Showing 96001 words to 99000 words out of 209297 words

Chapter 33 - Akidata Book 2 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

745

me kike inba shagwaɓashi ba, baccin ma sekin kaishi, ƙyalemin yarona ya gama jin ɗumina tukuna"

"Ka maida shi ciki mana ƙarewar soyayya"

Sukayi dariya gaba ɗaya.

Yusuf yace "Abbana ɗan aljanna, ina sonka da kai da Umman Yusuf, Allah yasa ku a Aljanna"

"Ameen ya Allah, ɗa ɗaya tamkar da goma"


Suka cigaba da hirarsu cikin so da ƙaunar juna, can Yusuf yayi shiru yana tunani, Bashir yace "ɗan waliyin Allah, me kake tunani ne? Kowani abun akayi maka da kuka fita, gayamin ko waye inci ƙaniyarsa"

"Abba meyasa ka ɗakkoni daga gidan marayu? .......





LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏


(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV

https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
11/15/21, 4:53 PM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"







100_101







Tsit sukayi gaba ɗaya suka shiga kallon kallo ita da Bashir, Bashir yace

  "Yusuf, waye yace maka a gidan marayu kake? Wani mara hankalin me ya faɗi haka?"

Yusuf yace "Yaya Asma'au naji tana faɗa, Mamansu Amira, kuma rannan dana tambaya ance mana a makaranta wanda suke gidan marayu basu da iyaye, tsintarsu akayi an jefar dasu"

Bashir a fusace yace  "ƙarya take yi kaji ko, ba wani gidan marayu da aka ɗakkoka, ƙarya take nina haifeka"

Jidda tace  "Abba ya zakace masa ƙarya take, babba ce fa ba haka yakamata ka faɗa ba, tunda yarone bekamata kace masa babba kamar wannan tana ƙaryaba, ka gaya masa wani abun dai"

Bashir yace  "idan bance ƙarya take ba me zance? Ko so kike a sawa ɗana wani tunani na daban a zuciyarsa, nina haifi ɗana duk wadda ta kuma gayamaka haka kace Nine nan babanka, in ba haka su gayamaka gidan marayun dana ɗakko ka, kuma duk wanda ya kuma gayamaka haka kazo ka sameni ka gayamin, kaga yadda zan da mutum"

Ran Bashir ya ɓaci sosai ya dinga faɗa yana mita, dan ba ƙaramin jin haushi yayi ba, abun yana damunsa yadda ake aibata masa yaro, yaron da yake jin sonsa a cikin jikinsa


Bashir yace  "Ke yanzu a gabanki ake gayawa ɗana haka, amma ba kice komai ba, kuma ni baki gayamin ba balle in ɗau mataki, ɗana me haƙuri da hazaƙa amma a fara cusa masa tunani da ƙuruciyarsa, bazan lamunta ba Wallahi tabbas duk wanda ya kuma wannan gangancin zanyi maganinsa"

Ya tashi Fuuu ya ɗau Yusuf, ya kai shi ɗakinsa ya kwantar da shi, ya zauna yaita masa addu'a yana shafa kansa me ɗauke da tarin suma me kyau, har bacci ya kwashi Yusuf, dukda zuciyarsa na cike da zullumi da tunani iri a kan maganganun da mutane ke gayamasa.

Haka Rayuwa ta cigaba da gudana, Yusuf yana cikin gata da jin daɗi dai dai ɗan talaka me rufin Asiri, Yusuf akwai tsanani biyayya da haƙuri, gashi tun yana yaro yana da ilimi sosai, gashi mahaddacin Al'qur'ani ne.

Bashir ɗan Sanda ne nagari, mutane sukance masa cinnaka ba ka san na gida ba, ko suce masa murmushin talaka, saboda gaskiya da riƙon Amanarsa, komarli kuɗinka da Arzikinka baze saurara maka ba idan baka da gaskiya, sannan umarni in dai na san zuciya ne, ba daga sama ba koda gurin uban waye baze karɓi umarnin san zuciya ba, aikinsa kawai yake bilhaƙƙi, ba son zuciya da cin Amanar ƙasa,shiyasa talakawa ke masa addu'a suke ƙaunarsa.

Shekarar Yusuf tara a duniya, Babansa Bashir akayi masa kiran gaggawa yayi tafiya Lagos a hanya 'yan fashi suka kashe shi, shi da uban gidansa.

Umman Yusuf da Yusuf sunji mutuwar nan, sun kaɗu dajin mutuwar nan, sunyi kuka, sunyi kuka dan sunsan sunyi rashin babban bangon jingina, Bashir mutum ne nagari, dukda ɗan takun saƙar dake tsakaninsa da maƙotansa akan Yusuf, amma sunji mutuwarsa, mutum ne me barkwanci da raha, ga kyauta da girmama mutane, mafi akasari in kaga anyi faɗa dashi to haƙƙin wani za'a take, shi be fiye daɗa akan kansa dan an masa wani abuba, sedai in an taɓa Yusuf ko Jidda, ko an danne haƙƙin wani, dan haka da talakawa masoyansa, da iyalansa da jama'ar unguwa sunji mutuwarsa sosai, hatta su kansu rundunar tsaron sun san sunyi rashin ma'aikaci.

Bayan an gama zaman makoki maƙota suka farayi da Jidda, wai saga yadda zata yi, ta miƙe ƙafa komai sedai miji yayi mata, hatta slifas na tsakar gida Bashir be yadda ta siya ba shiyake siyan komai, yanzu tunda ya mutu a ga yadda zata yi, gata ga yaron da ba'a san wace tayi cikin shege ta yar ba, sukaje suka ɗakko, yanzu ai taje ta maida ɗan da suka ɗakko ai.

Jidda bata da matemaki se Allah, rayuwa ta fara musu zafi, saboda bata da hanyar samun kuɗi, ta fara tunanin sana'ar da zata yi danta samu suci Abinci, kar ɗanta yasha wahalar rayuwa.

Manyan 'yan sanda suka shiga yi mata romon baka, akan cewar zasu shiga su fita a samu haƙƙinsa ya fita, duk da jajircewar Bashir da wahalar da yayiwa Ƙasa, babu wanda ya kuma bi ta kan iyalansa, haka Umman Yusuf ta shiga faɗi tashin yadda zata yi domin ganin basu tagayyara ba, amma abun mamakin, komai ta kasa na siyarwa se maƙotanta suƙi siya, ko kuma su karɓe bashi su barta, sunaji suna gani haka ta cire Yusuf daga makarantar kuɗi ta maida shi ta gwamnati, dama ya gama primary secondary ze shiga, wasu lokutan har Abinci ma se tayi fama sannan suke iyaci, mutanen da Bashir ya dinga tallafawa babu wanda ya kuma bi takansu, dama ba'a batun danginsa tunda ba ƙaunarsu suke ba, haka Umman Yusuf ta samu Nanny a wata makaranta da ƙyar, ta kaɗa ta raya su ɗauketa aiki, tana da diploma amma suka ƙi, waisu masu degree suke ɗauka, sedai su bata Nanny, haka ta karɓi aikin Nanny take yi, tana zama ta zubda hawaye idan ta tuna Bashir, wata wahalar duk bata santa ba se daga baya, dama 'yan uwanta duk kusan matane, kuma uba ɗaya suke ba uwa ɗaya ba, kuma mahaifim nasu ya rasu, gashi dama suma duk fama suke da kansu, talakawa suke Aure, dama ita suke raɓa su samu wani abun, shima suna yi suna mata hassadar tana auren me rufin Asiri, tunda aka gama zaman makoki babu wanda ya sake ya waiwayarta.

A hakan ana wannan faman, amma Umman Yusuf bata yadda Yusuf ya fita da mummunar kama ba, ko yayi mummunar cima ba, ta yadda ta zauna da yunwa, Yusuf yaci.

Ga aikin Nanny ɗin nan babu wata riba, se zunzurutun wahala, ga wulaƙanci daga malamai, yaran da iyayen su dukda wannan ƙoƙarin da take yi ba'a gani.

Yusuf idan yaga tayi shiru se yace "Ummana kiyi haƙuri kinji, nima bana son wannan aikin da kikeyi, nima zan duba sana'ar da zan iya in dinga temaka miki, ki bar wannan aikin"

Umman Yusuf tace  "A'a ban yadda ba, yarone kai ƙarami kamata yayi ka maida hankali akan karatunka, idan kasan daɗin kuɗi bazaka maida hankali ba"

Fafur ta hana shi neman kuɗi, idan bashi da littafi yana son ya siya baze tambayeta ba, sedai ɗan ashirin ɗin motar da take bashi, da kuɗin break ɗinsa haka ze tafiyar ƙafa, dan ya rage ya siya, karya tambayeta yasan bata dashi, dubu goman da'ake bata na aikin bata zuwa ko ina.

Watarana Ummansa ta tashi babu lafiya, kusan sati biyu ba taje makaranta ba, gashi babu kuɗin magani, ko zuwa Asibiti tana ta fama da Asma, dan haka bata sani ba Yusuf yaje gidan Yayan Bashir, Ɗanlami yaje ya gaya masa amma yayi masa kaca kaca ya kore shi, yace baze taimaka musu ba, bayan zagi da cin mutunci da yayiwa Yusuf da gorin aishi ba ɗan ɗanuwansu bane, tun daga nan Yusuf ya ƙuduri aniyar kome ze samesu, baze ƙara neman taimako a gurin wani ba.

Haka Yusuf ya samu guri a hanya ya zauna yayi kuka, yayi kuka yai me isarsa sannan ya koma gida haka ya zuba ido, Jidda tasha jiki ta rame tayi wani iri, tana ɗanji sauƙi ta koma makaranta suka bata dubu huɗu, suka ce sun koreta, dukda sun san bata da lafiya, haka suka koma gida suka tsuguna, Umman Yusuf ta rasa inda zata saka ranta, ga larura ga babu ta musu katutu, kuɗin da aka bata dubu huɗun nan baze sai musu ishashsen Abinci ba, balle ta sai magani, maƙota babu me taimakonta dako ƙwayar hatsi, sedai in ta fito aita mata habaici ana yada mata magana.

Abunda bata taɓayi ba, ta shiga ɗibar zannunwanta tana siyarwa, dan a lokacin Yusuf kansa bashi da lafiya, dauriya kawai yake yi, tun yana daurewa harta koma ta kwanta babu lafiya, shima ya kwanta ba lafiya, dan komai se tayi masa saboda zafin ciwo.

Haka ta kwashi flasanta da Bashir ne mafi akasari yake sauya mata, ta kai kasuwa akayi musu sayen wulaƙanci, ta karɓo kuɗin ta ɗau Yusuf zuwa Asibiti, suna zuwa aka basu gado, Ulcer ta masa mummunan kamu, ga typhoid da malaria, ita bata ta kanta ta lafiyar Yusuf take, Bill ɗinsu kusan dubu goma sha huɗu dukda Asibitin gwamnati ne, haka ta zare ta biya, taje pharmacy ta karɓo magani zata koma ward, 'yan sanda suka kawo wasu sunyi accident.

Wani ya kalleta yace  "wannan kamar matar Bashir"

Ta kalle shi tace  "eh nice"

Yace  "Ai na sanki, ai tare mukayi aiki da Bashir, baki ganeni ba? Isyaku ne fa, amma yana ganki haka, baki da lafiya ne?"

Tace  "A' a Ɗanmu ne ba lafiya, na kawo shi nan aka bamu gado, an kaantar dashi"

Mutumin yace  "A'a, naga da kamar private Hospital kuke zuwa? Ya zaki kawo yaranku nan gurin? Ke kanki kamar baki da lafiya fa"

Haɗe rai tayi, dan mutumin nan ya fara isarta tace  "lafiyata ƙalau ni"

Yace "yi haƙuri, naga kamar kin fara hasala, amma ai naga kuɗinsa ya fito wata biyu baya, amma ya zan ganku haka, kuma kuɗin nasa dayawa"

Ta kalle shi da sauri tace   "Yaushe kuɗin nasa suka fito?"

"Kina nufin baki sani ba? To 'yan uwansa da wasu' yan sanda sun haɗa kai sun karɓi kuɗinsu, ai na zata an baku naku?"

Da gudu ta wuce ɗakin da Yusuf yake kwance, tana kuka yanzu kuɗin mijinta sun fito amma sun karɓa sun cinye, tasan babu yadda za'ayi ko ficika su bata, ga tarin wahala da suke ciki, amma ba imani suka hanata kowani kasone a ciki, haka taje ta zaunatayi kuka kamar ba gobe.


Kwanansu takwas a Asibiti aka sallami Yusuf suka koma gida, ta ƙarasa jinyarsa a gida ya koma makaranta, tayi tayi makarantar nan da take Nanny su maida ta bakin aikinta amma suka ƙi, haka ta haƙura duk yadda ta kai ga danne zuciyarta, seda tayiwa dangin mijinta Allah ya isa, akan haƙƙin mijinta da suka danne suka cinye sukaɗai.


A ɓoye wani maƙocin su yaga yadda taketa wahala, yai mata hanya gurin wani ɗan siyasa a temaka mata, amma mutumin nan ya nuna mata halin bunsurai, dan haka bata kuma zuwa ba, itace wankau, itace aikatau na biki kona taro, Yusuf yana Sss1 aka tafi da shi Quiz Abuja na akan harkar lissafi, aikuwa Yusuf yazo na ɗaya aka  bashi kyautar dubu ɗari biyar, malamansu suma suka cicciri nasu dana babu gaira ba dalili, ƙarshe dubu ɗari biyu aka bashi.

Umma tayi murna da samun kuɗin nan, Yusuf yace  "Umma duk an kwashe fiye da rabin kuɗin, kinga da mun samu da yawa, dubu ɗari biyar fa aka bani"

Umma tace  "Yusuf ina lefi, da ina muka samu wannan ɗinma? Ai Alhamdilillah mai dai Allah yayi maka albarka, ya ƙara hasken makaranta ya jiƙan Abbanka'

Yusuf yace  " Ameen Umma, ga kuɗin nan, wace sana'a kike ganin zamu fara ne? "

Umma tace " Yusuf ka maida hankali a karatunka, sannan kuɗin nan ka ɗau abunda zaka ɗauka, semu yi tunanin abunyi"

"haba Umma, na girma fa ki bari in fara sana'a mana, kuma ni ba abunda zan ɗauka a kuɗin nan, muyi tunanin abunyi"

"A'a Yusuf, dole ka sai sutura, zan shiga kasuwa in samo maka yaduka, da takalama, dako ɗan agogone, ka fara zama saurayi, ina kallo kayanka duk sun mutu, ba yadda zanyi ne kawai"

Yusuf yace "Umma karkice zaki kashemin kuɗi dayawa, ina sa ran zamu kuma zuwa wani competition ɗin, kema ki sai wani abu a ciki, nace ko injin markaɗe zamu siya, se a ajiye shi a ƙofar gida idan na dawo in dinga zama"

Aikuwa Umma ta yadda da shawarar Yusuf, suka ajiye kuɗi basu taɓa ba tukuna, suna shirin siyan injin markaɗe.

Yusuf ya dawo daga makaranta sukaje kasuwa suja siyo inji, akazo aka saita komai suka sai kayan Abinci da sauran buƙatu.

Da safe idan Yusuf ya tafi makaranta, Ummace take markaɗen a cikin gida, idan ya dawo ya fito dashi waje yayi zuwa magariba, se maƙota suka fara surtu wai ana cika musu kunne, bayan a ƙarshen kayanma akwai babbn gurin niƙa, da suke wuni guda niƙa, amma suka zo sukace wai suna takura musu da ƙarar inji.

Duk shiru na Yusuf ya dinga faɗa, yace "wallahi babu wanda ya isa ya hanamu sana'a, me kuke so muyi ƙasa zamu ci kome, yanzu da wani fitinannen na zama sekunfi kowa tsinemin, ba irin wahalar da bamu shaba, kuma mun kafa sana'a kuce semun ɗauke baze yuwuwa ba"

Maƙwabcinsu Na jikin gidansu yace  "kai dalla har kana da bakin magana, banza tsintacce wanda ba'asan asalinsa ba, karuwa tayi ciki ta haife ta yar, an tsintoka an rufa maka Asiri, amma kazo kanawa mutane Iskanci a gari"

Maganar nan tayiwa Yusuf ciwo, yaji haushin maganar nan, yaji kamar ya soka masa mashi a zuciyarsa, amma ya dake yace  "idanma hakan akayi, inma ba hakan bane, ba a kaina aka fara ba, kuma ba kaina za'a ƙare ba"

Umma dake cikin gida, tazo ta janye hannun Yusuf tana kuka suka koma cikin gida  tace   "Yusuf mi haƙura da markaɗen nan kawai, bazan iya jure ana cimim zarafinka ba, bazan iya ba"

Ya goge mata hawaye yace  "Umma idan mun dena Meza muci, kidena damuwa ni baya damuna, saboda nasan bani da wasu iyaye inba Ummana ba, da Abbana Allah ya jiƙansa, ki rabu dasu kawai, komai lokacine wataran in ance suyi min ba zasuyi ba"

Haka yaita rarrashinta yana bata haƙuri, washegari ya tafi makaranta, bayan ya dawo tun daga soro ya fara jiyo kukan ummansa tana   "da ikon Allah se Allah yasakamin abunda kukayi min, yadda kukayi nufin tozartani Allah yasakamin, wallahi ɗanlami da kai da Ballo da 'yan uwanka bazan yafe muku zaluncin da kukamin ba, wallahi Allah ya isa"

Yusuf ya shigavda sauri, yaje ya sameta a dirƙushe tana kuka, ga su Yaya ɗanlami da wasu mutane.

Yusuf yace "Umman Yusuf, lafiya kuwa me suke mana a gida? Me kuma mukayi musu?"

Yaya Bello yace  "kai dalla tafi can banza, meye naka a ciki wani wai me muke muku a gida, inane gidan naku meye haɗakinka da Bashir,? Ɗan tsintuwane fa kawai amma ko taku baka dashi a abunda ya bari, seka bazama neman karuwar da ta haifeka ta yasarka ta nuna maka ubanka"

Cikin kuka Umma tace "Wallahi karka ƙara shegantamin ɗa, Yusuf ba karuwa ce ta haife shi ba, ɗana ne, kuma ɗan sunnane duk Wanda ya kuma shegantashi ban yafe ba"

Yusuf bece komai ba, yaje ya durƙusa ya ɗago Umman dake kuka yace  "Umma meyafaru ne wai?"

"Yusuf kaga, bayan sunje sun karɓe haƙƙin Babanka sun cinye, babu wanda ya waiwaye mu, sun saida gidan da muke ciki, an bamu notice, wai bazasu bamu gadon komai na Bashir ba, Yusuf an mana adalci kenan? Yanzu sun kyauta kenan? Yusuf ynzu kana ganin da Bashir ne a raye ze musu haka? "

Yusuf ya rumgumeta ganin yadda jikinta har rawa yake tana kuka, gata ba cikakkiyar lafiya ba yace "Ummana kiyi haƙuri, ai Allah baya bacci ni idan bani da gadonsa aike matarsa ce yakamata su baki"

"Yusuf gidan nanfa nawane nida kai, har rubutu Bashir yayi ya bari kafin ya rasu, kuma Bello ya sani amma shine suka saida gidan, idan na tashi daga nan mu koma ina? Me nake dashi idan na bar nan?"

Ɗanlami yace "koma gidan ubanwa zaki ki tafi, ai dama ba gidan ubanki baane, seki koma gidan ƙasar da ubanki ya mutu ya bari, shi kuma ya koma gidan ajiye shegu da kuka ɗakko shi"


"Wallahi se nayi shari'a daku, se an ƙwatar mana haƙƙinmu"


"Haba Umman Yusuf, aishi Allah baya bacci, kuma Allah na kowane baya barin zalunci, menene gida idan sunyi haka dansu wulaƙantamu Allah baze basu dama ba, ki kwantar da hankalinki mun rasa Abba ma, kuma dangana mukayi mukai haƙuri, dan haka gida ɗazune, in da rai da lafiya insha Allah sena gina miki gida na ban mamaki, gidan a wanke hannu kafin a taɓa "

Yai maganar yana goge mata hawayen fuskarta, yana murmushi dukda Shima fuskarsa sharkaf take da hawaye.

Murmushi tayi na ƙarfin hali tace " na dena Yusuf, na barwa Allah nasam baze wulaƙantamu ba"

Saboda keta haddi da cin mutunci, tana zaune wai za'a wuce da masu siuen gida har ɗakin baccinta a duba, Yusuf ya miƙe ya tare ƙofar yace "dul abunda zakumin zan iya jurewa, amma wallahi duk garin nan babu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login