Showing 120001 words to 123000 words out of 209297 words

Chapter 41 - Akidata Book 2 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

1091

garkuwa dani ba sam, anyi garkuwa damune ni da shi, ba wahalar da beyi ba saboda in tsira da rayuwata, meyasa yanzu za'ace shine ya saceni? Anyi masa adalci kenan kasa a sake shi please, dan Allah a saki Yoseef bashi da laifin komai fa" ta ƙarasa maganar tana kuka.

Bulama yace "Ni yanzu ta yaya zan fara sakawa a sake shi? 'yan sanda sun fitar da rahoto akan abunda ya faru kawai ace nasa a sake shi, bafa a ko ina ake alfarma ba, yanzu gaba ɗaya case na hannun hukuma, babu abunda zan iya ni"

"Shikenan tunda babu abunda zaka iya, ni zanyi ko zan ƙarar da dukiyar Daula sena fitar da Yoseef, saboda ni ba butulu bace ba, Yoseef yayi min halacci"

Ta miƙe ta kwanta a gurin, tana ta kera gwaron numfashi, wani na bin wani.


Suleiman gidan su Yusuf ya tafi, yana zuwa ya tarar da Umman Yusuf a kwance, an kewaye ta ana yayyafa mata ruwa, sam bata san inda kanta yake ba, ga Asmarta ta tashi tana jan numfashi da ƙyar, an sheƙa mata inhaler amma a banza.

Suleiman yace "Subhanallah, ya ba'a kaita Asibiti ba? Meye ya faru da ita haka?"

Wata maƙociyarsu tace  "wallahi yau da Asuba bayan ta idar da sallar Asuba, ya kunna radio taji ance an kama ɗanta Yusuf, shikenan muka jiyo kukanta, muna shigowa harta fara fita daga hayyacinta, numfashi yaƙi tsayawa a ƙirjinta.

Suleiman yace" da ba seku kaita Asibiti ba, koda kuwa na gwamnati ne ba, zata iya rasa ranta fa a haka, maza ku ɗakkota ga mota can, a sata a ciki mu tafi Asibiti "

Haka kuwa akayi, aka sa Umman Yusuf a mota, da wasu maƙotanta suka Tafi Kaita Asibiti.

Suna zuwa aka karɓeta a emergency, aka shiga da ita, likitoci sukayi gwaje gwajen da zasuyi suka ga jininta ya hau fiye da kima, dama tana zuwa shan magani ana duba jinin, tun lokacin da Yusuf ya ɓata ta haɗu da hawan jini.

Yanzu jinin ya hau fiye da kima, ga Asma ta tashi saboda kukan da take yi, gaba ɗaya bata a hayyacinta, a nata ƙoƙarin ganin jinin ya sauka amma abu ya gagara, ƙarshe seda aka haɗa mata da oxygen, da allurai da drip, Suleiman duk ya biya charges ɗin.

Da Safe Amal bata tashi ba se wajen sha ɗaya na safe, ta tashi daga bacci ta tashi da wata irin yunwa, ta tashi ta shiga toilet tayi wanka, ta canza kayan jikinta daga na bacci, har zata fita tace "bari dai in kunna wayata, inga me wannan jakin kuma ya kuma turowa" ta zauna ta kunna wayarta, ta buɗe data messages nata shigowa, amma babu na Alhaji Haruna, ta taɓe baki ta tashi zata fita, sega kiran wayarsa ya shigo wayarta.

Ta koma ta zauna sannan ta ɗaga, Alhaji Haruna yace
"yaushe zanzo in karɓi takaddar nan ne?"

"ba rana ba wata, muddin ba zaka cika sharuɗan dana sama ka ba"

"Waike ynzu 500k ne suka miki kaɗan? Haba ke kuwa dan Allah"

Amal tace  "kaga sauraramin, meye wani 500k,duk kuɗin da kake sata na haram kakeci, seni zaka rainawa hankali, wallahi bazan baka takaddar nan a 500k ba"

Aikuwa ya fusata yace  "ke wai wace irin yarinya ce, kwana bakwai fa kawai aka bani in kai takaddar nan, ya zakice bazaki bank ba haka akeyi?"

"Kai bari kaji in gaya maka wani abu, wallahi idan baka yi wasa ba sena sa takaddar nan ta zama hujja akanku gaba ɗaya"

"har babar taki?"

"Eh har ita, duk zaka ja muku ne, bari in maka magana ta ƙarshe, wallahi bazan baka takaddar nan ba har se ka bani kuɗin da zaka fanshi budurcina da ka karɓa ta ƙarfi"

"Ke, ni kike gayawa haka? Wace irin magana ce wannan?"

"ai kace min ka ga kaidi iri iri na mata a bariki, to zan nuna maka nawa na dabanne, zan kawo ƙarshen bunsurancinka, wallahi ko inje in haɗa maka masifa da tashin hankali a gurin Alhaji Bukar ɗin, baka san kalar nawa kaidin ba zan gwada maka Akuya kawai"

Ai kasa magana yayi, se bin wayar yayi da kallo, lallai yarinyar nan bata da mutunci sam.

Ta ajiye wayar tace za kaga tsiya ganin idonka, tai tsaki ta saka wayar a caji ta fito falo, Dariyar Mummy taji da Ramlah, Ramlah tace  "dara taci gida, sunzo hannu Alhamdilillah, naji ance a ƙungurmin ƙauye aka gano su, koya akayi ta iya zaman wannan ƙauyen oho"

Mummy tace "su suka sani, ni dai tunda an kamo su na fara jin ƙamshin samun kuɗin nan"

Ramlah tace "Ance yana can hannun 'yan sanda ido ya raina fata, tun jiya ya fara cin ƙaniyarsa a hannunsu, ai gara yaji jiki, kafin a shiga kotu ya raina kansa"

Mummy tace "eh Bulama ya cemin idan aka gama bincike kotu za' a kaishi, dan haka ni yanzu ba ta tashi nake ba, ta Anwar nakeyi har yanzu shiru, tunda Amal ta kai musu takaddar basu sake cemin komai ba"

Ramlah tace "zasuyi miki magana ne, bari mu kunna TV mu sake ganin idon munafukin nan, dan ban manta lokacin da ake wulaƙantamu ana cin zarafin mu saboda shi ba"

Ajiyar zuciya Amal tayi, wanda yasa suka juya gaba ɗaya suka kalleta, wucewa tayi kitchen dan Samarwa kanta abunda zata ci.

Mummy tace  "Auta ya jiki?"

Ta kalli Mummy ta ɗauke kai, ta wuce kitchen, ta fito daga kitchen tazo ta zauna tace "Mummy, hira naji kuna yi kamar an kama Yusuf ko?"

Ramlah tai farat tace  "Eh an kama shi, seme ne kuma? Ko zaki fara wa mutane shirmen naki ne?"

Amal ta girgiza kai tace  "No akanme? Ina Ita Widad ɗin take?"

"Tana gidan Bulama, dan shi ze iya wannan haukan nata"

Amal ta jinjina kai, ta tashi ta tafi ɗakimta, tana jinjina kai, da sauri ta ɗauki wayarta ta shiga social media, aikuwa taga yadda labarin ya cika social media, yadda aka haɗa ƙarya da gaskiya.

Ta ajiye wayar tayi shiru tana tunani, kasa shan tea ɗin nan tayi, se tunani daya dabai baye zuciyarta, gaba ɗaya tausayin Yusuf ya mamaye zuciyarta, tama jin tsohuwar soyayyar sa na taso mata.

"Nurat" Alhaji Musa ya kira sunanta, ta amsa masa da "Na'am Daddy"

"ya maganar shirye shiryen tafiyarki ne, you should preparing for it fa, lokaci yana gabatowa"

"but Daddy, i thought we have discussed this issue since"

Ya kalleta yace "muka ce mene?"

"Daddy na gaya maka ni bana son tafiyar nan, ni ba inda zanje a gida Nigeria zanyi karatun"

"ba zakiyi a nan ɗin ba, ƙasar nan zaki bari, waike yaushe muka fara sainsa dake ne? Ni zance ga yadda za'ayi amma ki bijiremin? To baki isa ba nina haifeki bake kika haifeni ba"

Ya dinga banbamin bala'insa, yayi ya gama tsaf bata sake cewa komai ba, seda ya gama tukuna sannan ta miƙe ta bar masa ɗakinsa, tana zuwa ɗakinta tace 'wallahi ba inda zanje, bazan bar ƙasar nan ana wannan halin ba, se naga abunda ya turewa buzu naɗi"

Yusuf kam ya daku a gurin jami' an tsaro, akan lallai seya amsa shine ya sace Widad, amma Yusuf ƙemem yaƙi magana, dama shi Saleh ba'a maganarsa saboda ya galabaita fiye da Yusuf ko magana baya iyayi, bama shi da lafiya.
Juyin duniya Yusuf ya amsa shine ya sace Widad yaƙi, yaƙi ko ɗaga kansa ma balle yayi magana.

Mutumin da yake jibgarsa yace "ga 'yan jarida cam suka cika harabar gidan nan, zamu basu lokaci suyi magana da kai, ka furta kaine ka sace yarinyar nan koka samj sassauci, idan kuma kaƙi to haka zamu ci gaba da casaka a gurin nan, gara ka nemawa kanka mafita, ka amsa kai ka sace ta"

Yusuf dai beyi magana ba, aka taso ƙeyarsa a gaba aka saka masa handcuffs hannu da ƙafa, aka fito da shi harabar headquarter na 'yan sanda, fuskarsa duk ta kumbur saboda duka.

' yan jarida sun cika gurin nan, suka kewaye Yusuf da abun magana, kowa yana yanko masa tambaya, wasu ta gaske wasu ta cin mutunci, amma Yusuf yai shiru, sukayi sukayi har suka gaji, har ya juya za'a maida shi ya tsaya ya waigo, ya kalli' yan jaridar nan yace "Bani na sace ta ba"

Kawai ya juya, ds ƙyar 'yan sanda suka dakatar da' yan jaridar nan aka mayar da Yusuf inda aka ɗakko shi.


Nurat gaba ɗaya ta tayarwa da Khalil hankali akan maganar Yusuf, ga koke koken da take akan batun komawarta karatu, tana ta saƙawa da warwar akan ta gudu ta bar gidan gaba ɗaya, amma sedai tasan idan tayi hakan ba zata sake daraja a idon mutane ba.



Alhaji Haruna duk ya shiga damuwa da tashin hankali, akan takaddar nan da Amal keta rainamasa hankali akan ta, ya shiga part ɗin Amaryarsa ya tarar da ita ta ƙurawa TV ido cike da damuwa, ya zauna kusa da ita yace "Baby kallo ake ne?"

Ta ɗan ɓata fuska tace "ina kallon wani abune daya tsayamin a zuciya, wannan bawan Allah da aka kama akan 'yar gidan Daula ya tsayemin, i can't imagine ze aikata wani abu makamancin haka, ƙarya ce kawai akayi masa"

Yace "ke ya akayi kika san ƙarya akayi masa? Wannan shine abunda ya dace dashi, kuma zamu tsaya kai da fata se an hukunta shi anyi maganin irinsa a cikin al'umma"

Ta kalle shi tace "Nasan Yusuf, fiye da yadda kake tunani, inaga mahaufiyarsa ce kawai zata fini sanin waye shi, wallahi wannan maganar ƙarya ake masa, mutumin da yake kamar waliyyi dan haƙuri, wannan maganar ƙaryane wallahi"

Alhaji Haruna yace "Salma meye haɗinki dashi da kike wannan zaƙewar, meye haka kike yi akansa, kuma a gabana?"

Ta Harare shi tace "Yusuf unguwar mu ɗaya, kuma tsohon saurayi nane, wanda aka hanani Aurensa aka ƙaƙabamin kai"

Kawai ya kwashe da dariya yace "lallai baki da hankali, aikuwa kina ji kina gani ze tafi prison Salmata, sedai haƙuri"

Ya tashi ya barta a gurin, tausayin Yusuf ya kamata, tasan Yusuf baze taɓa aikata abunda akace yayi ba.



Widad tana zaune kamad wata mahaukaciya, tun jiya da safe rabonta da Abinci, tana jin yadda zuciyarta take bugawa ba daidai ba, tai shiru tunani da tausayin Yusuf ne yake ta ratsa zuciyarta.

Iman ta shigowa da Widad da Abinci tace "ga Abinci, ki daure kici dan Allah"

Widad tace "kiramin Bulama, zamuyi magana"

Iman tace to, befi mintuna biyar da fitarta ba sega Bulama ya shigo ɗakin, yana shigowa ya kalleta yace "innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Widad har yanzu bakya cin Abincin, subhanallah ko mota za'a ɗakko mu tafi Asibiti ne?"

Tace "wani hali Mijina yake ciki?"

Bulama yace "waye mijinki kuma?"

"Yoseef" ta bashi amsa

"yaushe kikayi Aure bamu sani ba?"

Cikin tsawa tace "ka dena amsamin tambayata da tambaya, ina Yoseef yake?"

Bulama yace "yana hannun hukuma har yanzun"

Ta miƙe tsaye tace "har yanzu baka yi komai a kai ba ko? Ni ka maidani gidan mu gurin Daddy na, shiyasan ranar da Yusuf yayi masa, baze bari ya cutu ba akan laifin da beyi ba"


Bulama yace "kinga ki kwantar da hankalinki".


"Karka ƙara cewa in kwantar da hankalina, ina Alhaji Nasir Daula yake? Ina babana Daddyna nake maka magana, yana ina? Ta yaya za'ace tun jiya har yanzu babu shi babu dalilinsa bezo inda nake ba"?
Tai maganar a jere bako haɗiyar yawu, tare da ɗaga murya sosai.

Bulama yace "kinga zauna kici Abinci tukuna"

Ai be rufe baki ba tasa ƙafa tai ball da kayan breakfast ɗin, ta riƙe gaban rigar Bulama tace "ka gayamin gaskiya, ina Daula yake? Idan an kashemin shine ka gayamin, yana ina? Ina yake ina Daddyna?!"

Jin Hayaniya yasa tuni mutan gidan suka fara taruwa a ɗakin, Hajiya Sarah tace "babanki Nasir Daula, tun bayan ɓatanki ya kwanta rashin lafiya, aka bishi har gadon Asibiti aka sace shi, har yau babu wanda yasan inda yake"

A hankali Widad ta saki rigar Bulama, tana kallon Hajiya Sarah "Annn. An sace Daddyn Widad a gadon Asibiti, this serious, Daddyn how comes? Ta yaya za'a sace shi ba wanda ya sani, shikenan na rasa Yoseef ɗina, Daddyna ma ace ba'a ganshi ba, Noooooo! This impossible!!!

Tana maganar ta silale ta faɗi ta ruf da ciki, ko numfashi ba tayi.




Ayi haƙuri ba editing

Ayi subscribing YouTube channel ɗina dan Allah, me suna Cool Arewa TV
11/21/21, 7:45 AM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680


(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"

110_111

Me Adda ya kawowa mutumin kujera ya zauna, ya kalli Saleh yace "ka dena mamaki mana, ai bekamata kayi mamaki ba, a zatonka kai kaɗaine me wayo, ko kuma kafi kowa wayo? Kifi na ganinka me jar koma, kallonka kawai nakeyi"

Saleh yace  "hmm Bukar kenan, kaima kuka karya Alƙawari balle ni, haka mukayi daku? Ashe kun kashe min ɗan uwana, banma sani ba balle kua bamu gawar muyi masa sitira, dama haka akeyi, kunyi amfani dani ne dan cinma burinku?"

"ƙwarai kuwa, muna amfani da kaine dan cinma burinmu, kai bari in gayamaka wani abu, ku duka wanda nake aikin harƙallar nam daku, ina amfani da kune dan cinma burina nikaɗai, na ɗaukeku karnukan farauta tane kawai "

" Amma wallahi Bukar baka da imani, baka da adalci "

Me Adda ya yunƙura ze kaiwa Saleh duka amma Bukar ya hana shi yace "ƙyaleshi, ai baaka ga komai a cikin ƙudrina da AƘIDATA ba, kuma dama tuntuni kowannen ku nayi masa tanadin makomarsa idan deal ɗinmu ya kammala, sedai kai kayi gaggawa gurin riskar taka makomar, tunda ka yaudareni kaci amanata zaka riski makomarka a nan kusa, ina Widad take? "

Saleh yai masa wani irin mugun kallo yace "ni ka bawa ajiyarsu kokuwa? Kaje ka tambayi wanda aka sa su sacesu gasu nan a gabanka"

'bana son in wahalar da kai kafin ka mutu Saleh, ko dan irin wahalar da kayimin, amma gaddama da taurin kai zesa in maka uƙuba wadda zata yi ajalinka, Saleh kaine ka bawa Widad da direbanta mafaka, kasan inda suke kaine ka kuɓutar dasu, dan haka karka wahalar dani, ko ka wahalar da kanka kafin ka mutu, ka gayamin ina ka kaisu"?

"Ni bani na ɗauke su ba, ban san inda suke ba, dan haka karka ƙara tambaya ta na gaya maka"

Bukar yace  "Shikenan, tunda baka san rarrashi ba, bari a biyo maka ta inda ya dace, Me Addda ku gasamim shi tsawon kwana uku, muga iya juriyarsa a mtsayinsa na kurtun soja"

Daga nan Bukar ya tashi ya fita daga ɗakin suka rufa masa baya.

Amal tana ta sauri taje ta kai takaddun nan, daga nan ta kai wadda aka bata ta kaiwa Alhaji Haruna, yamma ta fara yi sosai kuma bata son Mummy ta kama faɗan nata akan bataje aiken da tayi mata da wuri ba, dan haka a harabar gidan gurin shiga mota ta ƙarasa saka takaddun a jakarta, da wasiƙar gurin Anwar, da takaddar form ɗinta, ta buɗe mota ta shiga ta fice.

Unguwar da guest House ɗin Alhaji Haruna take shiru babu mutane a unguwar, duk se kangwaye da sababbin gidaje, bata kawo komai a ranta ba tace bari taje ta fara kai masa tasa takaddar, daga nan kuma seta je gurin nata kai takaddar.

Tana zuwa megadi ya buɗe mata gate ta shiga, tace  "yana nan kuwa?"

Megadi yace "Eh yana ciki"

Ta fito daga motar ta shiga, ta murɗa ƙofar falon tare da yin sallama, sedai babu kowa a falon, ta nemi guri tayi zamanta a falon, shiru shiru babu wanda ya fito, ta tashi ta koma gurin megadi tace  "Anya kuwa yana nan? Naje nayi sallama amma shiru ba'a amsa ba"

Megadi yace "ai be fiye zama a falon ba, ki shiga yana ciki"

Tace "Cikin ina? Kaga ungo bari in baka takaddar ka ajiye masa"

Megadin yace "rufani ki saya, ai be yadda in karɓi kowane saƙo ba idan bashi yace ba, ki buɗe ƙofar dake cikin falon wasu falukan ne a ciki fa"

"kaga muje ka rakani da kanka, ni bazan shiga ni kaɗai ba"

Yace "shikenan muje"

Ya rakata, yana gaba tana bin bayansa, suka dinga ratsa faluka, sukaje wata ƙofa yace "yawwa a nan yake ganin baƙi, ki shiga ki bashi"

"kazo dai mi shiga tare, danni bazan iya maida kaina waje ba, wannan gida duk lunguna kamar gidan matsafa"

Yace "A'a shiga dai ki fito, ina nan ina jiranki"

Tace "to shikenan"

Ta buɗe ɗakin ta shiga da sallama ashe bedroom ne, ya amsa mata yana zaune akan gado yana danna system, yana ganinta ya faɗaɗa murmushinsa yace  "Ashe kinzo, ai tun ɗazu nake jiranki" yai maganar yana binta da kallo.

Haɗe rai tayi tace  "eh nazo, ina falo ne ga takaddar tace akawo maka"

Alhaji Haruna yace  "ok kawomin nan"

Ta ƙaraso tana zumɓura baki, ta sa hannu a jakarta ta ɗakko takaddar, ta ƙarasa inda yake ta miƙa masa takaddar, sedai me se ya haɗa da hannunta, ya riƙe.

A fusace ta kalle shi tace  "meye haka kuma? Dalla malam sakeni"

Yace "haba Baby, gaki kamar wayayyiya amma kina wani kidahumanci, ki kwantar da hankalinki karki ji komai kinji"

"Dalla ka sakeni ko in maka ihu wallahi"

Yai murmushi yace "to idan kinyi ihu kina tunanin akwai wanda ze kawo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login