad ta jinjina mata kai, Huda tace "Widad kin fiye rigima, ko tausayin halin da nake ciki bakya yi, tashi muje in haɗa miki"
Haka ta kama hannun Widad zuwa kitchen, ta haɗa mata Frisco ta samata madara ta bata, Widad ta zauna tana sha, yayin da Huda keta hamma saboda bacci.
Widad ta kalli Amminta tace "Ammina kije ki kwanta, idan na gama nima zanzo in kwanta"
Huda tace "kin tabatta bazaki min fitina ba?"
Widad tace "yes Ammi, i promise you i won't do anything bad"
Huda tace "Yawwa my lovely friend, barakallahu fik"
. Ta sunkuyo ta sumbaci goshin Widad, itama ta sumbaci goshin Amminta, har taje bakin ƙofar kitchen ɗin, Huda ta juyo ta kalli Widad ta ɗaga mata hannu, itama ta ɗaga mata, Huda tace "Babyna, ki zama me riƙon Alƙawari, sannan karki zama me manta alkhairi"
Widad tayi murmushi, ta jinjinawa Amminta kai.
Tafiyar Ammin ɗaki ba daɗewa, Widad taji kamar ana taɓa gate ɗin gidansu, ga Ƙaton karensu yanata zabga haushi, a zatonta ko Daddynta ne ya dawo a daren nan, dan haka ta taka kujera, ta hau kan drower ɗin kitchen, ta leƙa Window, da yake gurin a saman bene ne, hakan ya bata damar ganin abunda ke faruwa a ƙasa harabar gidan.
Ƙaton police dog ɗin nasu yake ta haushi yana zagaye, a harabar gidan, Bala soja ya kama karen ya maida shi ɗakinsa ya rufe, sannan yaje ya zare sakatar dake gate ɗin.
Wasu mutane ne suka shigo cikin gidan, sun kai su biyar fuskarsu ɗauke da mask baƙi, baka gane fuskokin su, ga manyan bindugu a hannunsu.
Tunani Widad tayi, a irin fina finan da take kallo, idan akaga mutane da irin wannan shigar musamman cikin dare, to they are dangerous, tana nan akan drower taga Bala yayi musu jagora har ƙofar da zata sadaka da cikin gidan.
Ya buɗe musu ƙofar suka shiga, Widad ta sakko daga kan drower a hankali, ta leƙa ta ɗaya window, tana gani suka shigo babban falon ƙasan benen, suka shiga haurowa saman benen, komawa tayi ta ɓuya suka buɗe ƙofar ɗakin da Huda take ciki suka shiga.
Suna shiga Widad ta fito daga kitchen ɗin, tana tafiya a hankali tazo ta window dake corridor ta tsaya ta Leƙa window a hankali, cikin sanɗa take komai.
Tana gani ɗaya ya kunna fitila, haske ya gauraye ɗakin, Huda ta buɗe ido tana salati, nan da nan ɗayan ya janyo pillow ya danneta, ta dinga mutsu mutsu tana fizge fizge, Kasancewar ƙaramar rigar bacci ce a jikinta, kana iya ganin yadda cikin dake jikinta ya dunƙule guri ɗaya.
Widad tana tsaye tana kallonsu, ta toshe bakinta da hannunta, tana ta gumi jikinta yana tsuma, ƙafafunta se rawa suke, tun Huda na iya mutsu mutsu da ƙoƙarin ƙwacewa, ɗaya ya zaga ya hau kan gadon ya riƙe hannayenta, tun tana motsa ƙafafunta, har rai yayi halinsa ta dena motsi.
Widad na zuwa nan kawai ta rirriƙe Yusuf ta fashe da wani irin kuka me matuƙar ban tausayi, ba Widad ba shi kansa Yusuf seda jikinsa yai sanyi, labarin ya ratsashi sosai, tun daga rayuwar iyayenta zuwa kanta a cikin ƙaddara take, rungumeta Yusuf yayi yana shafa bayanta da sigar rarrashi, amma ya kasa magana sam se Ajiyar zuciya.
Ganin Widad bata da niyyar sassauta kukan da take yasa Yusuf ya fara magana, cike da rauni da tausayawa yace "Am very sorry dear, ubangiji Allah jiƙansu gaba ɗaya, take heart Widad, Allah ya jiƙan Ammi"
"Yoseef, my Mum was killed before my eyes, a gaban idona aka kashemin ita, bayan an san bani da gata se Allah se ita da Daddy na, amma without fear, she was killed mercilessly, ga tsohon ciki, how can I forget this in my life, how?"
Jikinta har tsuma yake saboda kukan da take, ga wani irin numfashi da take jerawa, Yusuf yace " tabbas an cutar da ahlinku, cutarwa mafi muni Widad, amma kiyi haƙuri ki miƙa lamarinki ga Allah, dama Allah yayi a lokacin mahaifiyarki zata rasu, bawa baya wuce lokacinsa"
Widad tace "na sani, da Ammi mutuwar Allah tayi, bazan cigaba da damuwa tsawon wannan lokacin ba, nasan lokacinta ne yayi, amma aka kasheta da tsohon ciki laifin meta yi? Me tayi musu zasu kashemin ita Yoseef?" ta maganar muryarta na sarƙewa.
Seda Yusuf ya zubda hawayen tausayin Widad, ya shiga share mata hawayenta yana, " kiyi haƙuri, mucigaba da yi musu Addu'a, kidena wannan kukan, Allah yayi mata rahama, take heart "
Shaƙuwa Widad ta dingayi, numfashinta yana sama yana ƙasa, gigicewa Yusuf yayi ya shiga kiran sunanta, tana jinsa amma bata iya magana hannunsa ya ɗora akan ƙirjinta ya shiga karanta mata duk abunda yazo bakinsa, na ayoyin alƙur'ani.
A hankali ta dinga sauke ajiyar zuciya, ta dena shaƙuwar, Yusuf yace mata sannu, jinjina masa kai kawai tayi.
Yace "dare yayi sosai yanzu, ma cigaba wani lokacin, ki kwanta ki huta"
Ta jinjina masa kai, ya gyara mata pillow ya kwantar da ita ze miƙe, ta riƙe hannunsa, ya kalleta yace "ya dai?"
"Akwai hadari a garin, akwai yuwuwar ayi ruwan sama, ka kwanta anan kawai".
Yusuf yace "to ai ba'a fara ruwan ba"
"Eh bakomai ka kwanta, i need a shoulder to cry on, ka kwana a kusa dani"
Har yanzun dai kuka Widad take yi, ya kwanta ya ɗora kanta a Ƙirjinsa, ya dinga sauke ajiyar zuciya, tana cigaba da zubar da hawaye.
Yusuf yaja wata doguwar ajiyar zuciya yace "Gimbiya kina son ki karyamin zuciya ne in cigaba da kukan nima?"
Girgiza masa kai tayi, yace "kinga har shaƙuwa kikeyi, kin kusa shiɗewa ɗazu saboda kuka, kiyi haƙuri dan Allah ki dena haka ya isa, yi shiru muyi musu addu'a"
Widad tace "karka damu da shiɗewar da nayi, bayan ciwon hauka inada ciwon zuciya kamar Daddy na, dan haka ba wani abu bane, nasan idan kwana na ya ƙare zanbi Ammi na ne"
"Widad bakya tausayina ko? Baki damu da ki dinga gayamin zaki mutu ki barni ba ko? Babu ruwanki da halin da zan shiga idan kika mutu kika barni bako?"
Ɗago kanta tayi tana kallon Yusuf, dukda a cikin duhu suke amma ta kai hannunta fuskarsa taji ɗumin hawaye a fuskarsa.
Murmushi tayi tace " Ragon maza kawai, ɗan sanda yana kuka, se kace ba jarumi ba, ni meyasa ka damu dani haka baka son in mutu in barka? Dukda tarin rashin kirki na a gareka"
Tai maganar cike da son bagarar da wancan zancen da suke.
Mirginata yayi ya koma kanta, a hankali ya kai fuskarsa kunnenta yana mata numfashi a kunne sannan yace "saboda ni bana ganin laifinki, kuma ni bana riƙo ina sonki sosai, kuma ba kince ni ɗan uwanki bane?, kuma seki tafi ki bar ɗanuwa haka akeyi? Bakya tunanin halin da ɗan uwa ze shiga? Anya kina 'yan uwantakar dani kuwa?"
Murmushi tayi tace "wani lokacin inayi, wani lokacin kuma ba nayi"
Tai maganar tana dariya, ta rungume Yusuf tace "dare yayi sosai, muyi shiru haka mu kwanta"
Yusuf ya sake gyara kwanciyarsa a jikinta, yayi shiru wani irin matsanancin tausayin ta yana ratsa ransa, daga ita har mahaifinta kowannen su yaga ƙaddarar rayuwa daban daban.
A haka har bacci yayi awon gaba da dukkaninsu.
Alhaji Musa yana zaune yana karyawa da safe a falonsa, wayarsa ta fara ringing, ɗaukar wayarsa yayi ya tafi bedroom, ya rufe ɗakin ya saka key sannan ya ɗaga wayar.
"Ka kasa kunne yau, zakaji matakin dana ɗauka akan Yaron nan, dan haka ka kwantar da hankalinka babu abunda ze faru"
Ajiyar zuciya Musa yayi yace "Alhamdilillah, Insha Allah zan saurara inji wani irin mataki ka ɗauka akan lamarin, amma to batun Daula fa? Har yanzu fa babu wani labari a game da shi, ya muke ciki a wannan ɓangaren?"
"Karka damu, shima ina nan ina tunanin mafita, sannan wannan Likitan shima masa a kau dashi, dan amfaninsa ya ƙare"
Musa yace "doctor Sufyan kake nufi wai?"
Bukar yace "Eh shi, na bada umarnin da ya dace akansa shima, dan haka kowa ya kwantar da hankalinsa"
Alhaji Musa yace "to shikenan, babu laifi godiya muke"
Daga nan ya kashe