Showing 78001 words to 81000 words out of 209297 words

Chapter 27 - Akidata Book 2 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

742

banɗaki, taga suna rigima seta koma bata fito ba.

Widad ta samu kujera ta zauna kawai ta fashe da kuka, tama rasa kukan me take yi ne.
Yusuf kuma ya koma ɗaki, ya rasa abunda ma zeyi.

Gwaggo ta fito ta kalli Widad tace  "Amarya lafiya kuwa?"

Widad ta goge idonta da sauri tace  "bakomai"

Gwaggo ta kamo hannunta ta janyota zuwa ɗakinta, ta zaunar da ita akan gado.

Jamila na nan zaune a ɗakin, da yake da ta gama aikin da zata yi a ɓangarenta nan take tahowa.

Gwaggo ta kalleta tace  "Amarya, meyasa kike haka? Meyafaru ne ba wai sa miki ido nake ba, na kawo kai naga kina rigima da mijinki, yana baki haƙuri, ba wai ina son jin lallai meya haɗaku bane, a'a yakamata ki gyara mu'amalar Aurenki 'yata, ki samu namiji ya damu dake haka, ga mijinki yaron kirki me haƙuri, amma ki dinga masa haka, anya kuwa namiji ya miki laifi ya baki haƙuri amma kiƙi saurararsa ba' a haka 'yata"

Jamila dake zaune tace "Taɓɗijan lallai ke' yar gata ce, har ana baki haƙuri, lallai kinyi dace ai wani namijim shi ze miki laifi, kuma ya dinga fushi sekin bashi haƙuri, ai kekam kinyi dace"

Nan suka dinga yiwa Widad faɗa, suna mata nasiha akan yadda ake kula da miji, Gwaggo tace "Amarya mahaifiyarki na da rai kuwa?"

Widad ta girgiza kai alamar a'a,  "mariƙiyarki bata gayamiki yadda rayuwa take ne?"

Widad tayi shiru ba tace komai ba, nan suka zage suna mata nasiha, se kuma jikin ta yayi sanyi, tabbas Yusuf yana matuƙar haƙuri da ita, sekuma taji sam bata kyauta ba abunda tayi.

Jamila ta tashi ta goya 'yarta tace' zomu je ɗakina kiji wani abu".......


LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏


88_89


Widad ta kalli Gwaggo, ta kalli Jamila, Jamila tace "magana zamuyi"

Widad ta tashi tabi Jamila, suka zaga ɓangaren Jamila, ta buɗe ɗakinta tayi mata iso, suka shiga sannan ta kalli Widad tace

"dukda naga baki da sakin jiki da mutane, amma naji ina son in temakeki, kinga nima da a ƙauyen nan nake, da mijina ya aureni muka tafi can barikin sojoji, to a can nima naga abubuwa, duk banyi karatun boko ba, amma na bazama na fara nema, naga yadda mata ke kula da mijk, naga a mugun ƙauye nake bansan komai ba, a tashin da mukayi a garin nan komai iyayen mu basa iya gayamana, mussman da ya shafi ɓangaren Aure ba abunda suke iya gayamana, saboda kunya amma ita rayuwar Aure faɗine da ita, amma a ɗan zaman da nayi zuwan nan nawa na fuskanci abubuwa da dama, ta wasu ɓangaren kina ƙoƙari, amma ta wani ɓangaren kina da rauni, mijinki yana da kyau yana da kirki masha Allah, idan har kikayi sake 'yan matan ƙauyen nan zasu cigaba da bibiyar sane, kiyi ƙoƙari ki riƙeshi sosai saboda mijinki zinare ne, samunsa a cikin maza akwai wahala
Dan haka shi namiji idan yana ta taka, baka wannan dogon jan ajin, ai daya miki laifi idan ya baki haƙuri kawai a wuce gurin, idan ba haka ba ze fara tunanin ko bakya sonshi ne, ya fara leƙe leƙen wasu matan, idan da ba yayi to zaki koya masa da kanki

Sannan wasu lokutan kina gsyamasa baƙar magana, kuma hakan be kamata ba tunda mijin kine, ba kowace magana zaki dinga gaya maaa yadda kike so ba, a koda yaushe mune ƙasa dasu dan haka dole mi bisu, dukda ban san dalilin zamanku a garin nan ba, amm gaki sam babu abunda ya haɗa kalarki da ƙauyen nan, dan baki kama da wadda take a wahala ba, amma ke yanzu dake kaɗai aka bari ki kula da kanki a ƙauyen nan zaki iya? Babu lallai ki iya saboda haka kodan yadda yake tsaye yana kula dake, yake iya ƙoƙarinsa akanki ya cancanci ki girmamashi saboda haka.

Nasan ko ban faɗa miki ba abubuwan da Hanne take kinsan son mijinki take yi, dan haka seki kula sosai bar ganin kima da wannan kyan surar, yanzu se hankalinsa ya ɗauke idan kika gaza sauke haƙƙoƙinsa dake kanki.

Ki kula ki tsare haƙƙinsa, sannan rayuwar Aure duk ta haƙurice, babu yadda za'ayi ace kullum shi ze dinga baki haƙuri, tun yana ta taki zeyi watsi dake wataran, mata na rububin irin mijinki, dan haka dan Allah ki dinga haƙuri dashi, karki ƙara yi masa abunda Gwaggo ta gani ɗazu.

Maza na son a girmamasu, ka basu girmansu tunda Allah ne ya basu.

Dan Allah ki kwantar da hankalinki ki kula da mijinki, duk abunda baki gane ba ki tambayeni zan gayamiki, dan ita Gwaggo bakomai zata gayamiki ba saboda kunya"

Nan ta cigaba gayawa Widad abubuwa da dama akan sabgar Aure, wanda Widad sam bata sani ba, nan ta dinga koya mata kissa da dabarun zama da miji, wanda ita Widad sam bata taɓa sanin su bama, dan ita rayuwar Auren bata gabanta balle tasan meya ƙunsa.

Abun ya dinga bawa Widad mamaki, lallai wanda ya rasa uwa yayi kuka, ita banda yanzu ma wasu abubuwan bata sansu ba game da Auren, lallai Yusuf yana haƙuri, wata zuciyar ta ta tace  'amma ai Auren bogine bana gaske ba meye na damuwa da ɗaga hankali?'
Wata zuciyar kuma tace 'dukda hakan dai, ai yakamata ko yaya ki kyautata masa, ko bakomai ya cancanci hakan daga gareki, karki zama me butulci mana.

Duk da Jamila ba wata babba bace, amma ta gayawa Widad abubuwa da dama da yakamata ace ta sani, game da rayuwar Aure, wanda yanayin zamansu da Yusuf ita bata saniba.

Widad tayi mata godiya, sannan suka dawo ɓangaren su Gwaggo, koda ta koma Yusuf ya fita bayanan, dan haka ta shiga shagalinta.

Hari na ganin Widad a tsakar gida tace  "Mhmm yau ninaga abunda yafi ƙarfina yafi ƙarfin idanuna, wai nikam dama Yaya nace mutane ma na wa junansu ɗura kamar yadda tsuntsaye keyi?"

Gwaggo tace "to ikon Allah, nima ban sani ba gaskiya dan ban taɓa jiba ko gani, se yanzu a bakinki"

Hari tace "hmmm, ai ina ganin tsiyataku kala daban daban, wani abunma idan na gani na dinga Tuba kenan kar inje in fita daga musulunci ban sani ba, banda jaraba ace mutum yasa bakinsa a cikin na ɗan uwansa, saboda tsabar ƙazanta, yo nidai nasam tsuntsaye ne kawai ke yin haka, amma se gashi mutane ma nayi, kai ina ganin masifa ƙuru ƙuru"

Widad ta ƙura mata ido, Ba shiri Hari taja bakinta ta tsuke, tun kan Widad ta gayamata baƙar magana itama.

Widad a ranta tace  "ke wannan haƙoran naki, gaftara gaftara koraye wane mijin ze sha'awar sa bakinsa a naki? '

Yusuf ya dawo amma yayi watsi da Widad, yaƙi shiga sabgarta ya cigaba da harkokin gabansa, sam yaƙi kula ta, gaba ɗaya se taji babu daɗi, ta kuma rasa yadda zata yi ya kula ta.

Yusuf ya samu guri yai kwanciyarsa, ba tare da ya tsokane ta ba yau, koya mata hira, ko yazo inda take ya share ta kamar shikaɗaine a ɗakin.

Bacci ma ya nemi ya gagareta, gashi 'yan kwanakin nan ta fara sabawa da kwanciya a jikinsa, amma yaƙi kulata yau, gaba ɗaya taji garin ya mata zafi.

Da safe ma farkawa tayi taga yayi ficewarsa, ta rasa abunda yake mata daɗi haka nan jiki a sanyaye take komai, tayi wanka ta karya.

Hindu ta tsiri yin Faten tsaki, Widad tace suyi a kan risho ɗinta, suka gyara yakuwa tare da kabewa, anan Jamila ta sake lura shikansa aikin Widad bata iya ba, danma ba tun farkon zuwanta taga kwaɓar da Widad take ba.

Akayi fate aka gama, suka zuba suka fara sha, Widad da ƙyar tai spoon biyu tace

"ni gaskiya wannan abun ba daɗi, tayar min da zuciya ma yake, ga tsami ga gishiri ni na kasa gane ma meye taste ɗin Abincin"

Jamila ta dinga tsokanar Widad, wai kodai cikine kuma baya son faten, ita dai Widad har yanzu bata sake da Jamila ba, amma taji daɗin bayanan da tayi mata.

Kuma babban abunda yake burgeta da Jamila, kullum jaririyarta tsaf da ita, kuma idan taje ɗauka bata hanata, tana bata ta ɗauka.

Jamila tace "kun shirya kuwa?"

Widad ta tura baki tace "baya ƙi kulani ba, me zance masa?"

Jamila tace "kinga abunda nake gayamiki ko? Allah yasa ba budurwa yayi ba wadda zata dinga tarairayarsa ba"

Zare ido Widad tayi ta harari Jamila tace "shi ya isa ma?"

"Au haka kika ce?"

"Eh haka nace"

Jamila tayi murmushi tace "ai shikenan, cikin hira ta cigaba da ganar da Widad wasu al'amuran, dukda wani lokacin in anyi gabas se tayi yamma.

Da yamma taga su Gwaggo suna ta shirye shirye, Widad tace" Mama ina zuku ne kuke ta shiri haka? "

Gwaggo tace  " bikine zamu wani ƙauye a gabanmu, Yayar Baffa ce zata yi Auren 'ya"

"Mama zan biku nima dan Allah"

"Ahh haka kurum, da mijinki da komai a' a ba ruwana"

Widad ta marairaice tace  "dan Allah Mama"

Gwaggo tace "to ki tambayi Yusuf tukuna, danmu kwana uku zamuyi"

"to ai bazece komai ba, dan Allah nidai zan biku zanje nima in haɗa kayana"

"Amarya, babu yadda za'ayi muyi tafiya dake, ba tare da kin nemi izininsa ba, idan ya bari bakomai semu tafi'

Widad tace  " bari yazo in tambayeshi to "







Wani wahalallaen bacci ne Nurat take yinsa bayan sallar Azahar, wayarta dake ƙasan pillow ta fara vibrating, a ɗan razane ta farka, tasa hannu a ƙasan pillowa ta ɗakko wayar, ta amsa sannan ta saka a kunnenta   "Hello Brother"

"Nurat, kina gida ne zan shigo yanzu?"

Ta miƙe zaune da sauri tace "No karka zo dan Allah, Daddy yana gida yanzu ze iya fara zargin wani abu, kuma kasan ya hanani fita, amma me ake ciki?"

Khalil yace  "Aikin da kika bani na fara, amma ko kin san cewa Yusuf ɗin nan ɗan sanda ne?"

"Kamar yaya? Wai dama dagaske ne shi ɗan sanda ne? Naji a labarai na zata ƙaryane ai"

Khalil yace "to gaske ne, ɗan sanda ne na farin kaya, yayi basaja yaje a matsayin direba, kuma yayi garkuwa da yarinyar"

"Kahlil saboda wanke Yusuf yasa na sakoka a cikin wannan lamarin, dan Allah karka ƙara danganta Yusuf da wannan mugun aikin, baze taɓa aikata haka ba na tabatta"

Khalil yace "shikenan naji, karkiyi kuka, ai ina kan yin bincike ne, ban tabattar ba, abun da ake ciki zan miki magana, amma banda kuka kinji ƙanwata"

Nurat ta gyaɗa kai kamar yana ganinta.



Widad da wuri ta sallami ɗalibanta yau, dan wasa wasa da yammar nan cika tsakar gidan Megari akeyi, an samo musu alli da allo na rubutu, sannan kowa da littafinsa da abun rubutu, babban abunda yake burge Widad be wuce yadda suke girmamata ba, suna girmama malami a ƙauyen nan, kuma a hankali tana jansu a jiki yanzu, musamman 'yan ƙananan yaran nan, da sunzo kwanukanta ɗakinta har tsakar gidan duk se subi su gyara, saboda tsabar girmamawa.

Widad nata ɗokin Yusuf ya dawo ta tambaye shi, dan harta manta sunyi faɗa, seda ya dawo taga ba fuska, Yusuf be taɓa mata kwarjinin da yayi mata yau ba, sam ta kasa masa magana sedai kallonsa kawai da take yi.

Koda yayi alwala ya fita sallar magariba, se bayan isha'i sosai sannan ya dawo, ya ɗau Abincinsa ya fara ci, ta zuba masa ido amma ta kasa magana, can dai taita maza tace

"Yoseef dama, su Mama ne zasu je biki, shine tace in tambayeka idan zaka barni in bisu, inje inga yadda akeyi"

Banza Yusuf yayi mata, kamar beji me tace ba, "Yoseef magana fa nake maka"

"Kiyi abunda kika ga dama kawai" ya bata amsa.

Jin maganar tayi wani banbarakwai ba tsari, wai tayi abunda taga dama.

"Ka barni inje kenan?"

"Meye na tambayata kuma ne? Nace kiyi abunda kika ga dama, ai damani baki ɗaukeni miji ba, na kan manta in wuce gona da iri wasu lokutan, waini game mata, na kan manta ashe nifa direba ne, iyakaci in miki aiki ki biyani, dan haka idan harni mininki ne, to ban yadda kije ba, sedai nasan ba lallai ki yadda da hukunci na, saboda ban kai a kirani mijinki ba, ban isa komai a gurin kiba, dan haka kiyi abunda kike so, zama ko zuwa ya rage naki"

Yana gama maganar ya tashi ya bar mata ɗakin, wani malolon takaicine ya tokare mata zuciya, dama Wai Yusuf ya iya fushi haka?

Har washegari be kumabi takanta ba, tana ji tana gani su Gwaggo suka shirya yaransu da manyansu suka tafi aka barsu a gida, Jamila na ɓangaren ta nata bisu ba, se abokiyar kishin Widad wato Hanne bata bisu tace bata da lafiya ita bazata ba dan haka tana gida itama.

Da daddare Yusuf ya idar da sallar isha'i yana lazimi, Widad a hankali tace 
"Yoseef" ta kira sunansa kusan sau uku, amma yayi shiru, can tace

"Yuzarsef"

Da sauri ya ɗaga ido ya kalleta jin sunan data faɗa, dukda be amsa ba amma taga damuwarsa ta ƙaru, ya kifa goshinsa akan gwiwar ƙafafuwansa daya ɗage.

Sanye da zumbulelen hijjabinta tazo, tasa hannu ta ɗago fuskarsa tace "wani laifin na kuma yi maka dan na kiraka da Yuzarsef?"

Girgiza mata kai yayi, alamar a'a yana ƙoƙarin maida kansa.

Ta sa hannu biyu ta tallafi fuskarsa tace "Yoseef, me nayi maka ne? Dan Allah kayi haƙuri"

Yusuf yace "aini baki min komai ba, sedai yau ina son in san saki nawa kike so in miki?"

Gabanta ne yayi mummunar faɗuwa, tace  "kamar yaya? "

Yace  "kamar yadda na tambayeki, saki nawa kike so?"

"Yaushe nace maka haka?"

Yace "kin manta abunda kika gayamin ne? Ina son in koyawa kaina rayuwa ko babu ke ne, kusan koyaushe kina maganar in sakeki, duk ƙoƙarina bakya gani, bakya tausayamin ya zanyi? Gara idan muka rabu inda wani ɗakin duk rashin kyansa a bani, in lallaɓa in fara koyawa kaina zama ko babu ke"

Aikuwa ta fashe da kuka tace "nifa ban san nayi ba, ban san meyasa nake jin haushi idan naga wata ta raɓeka ba, tun jiya nake maka magana, amma kana shareni, se kulaka nake amma kaƙi ko kallona, na tambayeka abu ka hanani, kuma banyi ba, amma ka kama min faɗa, you want turn on me ko, shikenan"

Ta juya zata tashi ya Riƙeta, yace "babu wani dalili da zesa in juya miki baya, sedai nine kin kasamin adalci, bakya iyayi min adalci a wasu lokutan, kiyi ta bani wahala saboda kinga ina sonki ko?"

Share hawaye tayi, ba tare da tace komai ba, Yusuf yace "yanzu me kikeson ayi?"

"Ka dinga kulani, ka dena ɗauremin fuska"

"shikenan za'ayi yadda kike so, amma da bakinki nake son ki faɗi saki nawa kike so?"

Shiru tayi batayi magana ba, sema sunkuyar da kanta da tayi tana kallon wani gurin daban.

"Widad magana fa nake miki"

Ɗison hawayen ta ya gani yana ɗigowa a ƙasa, taƙi ɗaga kanta kuma taƙi magana.

Yace "shikenan, tashi kije ki kwanta"

Ta miƙe sum sum ta tafi katifarta ta kwanta, tai shiru tana tunani, wai yanzu dagaske Yusuf yake sakinta zeyi, se taji gabanta ya faɗi, 'to meye dan ya sakeki, dama ai akan haka kuke' wani sashe na zuciyarta ya gayamata.

'Amma dukda haka nayi sabo dashi, sabo me ƙarfin gaske, yanzu idan ya rabu dani ya zanyi? Zan koma irin rayuwar kaɗaici na ta baya kenan?'

Kawai ta sake fashewa da kuka, yana jinta amma yai shiru kamar be san tana yiba, se can dare bayan ya idar da sallar dare, yayi addu'oin da zeyi sannan ya tao a hankali ya hau kan katifar ya rungume ta a jikinsa, lokacin har riga tayi bacci, wannan fushin da yayi da ita na kwana biyu shikansa yaji a jikinsa, dan ba ƙaramin kewarta yayi ba, a jininsa yake jin soyayyar Widad na ratsashi, shi dai yana matuƙar sonta.







Kamar yadda Suleiman ya buƙata, Abbas yaje office ɗinsa, seda ya ɗan jira ya sallami baƙi sannan ya ganshi.

Bayan sun gaisa ne Suleiman yace "Abbas ashe ka shigo garin nan babu Labari, sekace wanda akayi zaman gaba aika leƙo a gaisa '

Abbas ya ɗan sosa kai yace " Ai Yallaɓai abubuwan ne dama duk se a hankali, kuma ni ɗanje ziyare ziyare ne, shiyasa amma dama can nayi niyyar in ɓullo a gaisa ai, da amana bazan watsar daku ba"

Suleiman yai murmushi yace "shikenan, ya aikin ya hanya?"

"Alhamdilillah, aiki can ai har yafi nan daɗi"

Suleiman yace "madalla ai haka ake so, nace ka kuwa ji abunda ya faru da Yusuf?"

Abbas yace "naji yallaɓai, abun ya bani mamaki, mutum a fuska mumini amma zuciyarsa ba Allah, saboda son zuciya kawai daga aiki seka yi garkuwa da 'yar mutane, gaskiya bewa kansa adalci ba, Yusuf ya bada mamaki"

Suleiman yai ƙuri da ido yana sauraren Abbas, se da ya gama sannan yayi ajiyar zuciya yace "to ai koma menene Allah baya bacci, kuma muna bayan ɗan uwanmu, Insha Allah, sannan bama saka ran Yusuf ze aikata abunda ake tuhhmarsa dashi sam, yanzu ni babban abunda yaaa na kiraka shine, kaga kaine babban Abokinsa, mahaifiyarsa tana cikin damuwa ƙwarai, naje gurinta take cemin taji ance kaje amma ba kaje ka mata jajen abunda ya samu Yusuf ba, dan Allah ka daure ka zagaya kayi mata jaje ko ka ɗebe mata kewar ɗanta"

Abbas yace "shikenan, dan dai wannan insha Allah daga nan ma zanje, Allah sarki insha Allah zan biya in gaisheta"

Suleiman yace "ba laifi hakan yayi kyau"

Abbas na fitowa yace "Aikin banza, ina ruwana uwatace ita,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login