Showing 153001 words to 156000 words out of 209297 words
tace "Na shiga uku ni Halima, wannan wace irin masifa ce haka, Ramlah dama baki dena wannan halin ba, Kisha kwalba huɗu a cikin ki?"
Amal kam taɓe baki tayi tai nata guri ta barsu.
Kamar koda yaushe, yauma zaune suke suna tattaunawa, Bukar yai gyaran murya yace 'ga samu ga rashi, labaran kala biyune, masu daɗi da kuma akasin hakan, wannan yaron munyi magana da A dutse, ya tabbatar min a zama na gaba ze ƙarƙare shari'ar yaron nan, sedai wani hanzari ba gudu ba, ita wannan yarinyar da yake ita uwar Daula ce a jarabar taurin kai, taƙi bayar da abun nan, ba irin azabtarwar da banyi mata ba, amma taƙi ƙarshe ma se cewa tayi ai "Recording ɗin inda dukiyar take Daula yayi, ya bata itama bata san inda dukiyar take ba, kuma wai recoding ɗin yana hannun Wannan yaron Yusuf"
What! Cewar Alhaji Munir "to yanzu meye abunyi?"
Alhaji Musa yace "kawai aje kurkuku ta ƙarfin tsiya ace ya bayar"
Bukar yace "Mhmm, baku san azabar taurin kan mutanen nan ba, ya saka hannu kawai mugani a tabattar idan wannan signing ɗin nasa ne, me kama dana Daula, amma wallahi fafur yaƙi, shima an azabtar dashi kamar kamar me a gidan yarin nan amma yaƙi, na rasa abunyi"
Alhaji Haruna yace "a sake azabtar dashi mana, ya faɗi inda recording ɗin yake, ko kuma aje a ɗauke mahaifiyarsa, ai naga tana zuwa kotun"
Bukar yace "ai abun ya wuce tunaninku, idan mukayi wani yunƙuri zamu iya barin ɓarakar da za'a ganomu, komai a sannu ake samun sa, zan cigaba da bibiyar yadda za'ayi a samu"
Suka gama tattaaunawa suka watse, dama a office ɗin Bukar sukayi meeting ɗin.
Bayan fitowarsu Alhaji Haruna yacewa Alhaji Musa "Waini anya ba raina mana hankali Bujar keyi ba, yarinyar nan tana hannunsa fa, babu wanda yasan inda take, ta yaya za'ace ko yaya bata gaya masa wanj abun ba, nifa kamar mutumin nan raina mana hankali yake"
Alhaji Musa yace "kai dai bari kawai, kallonsa kawai nake yi, gaba ɗaya kuɗaɗenmu sun tafi akan wannan harkar, amma Har yanzu babu wata riba"
"ba gara kaiba akaina, ni kamanta wannan yarinyar ta damfareni, rabin kuɗin account ɗina ta kwashe fa"
"kasa a sato maka ita, kaci ubanta ta mayar maka da kuɗinka, ni yanzu kallon Bukar kawai nake idan be wasa ba, zan ɓallo ruwa...
LITTAFIN KUƊI NE, IDAN KIN SIYA AMANANE, IDAN KIKA FITARMIN KINCI AMANA, KIMIN ADALCI KIYIWA KANKI
AYSHERCOOL
07063065680
11/29/21, 8:55 AM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
138_139
Alhaji Haruna yace "kamar yaya zaka ɓallo ruwa?"
"Eh zan ɓallo ruwa mana, muddin naga za'a cuceni, zan tads husuma ne, daga fara harƙallar nan zuwa yanzu zunzurutun kuɗi nawa muka kashe? Haka abun yayi yawa, mutumin nan ba imani ne dashi ba, ze iyayin komai dan haka gara mu saka ido yadda yakamata"
Alhaji Haruna yace "hakane kam, shikenan se anjima se yadda ta yuwu"
Daga nan suka watse.
Ramlah har gari ya waye, tana tangaɗi bata san me takeyi ba zabo maye, kwalba huɗu ta shanye babu sirki da komai, tayiwa kanta caji na sosai, yayin da Hajiya Halima ta dinga kuka, ganin yadda shaye2 ya ratsa Ramlah haka, ga ɓatan Anwar yana cin zuciyarta, gashi duk 'yan kuɗaɗen data tara Shu' aibu ya karɓesu, ta rasa inda zata saka kanta.
Amal kam bata tasu takeyi ba, gaba ɗaya bata jin daɗin jikinta, ta rasa takamaimai meke damunta, tana zaune tana danna wayarta taga wani business, wanda idan kayi investing kuɗinka, zasu nunnuku a lokaci kaɗan, nan da nan ta gyara zama tana sake duba yadda bayanin abun yake, ta shiga link ɗin group ɗin da aka bayar, taga yadda mutane keta comments wai sun sak kuɗinsu an riɓanya musu an basu.
Nan wani tunani yazo mata, dan wannan maƙudan kuɗin da suke account ɗinta bata san ya zata yi dasu ba, dan haka ta jarraba saka naira dubu hamsin, bayan awannin biyar aka turo mata dubu ɗari da biyu, abun ya bata mamaki, nan ta dinga murna akan ta samu sana'a daga kwance zata dinga samun kuɗi.
Widad se kaffakaffa take da Cikinta, kar Bulama ya gane cikin nan yana nan be fita ba, dan ya fara ɗagawa sosai tana jin motsinsa, wasu lokutan yaji yana motsi sosai, wani lokacin kuma yayi dankam motsinma se kaɗan kaɗan, mussman idan bata da lafiya, duk lokacin da taji ya daɗe be motsa ba se tai taɓa cikin tana addu'a Allah yasa ba wani abunne ya sami abunda take ɗauke dashi ɗin ba.
Cuta kuwa kullum a cikinta take, gashi babu me gayamata yi kaza bar kaza, ita dai Sabuwa ta kan tirsasata ne taci Abinci, amma babu magani ga kwanciyar ƙasa da take, da shan abu me sanyi duk se tabi ta kukkumbura, babu hanyar zuwa Asibiti, ga Fahad dayake yawan kawo mata farmaki wasu lokutan, dan haka baccinma ba iya shi take cikin kwanciyar hankali ba, sedai tana yi tama farkawa, gani take da nannauyan bacci ya ɗauketa Fahad ze shigo yai mata wani abun.
Haka rayuwar Widad ke tafiya a wannan gurin da take, gashi dai yafi ɗakinta na ƙauye nesa ba kusa ba, amma ɗakinta na ƙauye ya fiye mata daɗi da kwanciyar hankali akan wannan ɗakin da take ciki haka a cike da wannan damuwar da tashin hanaklin.
Se wajen laa'sar sannan Ramlah ta dawo hayyacinta, daga wannan muguwar buguwar da tayi, taje tayi wanka ta canza kaya, ta nemi abunda zata saka a cikinta, ba tare da ta kula kowa ba, Hajiya Halima ce ta bita ɗakinta, ta sameta tana ƙoƙarin fara cin Abinci.
Ta ƙare mata kallo sannan tace "Ramlah, wannan rayuwar ita kika zaɓawa kanki ko? Rayuwar shaye2, Ramlah kwalba huuɗ fa kika shanye a cikinmi, ke ko tsoron lafiyarki bakya yi, bakya tausayin halin da nake ciki ko? Ban san inda ɗan uwanku yake ba, ga wannan uban naku yana ta min barazana akan ze tonamin Asiri, amma a haka kike ƙara gayyato mana wata matsalar, meyasa haka Ramlah? "
" Dan Allah Mummy ki ƙyaleni injibds abunda ya dameni, ni Fahad ze kalla yace baze Aureni ba, bayan tuntuni yasan zaman jiran sa nakeyi, amma zemin haka"
"to yanzu dan yace naze aureki ba shine zaki kashe kanki? Shine zaki sha wannan maganin haka? Haba Ramlah shikaɗai me namiji ko shine autan maza, kina gani kuɗaɗen hannuna duka babu sun ƙare, shine yake kawo mana wanda suke siyan kadarorin nan fa a ɓoye, ki lallaɓashi ku rabu lafiya mu samu mu sake wawurarar abunda ya samu mu siyar, idan muka siyar seki ƙyaleshi, Allah ya baki wani ki aura"
"Mummy, ni gaba ɗaya ma nakasa gane kan maganganun nan da kikeyi fa, kamar yaya babu kuɗi a hannunki, ina duk kuɗaɗen da kika saida filayen nan? Duk suna ina, kuma ga wannan kuɗaɗen da ake saka rai na gurin Bulama daze samo a hannunta suma basu samu ba, abun yazo da rainin hankali fa"
"wai bana gayamiki ubanku ke tamin barazana ba, kin sam maƙudan kuɗaɗen daya karɓa kuwa hannu na?"
Ramlah tace "wai wannan jakin da yazo harya mareni kike nufi?"
"Eh, shu'aibu dai"
"to meyasa kike bashi?"
"Ramlah idan shu'aibu ya tinamin Asiri na kaɗe, dan na gama yawo, mutumin nan hatsabibin gaske ne, baku da wayo lokacin da muka rabu ai"
"Lallai Mummy, wallahi dana san hakane baza'a bashi ko kobo ba, sedai yaje ya tina karya fasa, yanzu shikenan mun tashi a tutar babu? Duk wannan baƙar wahalar da mukayi? Yana gefe kika dinga tura masa kuɗi, baze yuwu ba Wallahi"
"bazs yuwu ba kamar yaya? Ai tuni ya yuwu, bashi kuɗin nam sune rufin asirinmu, kuma karki kuskura kice zakiyi wani abu, kinji ma gayamiki sannan Ramlaj ki shiga hankalin ki, akan wannan mummunar ɗabi'ar, babu inda zata kaiki shaye2 ba abunyi bame, kuma ba cinyewa bane "
'mhmm Mummy kenan, yadda raina yake a ɓace idan har ba caji nayiwa kaina ba bana jin daɗi, kawai ki ƙyaleni idan kuma kina buƙatar in dema shaye2 to tabbas Fahad ya aureni, idan bahaka ba bakiga komai ba har yanzu"
"Ramlah ni kike gayawa haka?"
"Ai gaskiya na gayamiki ba wani abu bz, idan harya Aureni shikenan an wuce gurin saɓanin haka kuma, komai ma zaki iya gani"
Ta ƙarasa magana, tare da fara cin Abimcinta, bata sake bi ta kan mahaifiyarta dake kallomta da mamaki ba.
Jiki a saɓule Hajiya Halima ta tashi ta fita ta bar ɗakin Ramlah, ranta sam babu daɗi, wai yanzu Ramlah ce a wannan mummunar hanyar.
Alhaji Musa sosai yake jin zuciyarsa tana ɗarsa masa wani abiua ransa, yana zargin Bulama kawai ƙoƙarin kifesu yake yi, yana can yana zare zaren, dan haka dole zeyi wani abu a akai, ta ƙarƙashin ƙasa ze bincika ya hani ko Bulama na karɓar wani abu basi sani ba.
Yauma akazo akace ana son ganin Yusuf, ya zata ma ko Ummace ko Suleiman wani ya kawo masa ziyara, sedai still wannan ɗan sandan ya gani, se wasu gandirobobi, aka saka Yusuf a wani tsukakkaken ɗaki, da gashi sesu a ciki, aka zaunar da Yusuf ɗan sandan ya kalleshi yace "Hmm Nasan kayi mamaki, ganin yarinyar daka ceta ta juya maka baya taje kotu ta bada sheda akanka ko? Dama haka mata suke basu da tabbas, gashi tana can tana hutawa, ranar da za'a yanke maka hukunci, a satin za'a ɗaura mata Aure da Fahad Bukar Bulama.
A razane Yusuf ya kalleshi yace "Bukar Bulama kuma?"
"Au kana mamakine? Ƙwarai Ɗan gidan Bukar Bulama, wato Fahad, yanzu haka ta aiko mune gurinka, akam cewar akwai ajiyar wani recording data baka, ka gaya mana inda recorder ɗin take, zamu je mu ɗauka '
Hankalin Yusuf sam baya kan Ɗan sandan, sedai nanata Bukar Bulama day keyi a zuciyarsa, wato abu biyune ya haɗar masa, ga mamakin Jin an Ambaci Bulama da Bukar, to kenam shine Bukar ɗin da Widad take magana kokuwa? Idan shine ya akayi gake zaune a hannun sa? Idan ya cutar da ita fa? Sannan wani irin azababben kishi ya taso masa, dagaske Widad ɗinsa ce zata Auri Fahad?
'to idan bata aure shi ba me kake so tayi? Kaida rayuwarka zata ƙare a kurkuku, kuma taje har kotu ta bada sheda akan ka' wata zuciyar ta tunasar dashi, amma dukda wannan abun ya kasa jin tsanar Widad a ransa, shi wani irin tausayinta ne yake kama shi ma, kuma gefe guda zuciyarsa ma cigaba da begen sake kasancewa da ita.
"Kai Malam magana nake maka fa!"
Ɗan sandam yai maganar cikin tsawa, Yusuf be razana ba ya kalleshi yace "ita Widad ɗince tace maka ta bani wani abu ajiya?"
"zan maka ƙaryane?"
Yusuf yace "to meze hana kayi ƙarya, tunda mutum ne kai ba mala'ika ba, kamar yadda tace muku ta bani ajiya, tazo da kanta ta Karɓa, ta gayamin lokacin data bani, sannan ta karɓa"
Ɗan sandan yai ƙasa da murya yace "ka bani tunda wuri, ko kuma a ran mahaifiyarka"
Yusuf yace "Ran mahaifiyata yana hannun Allah, babu wanda ze iyayi mata abunda Allah be rubuta ze sameta ba, Magana ɗayace, ni bata bani komai ba, idan kuma ta bani ku kawota ta gayamin lokacin data bani ajiyar recording ɗin"
Ɗan sandan nan ya jinjinawa azababben baƙin taurin kai irin na Yusuf, ya kalli gandirobobi yace "ku tambayeshi"
Yusuf be motsa daga inda yake ba, suka dinga buga masa kulki kota ina, sedai yana ƙoƙarin karewa, babu wata gaɓa ta jikinsa da bata masa ciwo saboda azabar dukan da yake sha a kowane lokaci.
Suka farfasa masa jikinsa, banda targaɗe dake yatsunsa saboda duka.
'zaka bamu ko bazaka bamu ba"?
Yusuf yace "ni bata bani komai ba na gaya maka, karka ƙara tambaya ta"
Ya ɗaga hannu ze wanke Yusuf da mari, Amma jarumin ya riƙe hannunsa yace "karka kuskura ka mareni, kuyita dukana har lokacin da zaku ga na dena numfashi, tunda haka kuke so, amma karka kuskura ka sake ɗaga hannu kace zaka mareni"
Suka kum sashi gaba da duka, seda suka ga baya motsi, sannan hankalinsu ya kwanta, suka tafi suka barshi a gurin.
Widad na zaune kawai taji gabanta ya faɗi, hakan yasa kawai ta fashe da kuka, domin ta fuskanci kamar idan Yusuf yana cikin mawuyacin hali se taji wannan faɗuwar gaban, ai kuwa ta hau aikin kuka, tayi ta gaji ta haƙura, ta cigaba da yi masa addu'a, tans tuno irin haƙurin daya dingayi da ita, ga rarrashinta da yake yawan yi, da yadda ta koyi abubuwa da dama a sanadin zama dashi Yusuf mutum ne, wani irin shauƙin soyayarsa ne ke taso mata, ta rintse ido ko zata samu sassauci a zuciyarta, tana jin inama tana buɗe idonta ta ganata a kusa da Yusuf, lallai so ba ƙarya ne ba.
"Allah ya fitomin da kai Yoseef, ka dawo muyi rayuwa tare, mu rainin cikin nan tare da kai, nasan da muna tare zan samu kulawarka" tai maganar tana hawaye.
Can kuma tayi wani tunani a ranta, wani irin kallo Yusuf zeyi mata idan Allah yasa ya fito, bayan taje ta tsaya a gaban mutane ta tabattar da Yusuf saceta yayi.
Cikin kuka tace "wayyo Allah na, Yoseef kayi haƙuri ba laifina bane, nayi hakan ne dan in ceci rayuwarka, karsu kashemin kai, ban manta halaccinka a gareni ba Yoseef, ba yadda zanyi ne"
Sabuwace ta shigo da sauri tana faɗin "lafiya kike kuwa? Kinga ki dinga ramgwatawa kanki wannan kukan da kike yi haka, naji ance kina da ciwon zuciya gashi ba ganin likita ake kaiki ba, karki kashe kanki a banza mana"
"Ni ki ƙyaleni inyi kukana, baki san abunda yake damuna ba, ki rabu dani dan Allah ki ƙyaleni"
Sabuwa tace "A'a Allah ya baki haƙuri, na ƙyeki yi abunki som ranki"
Widad ta cigaba da gunjin kukanta.
"Allah ya isa tsakanina da kai Bulama, Insha Allah se gawar jaki tafi taka daraja, Azzalumi macuci"
Bulama yace "yi addu'arki da kyau, ai ina kusa ba nisa nayi ba, duk abunda zaki faɗa ki faɗa"
"me Yoseef yayi maka? Meye laifin da yayi maka da kake azabtar dashi haka, kake neman cutar da rayuwar sa Kasashi a garari?"
Bulama yace "saboda ya raɓeku, ni kuma duk wanda ze raɓeku, in dai ba dani ze haɗa kai ba in mallaki abunda nakeso to tabbas bashi da wani amfani, shiyasa nake kawar da du wani makusanta a gareku, ko wanda ke shirin sama muku farinciki, kum ɗaukake shi da matsayi me girma, dukda baki yadda da mutane amma naga ya zama wani abun yadda a gareki, nasa an jarabbashi koze aminta damu, ya karɓo abun hannunki ya bamu, sena fuskanci shima irinki ne, me taurin kan tsiya, kuma ya dasa hasashensa da bincikensa a kaina, Allah yasa na farga da suri, da yanzu ya kassarani, dan haka dole in koya masa darasi "
Widad ta ƙure shi da ido tace" Shikenan, ayi dai mu gani, na yadda da rayuwata da Yoseef da Babana jarrabawa ce Allah yake mana, kuma ina fatan muyi nasara, Allah ya nunamin ranar da zata zo ka wulaƙanta, ka tozarta a idon duniya "
Bukar yace " daha baya kenan, bayan ns mallaki wannan dukiyar, sannan Wannan uban masu koɗaɗɗen idon, yaƙi bada recording ɗin, yace shi baki bashi komai ba, dan haka a wannan karonma dole ki san yadda zaki yi, kodai ya bayar kodai yaita shan wahala harya mutu a kurkuku, kamar Yadda nasa a ka kashe Bala a gidan yari "
Widad tai murmushi tace " Yoseef be san na bashi ajiyar nan ba, dan haka Kadena yaudarar kanka da tunanin ko zaka samu abun nan cikin sauƙi "
Bukama ya ƙure ta ido, ta ɗauke kanta daga kallon inda yake, yama rasa me ze mata saboda tsabar wasa da hankali da raina masa hankali da take yi.
Ya kalleta yace " shikenan, a bakin ran mahaifiyar Yoseef "
" itakuma me tayi maka? "
" zaki fanshe ta ne idan kika bada abunda ake nema, dan haka ki zaɓa ko ki bani abunda na nema, ko kuma a bakin ranta"
"Abunda ka nema yana hannun Yoseef, kuma shima besan meye na bashi ba, sedai ka kaini gurinsa in karɓa maka, amma karka cutar da ita dan Allah"
"Se kuma kiyi, ba dai taken ki rainin hankali da iya wasa ba, to zaki gane kurenki"
Widad ta bishi da kallo harya fice, ta kwanta a nan inda take, ta lumshe idonta tana tunani.
Mutane nata sauraren lokaci yayi, suji yadda za'a ƙarƙare shari'ar Yusuf, kullum Gidajen radio da dandalin sada zumunta zancen kawai ake yi, kowa yana tofa albarkacin bakinsa, wani ya tofa na alkhairi wani kuma ya tofa akasin haka.
Suleiman yaje kaiwa Umma ziyara shida matarsa Surayya, sedai kallo ɗaya zakayi mata kasan bayan damuwa harda rashin lafiya take fama.
Surayyah ce ta fara cewa "Umma kodai jikinne ya motsa? Naga kinyi wani iri"
Suleiman yace "nima nagani, ko gurin likita zamu koma ne?"
Umma tace "A'a Suleiman, ɗawainiyar nan tayi yawa, lafiyata ƙalau ai"
Suleiman yace "wace irin ɗawainiya kuma Umma, ai in dai da amana nine yakamata in kula dake, Umma ban san haka abun nan ze kasance ba, Abbas ne yace a bawa Yusuf aikin nam ze iya, na goyi bayan hakan na bashi aikin, dana san haka zata faru da ban bashi ba, kuma ace wannan abu ya faru dashi, in kasa kulawa da mahaifiyarsa, ai da banyi wa kaina adalci ba, ni dai ina baki haƙuri Umma"
Umma tace "haba Suleiman, ai duk wani mumina dole ya yadda da ƙaddara, ba kai ka kama Yusuf ba, kuma ba kai kasa aka kamashi ba, ƙaddararsa ce a haka, duk imani da girma irin na Annabawan Allah, seda ya jarrabesu to waye Yusuf da Allah