Showing 48001 words to 51000 words out of 209297 words
"Ta yaya zanga abunda kika gani? Ina nan kina can"
"Mummy an buga fastocin Yusuf, wai he is wanted shine yayi garkuwa da Widad sannan yayi da mahaifinta"
Tace "wai waye Yusuf ne?"
Nurat tace "Mummy direban Widad ne fa"
Tace "Allah sarki, dama duk abun nan shine ya sacesu aketeta nemansu?"
Nurat kamar ta fashe da kuka tace "Mummy, ki gane me nake nufi mana, wannan abun duk shirin su Daddy ne, Daddy ne suke ƙulla wannan abubuwan, Yusuf bashi da laifin komai fa"
Da sauri Mahaifiyarta ta riƙota, ta rufe mata baki tana waige waige, a fusace ta kalli Nurat tace "waike yaushe zakiyi hankali ne? Kina kallo kwanan nan ya kusa halakaki, shine kike wannan maganar, maza ki bari ya jiki idan ya ƙarasaki shikenan"
Cire hannun Mahaifiyarta tayi daga bakin ta ta kalle ta tace "haba Mummy, yanzu shikenan mu zuba ido babu wani abu da zamuyi, wallahi Umma Yusuf baze sace Widad ba, ina yaga yadda ze iya sace Daula a gadon Asibiti, shikenan idan baka da kuɗi baka da gata a garin nan?"
"to dan ubanki kije kiyi tayi, ina gargaɗinkibakan shiga wannan sabgar tasa, akan ya hana ki fita kawai ya kusa aikaki lahira, amma se sake cusa kanki kike kina bin diddiginsa, ki cigaba karki fasa, inya kasheki ya kashe banza dukda shiya haifeki, kinfi kowa sanin takun saƙar dake tsakaninsa da Daula, kuma kin san alwashin da yayi, ki cigaba da sa kanki a lamuransa, inkin ƙiji ba zaki ƙi gani ba"
"Amma Mummy......"
A fusace tace "Amma me? Kije kiyi dan ubanki karki fasa, fita ki barmin ɗaki"
Jiki a sanyaye ta fito daga ɗakin, tana jin wani irin jiri yana kwasarta, tana fitowa falo taci karo da mahaifinta, yana shirin fita, suka haɗa ido ya ganta kamar wata mara gaskiya, tana tafiya a hankali, ya kalle ta yace "ke lafiya kuwa?"
Ba tace masa komai ba, se binsa da tayi da ido.
Yace "jeki ki kiramin mahaifiyar ki" ko kallon inda yake ba tayi ba, ta shige ɗakinta ta kulle ƙofa, ta faɗa kan gadonta ta fashe da kuka.
Mamaki ne ya kama Alhaji Musa, ya nufi ɗakin Maman Nurat, yaje ya tarar da ita tana gyara kan mudubinta, ya kalleta yace "to uwar masifa, hala wani abun kikayiwa yarinyar nan, na ganta a waje na mata magana taƙi kulani"
Wata uwar harara maman Nurat tayi masa tace "masifa harna kaika, daka kusa hallakata saboda tsabar masifarka da son zuciya, niba wani abun nayi mata ba, halayenka ne suke baƙanta mata zuciya"
"Halayena kamar yaya?"
Tace "Ahh gaba ɗaya ka canza mana, kana treating ɗinta kamar ba kai ka haifeta ba, dole ranta ya dinga ɓaci"
A fusace yace "ƙarya kike munafuka, kece kike zigata, idan ba haka ba ya za'ai in haifi 'ya sannan kikama kawomin ƙabali da ba' adi, babu yadda za'ayi 'yata ta dinga min wannan halin na taurin kai, in bake kike zigata ba"
Ta Harare shi tace "au har kamanta tantama kakeyi akan ko kai ka haifeta? Ai baka da tabbacin kaika haifeta ko ba kai ka haifeta ba"
"Malama karki gayamin maganar banza, Nurat' ya tace nina haifeta, kuma ina son abata"
Tsaki tayi ta miƙe tace "ƙaryar banza kawai, ji wata fuffuka kake 'yarka ce, bayan da hannunka ka kusa kasheta"
"Muka kusa kasheta dai, waye sila?"
Banza tayi masa ta shige banɗakinta, ta rufe ƙofa ta barshi a gurin a tsaye.
Juyawa yayi ya fito daga ɗakin, ya kuma kallon ƙofar Nurat, still a rufe take bata buɗe ba, girgiza kai kawai yayi ya fice abunsa.
Ita kuwa Nurat tana cikin ɗakin, se rusa uban kuka take, tana jinjina zalunci irin na Mahaifinta, sun haɗa kai sun sace 'yar Daula tare da Yusuf, kuma ya koma sunsa ace shine yayi garkuwa da mahaifinta, tuna tana iya kukan hawaye na zuba, har tayi shiru se ajiyar zuciya da take yi.
Da Yamma Widad suna zaune dasu Hindu, kowacce da littafinta tana koya musu karatu, cikin ikon Allah da yake sunsa kansu, suna fahimtar karatun sosai, duk me tambaya ta bashi damar ya tambaye ta, dukda idan tare da su Indo take koyawa Hindu karatu bata wani sakar musu fuska, amma a hakan girmamata sukeyi sosai, saboda bata hantararsu sam, bayan sun kammala karatun ne kuma ta shiga yi musu bayani akan tsafta da mahimmancinta, ta shiga ɗakinta ta ɗakko musu pad a cikin wadda Yusuf ya siyo mata, ta bawa kowa ɗaya, tayi musu bayanin yadda ake amfani da ita, da kuma yadda zasu dinga kula da kansu lokacin al'ada, kunya suka dingaji suna wani sinne kai, hakan seda ya kusa bawa Widad dariya, dan sam ba taga abun jin kunya a bayanin nata ba, suka karɓa suka dinga yi mata godiya, suna nan zaune suna bitar karatun da tayi musu, ita kuma tana ta faman saƙar mafici da Hindu ta koya mata.
Yusuf ne yayi Sallama, suka amsa gaba ɗaya suna gaishe shi, hannunsa ɗauke da ledoji, Widad ta kalle shi ta basar tana zumɓura baki, Gwaggo ta harareta, ta gane kallon da Gwaggon take mata, taje ta karɓi kayan hannun Yusuf ne, aikuwa ta tura baki tace "mhmm Mama kayanfa da nauyi, kuma ze iya kaiwa ɗakin"
Dariya ta bawa su Indo, dan yadda take haɗe rai tana koya musu karatu, bazaka ce tana dariya ba, Gwaggo tace "haba yarinyar kirki, aikin ladane fa duk abunda kika masa yaji daɗi lada zaki samu, ko ba kyason ladan ne?"
"Ina so mana"
Gwaggo tace "Yawwa 'yar Albarka, aje a karɓi kayan hannunsa"
Widad ta miƙe ta ƙarasa inda Yusuf yake yana kallonta, tana zuwa ta karɓi leda ɗaya tana harararsa, Yusuf yace "to mara kunya, ni kike harara ko?"
"Mama kinga yana cemin mara kunya ko?"
Gwaggo tace "Allah ya huci zuciyarki, tuba muke, kai kuma haka akeyi, ka samu za'a karɓi kayan naka shine za kace mata mara kunya?"
Yusuf yayi dariya suka wuce ɗaki, Hari tace "wallahi Wudas ɗin nan ba ƙaramar taɓararriya bace, gaba ɗayanta gaɓuwa ce"
Hansai tace "Allah yasa ta jiki, ta ƙare miki tatas ai"
Me gari kam yana ɗaki yana jin dramarsu, koda ya fito ya kalli Gwaggo yace "Allah ya saka miki da Alkhairi Hasana, kina ƙoƙari da wannan 'yar taki"
Sukayi dariya, ya koma kan ɗaliban Widad yana cewa "masha Allah, kuna gane karatun dai ko?"
Hindu tace "muna ganewa sosai"
Ya kalli inda Hanne take zaune, yace "ke ina naki littafin?"
Hindu tace "ai banda ita ake koyamana"
Me gari yace "saboda me banda ita? Ke meyasa ba zaki koya ba? '
" Baffa ni bana so" Hanne ta bashi amsa.
"ba kyason ƙaniyarki, kije ki samu Ila, ki gaya masa nace idan yaje kasuwa ya taho miki da kayan rubutu kema, idan na kuma zuwa na tarar ana karatu bake senaci mutuncinki"
Kallon me gari tayi, ta yaya ma zata fara zama wannan mara mutuncin, 'yar wulaƙancin ta koyar da ita? Shiru tayi masa taƙi kula shi, dan ba zata taɓa zama wannan banzar ta koya mata karatu ba.
Gaba ɗaya Anwar a rikice ya shigo babban falon gidan, ya tarar da Amal da Hajiya Halima na shirin fita, yayin da Ramlah ke zaune tana zuba Coca-Cola a kofi tana sha a hankali.
"kai lafiya kuwa na gankaba haka? Kamar wani korarre?"
"Mummy, kin saurari labarai ne yau? Ko kuma kin kalla?"
"A'a ni kasan ba wani shiri nake da radio ba, dama da Daula yana nan ne, shine sarkin labarai da radio saboda kasuwanci"
Anwar ya girgiza kai yace "Mummy, na rasa mema zance miki, yanzun nan naji a labarai, wai hukumar 'yan sanda sun fitar da sakamakon binciken ɓatan Widad"
Cikin Hajiya Halima yayi wata ƙara, ta dake tace "me sukace, ni sam banji labarai ba, am ganta ne?"
"Mummy wai ana zargin Yusuf ne yayi garkuwa da ita, ya nemi maƙudan kuɗaɗe da aka hana shi, shine yayi garkuwa da Daddy"
Wani sanyi ne ya ratsa Hajiya Halima, dan ba ƙaramin daɗi labarin yayi mata ba, amma ta nuna kaɗuwarta a fili tace "to yanzu ya ake ciki? An kama shi ne?"
"Mummy ba'a kama shi ba, amma ance duk inda aka ganshi ko a mace ko a raye a kamo shi, Amma ni sam banji na yadda da wannan labarin ba Mummy, ya za'ayi Yusuf ya iya aikata haka? Yusuf baze wannan abunba, dukda ban daɗe tare da shiba, amma beyi siffar miyagu ba, ni ban yadda da wannan labarin ba"
"to kar Allah yasa ka yadda mana, ubankane shi, ai a rayuwar nan kai dai kaga mutum kawai, yana ta shisshigi a gurin me gidan nan da Widad, ashe macuci ne Azzalumi, ai ba'a gane mugu a fuska tunda kaji an faɗi haka to tabbas ya aikata ne"
Anwar ya girgiza kai yace "gaskiya bazan taɓa yadda ba Mummy, dan yadda akayi aka sace Alhaji Nasir ba ƙaramin me hikima ne ya shirya faruwar hakan ba, kuma shida aka sace su ta yaya harya iya dawowa ya sace mahaifin Widad, nifa ina da shakku akan wannan sakamakon fa"
Ramlah ta taɓe baki tace "ni dama wannan da ganinsa ya saba aikata laifi, kuma zata iya yuwuwa da wasu ya haɗa kai bashi kaɗai yayi ba, tunda ɗansanda ne yasan duk wasu hanyoyi na aikata laifi, kuma ba abun mamaki bane dan yayi garkuwa da ita, tunda yasan da yawa daga sirrikanta, har ATM ɗinta tama bashi, ba inda be sani ba a ɗakinta, duk wani gantali da zata tare suke zuwa, Allah kaɗai yasan iya abunda suke yi kaga kuwa ba abun mamaki bane dan ya sace ta"
"ƙarya kikeyi Ramlah!!! Nasani kin sani Wallahi Yusuf baze taɓa iya sace Widad ba, a gaskiya abun nan ya isa haka, haba dan Allah shikenan a dinga rayuwa babu tausayi ba imani, mutum beji ba be gani ba a ɗora masa wannan masifar, kun san hkuncin duk wanda aka kama da laifin garkuwa da mutane kuwa? "
A fusace Hajiya Halima tace " Ke Amal rufemin baki, ya isheki haka, koma meye hukuncin ina ruwan wani tunda harya iya aikata laifi mummuna irin wannan, yaje ayi masa duk hukuncin daya dace dashi, ina ruwan wani can ta Matse masa"
Ƙurawa mahaifiyarta ido tayi na wani ɗan lokaci, kawai tayi ƙwafa ta juya da gudu ta koma ɓangaren su tana kuka.
Kame kame Hajiya Halims ta shigayi "Amm gaskiya Amal yarinyar nan bata da hankali, tunda ta ƙyalla ido akan yaron nan ta fara sonshi shikenan ta susuce, bata taɓa yadda ace ga abunda yayi, yaro sekace iblishi, duk yabi ya saye zuciyar mutane da halin kirki amma yana zagayewa yana cutar da mutane, me siffar munafukai.
Wani irin kallo Anwar yabi mahaifiyarsa dashi, kallon data kasan tantance kallon meya ke mata, cam yace "koma meye dai, shi Allah ya haramtawa kansa zalunci sannan hmya haramtashi a tsakanin mu, dan haka yana kallon komai, Mummy be halatta kidinga saurin yanke hukunci akan abubuwa ba, baki da tabbas akan shiya aikata dagaske ko kuma bashi bane, amma kin zauna kina ta tsine masa kin aibata shi, nan akamin ƙazafi aka ɗaureni kika kasa samun sukuni sam, bakya tunanin shima uwace ta haife shi? Bakya tunanin wani hali take ciki itama a yanzu, kefa uwace Mummy, duk abunda zakiyi you need to have that feeling as a mother, saboda kema kin haifa, kuma kome ka shuka duk daɗewa zeyi tsuro ka girbi abunka da hannunka....
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
MASU FITARMIN DA LITTAFI KUJI TSORON ALLAH, AMANACE TSAKANIN NI DAKU, IDAN KUKA FITAR BAKUMIN ADALCI BA
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
72_73
Saroro Hajiya Halima tayi tana kallon Anwar, har yayi ya gama ya juya ya bar ɗakin.
Hajiya Halima tace "ke me yaron nan yake nufi ne? Naji yana wasu maganganu, kamar jurwaye me kama da wanka"
Taɓe baki Ramlah tayi tace "dan Allah ƙyaleshi Mummy, kin sanshi da sanyin haki da kuma tausayi, shi gaba ɗaya kamar bake kika haife shi ba saboda sakalancinsa, kawai dai surutu ne irin nasa, manta da shi kawai"
Hajiya Halima tayi ajiyar zuciya tace "Saura waccan makirar, bari inje inci ubanta, tana nema ta tonamin Asiri, 'yar banza mara mutunci"
Ramlah tace "A' a Mummy karki kuskura, kin san haukan Son Guy ɗin nan da take, kina matsawa ba taƙi ta ɓata komai ba, ki bita a sannu".
Tai ƙwafa tace "yarinya se kace yayi mata Asiri, duk zancen da za'ayi akan yaron nan seta kawo cikas, dani take zancen dan ƙaniyarta"
"ki daibi a hankali Mummy, dan ba taƙi ta zama rival ɗinki ba, kin san halin Amal sarai"
"Aikuwa da nayi maganinta, ina uwatta ta zama rival ɗina, amma nikam ba ƙaramin daɗi matakin nan yayi min ba, gaskiya mutanen nan basu da dama, kinga tunda akayi wannan sanarwar da an gano shi shikenan, a yanke masa hukunci kowama ya huta"
Ramlah tace "hakane, sedai ita uwar gayyar wani mataki zaku ɗauka akanta, dan bana tunanin zata bari a rufe shi, ƙaddara ma an rufesh ta yaya za'a karɓi abun hannunta, dan ba ƙaramar gaddamamiya bace"
"Allah masani, su suka san yadda za suyi da ita, nidai fatana ayi abani kasona kawai".. Suka kawashe da dariya kamar wasu ƙawaye.
Widad kam suna shiga ɗakin ta ajiye ledar data karɓa a hannunsa, ya zagaya gefenta ya ajiye na hannunsa ya kalleta yace
"Sannu da gida rigimammiya, tunda baki iya cewa miji sannu da zuwa ba, se tura baki kika iya"
Kallonsa tayi ba tace komai ba ta sake tura baki, ta nemi guri ta zauna, Yusuf yace "kin gama da ɗaliban naki ne? Naga kin zauna"
Tace "eh mun gama, na basu assignment ma, sannan nifa na bada kyautar pad ɗin nan, na basu suma su dinga amfani da su, zan baka kuɗi ka siyo musu brush da toothpaste, da shaver they need a lot counseling on personal hygiene, naga abubuwan nasu duk se a hankali"
Yusuf yayi murmushi yace "kaga malama ta gari me son ɗalibanta, naji daɗin hakan da kika yi dan kin temake su sosai kam, Allah ya baki lada amma a ina kika samu kuɗi?"
Widad tace "kuɗin sadakina mana, kuma yanzu na iya wannan maficin, Hindu kuma zata koyamin saƙa ksya, Mama tace idan nayi aka siyar na tara kuɗina, nikuma nace mata zomaye zan siya nima in dinga ganinsu"
Murmushi kawai Yusuf yayi, Widad akwaita da Wauta wasu lokutan, yace "Sannu sarkin son dabbobi, gashi nan Na auno mana shinkafa, na siyo mana kifi da gurji da albasa, zaki ci Abinci me daɗi yau, bari inzo in tsince shinkafar kafin magariba tayi"
"Yoseef wai me kake tsinta a cikin shinkafar ne?"
Yusuf yace "tsakuwa ce da sauran dattin dake ciki"
Widad tace "tsakuwa kuma? A cikin Abincin ake ganin tsakuwa kuma a ci?waye yake zubawa"
Yusuf yayi murmushi yace "Eh mana, ke kinma samu me tsakuwar, idan na gaya miki a inda nake samo me tsakuwar zakiyi mamakin nisan gurin, ko kinga gidan nan ana dafa shinkafa dukda a haka wai gidan megarine?"
Shiru tayi, tabbas tunda sukazo bata taɓa ganin an dafa shinkafa ba, babban abunda suka fi ci shine, dankali, rogo, kunu, se kayan rama, zogale da sauran kayan gargajiya.
Amma abun ya ɗaurewa Widad kai, wai tsakuwa a cikin Abinci, ta kalli Yusuf jiki a saɓule tace "Sannu da ƙoƙari, Allah ya saka maka da alheri, na tambayi Mama meye faskare, ta gayamin dama ina son in gaya maka, yakamata Kadena wannan aikin, kaga jikinka be saba ba"
Yusuf yai murmushi yace "eh jikina yafi saba wa da tuƙa motocinki manya masu AC, sanyi na ratsani ƙamshin turarenki ya hanani sukuni, shauƙin soyayyarki yaita ɗibata, gefe kuma anamin tsiwa ana dakamin tsawa, i miss that moment fa"
Dariya ya bata tace "hakama zakace?"
Yace "eh mana, sedai duk da haka nauyin ciyar dake a wuyana yake, dan haka zan iya kowane aikine muddin be saɓa dokar addini ba dan in ciyar dake, bani da hujjar da zan tsaya gaban Allah in faɗa na kasa ciyar da ke alhalin inada rai da lafiya, dan haka karki damu kinji beb" yai maganar yana kashe mata ido ɗaya.
Ta ƙara tabattarwa da kanta da lallai Yusuf na daban ne, shi dai akwai sanyin hali, ta tuna labarin da Daddynta yake bata akan Yayansa, hakan yana nuna duk masu sunan haka suke kenan.
Zuwa isha'i ya kammala girkin, ya haɗa shinkafa da manja da gishiri da tumatir da albasa, ga gurji ya marmasa musu kifi, ba ƙaramin daɗi Abincin nan yayiwa Widad ba, dan ko ba'a gaya mata ba tasan wannan Abincin da take ci yafi wanda take ci a gida lafiya, duk gayyar iyayi ga ba ƙoshi ake ba, ga kayan cutarwa.
Suka gama ci, ya ɗakko rake a leda, yace mata "ga tsaraba na kawo miki, ko shima baki sanshi ba"
Ta kalli raken ta harareshi tace "sugar cane ɗinne ban sani ba, amma bazan iya sha a haka ba, yayi min gjrma a baki"
Yusuf yace "toni ba abun in dinga gutsuro miki ina baki ba, kar in sa yawu kiƙi sha"
Hararasa tayi tace "yawu kuma na nawa, sedai kuma kar a ƙara, ka koyamin ƙazanta kawai"
"dama can kin iya a barki, bani na koyamiki ba"
"wallahi ban iyaba, dan ban taɓayi ba, kaika fara Yimin"
"Nayi miki me?"
"Kiss mana" Yusuf yayi dariya sosai, ba ruwanta wasu lokutan sosai yake ganin ƙuruciya da kuma wautar Widad.
Yusuf yace "Nima a nan na koya, ai"
Tace "Kai dai ka sani"
Murmushi yayi, ya samo wuƙa ya dinga sara mata raken ƙanana, tana ɗauka tana sha, seda suka gama shan rakensu tare, sunayi suna hira,
Yusuf yace "gaba ɗaya kayan ƙwalamar nan na gargajiya sunfi lafiya da inganta jikin ɗan adam, saɓanin artificial ones ɗin nan, suyi ta haddasa ciwo kala kala"
Widad tace "aikam dai