Showing 156001 words to 159000 words out of 209297 words

Chapter 53 - Akidata Book 2 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

767

baze jarrabeshi ba, nasani Allah yana jarrabar bayinsa ne wanda yake so, dan haka inawa Yarona Addu'a, Allah ya bashi mafita ta idan bamu zata ba, sedai babu wanda ya bani mamaki kamar Abbas, ba ƙaramin mamaki ya bani ba, irin yadda yake nunawa Yusuf soyayya, Yusuf bashi da abokin daya wuce shi, da kansa yazo ya ɗau Yusuf ya kai shi gidansu yarinyar nan, amma yace be san zancen ba"

Suleiman yace "Umma kiyi haƙuri, ki dena tunawa kawai, mu barwa Allah mucigaba da Addu'a"

Umma tace  "Addu'a kam, na duƙufa ina nan inayi, kuma na saka anata saukar Al'qur'ani, na miƙawa Allah ya isar mana"

Surayyah tace "insha Allah, addu'arki bazata faɗi ƙasa ba Umma, amma Umma akwai Abinci a gidan nan?"

Umma tace "eh ina da Abinci"

Surayyah tace "dafaffe fa"

Umma tace "Aa', sedai in yanzu za'a girka miki, kina jin yunwa ne?"

Surayyah tace "hakan ya nuna bakya cin Abinci Umma, ƙarfe biyu yaci ace ai anyi girkin rana"

Umma tai murmushi tace "wayo kikayi min kenan?"

Surayyah tace "ai ramar taki tayi yawa, dama munyi magana da Abban Nihal ne, muna so ki koma gidanmu zuwa muga yadda hali zeyi"

Umma tace "A'a, hakanma nagode ku barni a nan, bazan ɗora muku wahala ba"

Surayyah tace "Umma ba wahala bace bafa, kinga kaɗaici yana damunki sosai, ga rashin cin Abinci, ga larurar rashin lafiya kina tare da ita"

Umma ta dage ba zata bar gidan nan ba, Suka dinga mata magiya sukace bazat wuce sati ɗaya ba, so suke jikinta ya warware.

Da ƙyar Umma ta yarda, Surayyah ta haɗa mata kayan ta, suka tafi da ita gidan Suleiman.


Yusuf duk iya azabtarwar daya sha, basu samu abunda suke so ba, ƙarshe ma Yusuf ya koma kurman ƙarfi da yaji, juyin duniya baya magana, itama Widad bata da maraba da 'yar prison ɗin itama, tayi wujuga wujuga itama, kamar korarriya ga Duka ga azabtarwa da take sha a hannun Bulama, duk ta fita hayyacinta.

Nurat ma bata da kwanciyar hankali, se fama take da damuwa da tunani, sedai ta rufe ɗakinta tasha kuka, gashi yanzu ta dena samun magana Da Khalil sam.

Haka gidan Hajiya Halima ya rincaɓe, Ramlah shaye2 ba kama hannun yaro, bata ganin kimar Mahaifiyarsu sam, yayin da Amal kuma gaba ɗaya haushinsu takeji, dan haka tai dumping ɗinsu gaba ɗaya a side, ta dena shiga sabgar su, ta kama wayarta take shiga wata caca a online da kuɗin data damfari Alhaji Haruna, sabgar ta kawai take ta dena shiga harkar mamanta da 'yar uwatta, idan taga Mummya zata dameta da koke koke ma, ko zancen Ramlah, se tai waje ta bar musu gidan, ko kuma ta shige ɗaki ta rufe taita danna wayarta, saboda tun kan Ramlah tai nisa da shaye2 Anwar yaso ɗaukar mataki akan lamarin, amma ta nuna bata so taci masa mutunci, dan haka na meye zata takura kanta akansu yanzu?.


Rana bata ƙarya sedai uwar ɗiya taji kunya, yau kotu tafi kullum cika, da mutane daban daban, duk ana jiran jin yadda zata kaya a wannan shari'ar, yadda aka rirriƙo Yusuf aka shigo da shi cikin sarƙa, yana jan ƙafa da ƙyar, saboda wahala.

Aka kammala wasu shari'ar da take kafinta su Yusuf, sannan akazo kan Tasu Yusuf.

Justice Abdullah A Dutse ya gama rubuce rubucensa sannan yace "duba da yadda muka fara wannan shari'ar, da irin shedu da hujjoji a gaban wannan kotu, kuma wanda ake ƙara ya gaza musanta abunda ake tuhumarsa dashi, an samu wanda ake zargi da laifin yin garkuwa da mutum, duba sashi na 273 na kundin penal court, wannan kotu ta yanke wa wanda ake ƙara hukuncin shekaru goma a gidan yari, ba tare da zaɓin tara ba, sekuma laifi na biyu da ake tuhumarsa dashi shine laifin fyaɗe ga ita wadda akai garkuwa da ita, duba da sashin manyan laifuka, ƙarƙashin sashe na 221 wannan kotu ta yanke wa wanda ake zargi hukuncin shekaru goma sha huɗu a gidan yari, tare da aiki me tsanani, sekuma laifi na gaba laifin sata da siyar da abunda ba mallakinsa ba, saida motar ita wannan yarinya wadda kuɗinta yayi naira miliyan talatin, wannan kotu ta yanke masa hukuncin shekaru bakwai a gidan yari, da tarar Naira million biyar, wanda ake ƙara idan hukuncin nan be masa ba, yana da damar ɗaukaka ƙara nan da kwanaki talatin masu zuwa "

Alƙali ya buga gudumarsa ta kotu, aka sake taso Yusuf a gaba, sarƙa hannu da ƙafa akayo waje dashi, kamar kullum duk yadda 'yan jarida suka so jin ta bakinsa, yaƙi cewa uffan.

Suleiman kuwa dama hana Umman Yusuf yayi zuwa ganin shari'ar gaba ɗaya.





Ramlah kuwa ta sake bin Fahad ɗakin Hotel, tana ta zazzaga masa bala' i akan lallai seya aure ta, Fahad yace "asje ke ƙwayar da kike sha, hauka ta saka miki ban sani ba, ko matan duniya sun ƙare bazan aure ki ba, kin zama second hand, kije ki samu wani ajawon daze iya rufamiki asiri".

Cikin ɓacin rai tace "ita wadda kake harin, itama ba second hand ɗin bace?"

'ai gara ita dake, koba komai ko second hand ce ai akwai kyau, dujda kema ba munine dake ba, amma ai kowa yana son canji, kuma itama da manufa zan aure ta "

" wallahi baka isa ba, kayi kaɗan Fahad, zan gwada maka Rashin mutunci, jaki macuci kawai wallahi bazan yafe maka ba"


"Ai babarki ce macuciya, itace babbar macuciya, kuma ina baki shawarar kije Asibiti a tabattar da lafiyarki, saboda akwai matsala a lafiya ta"

Maimakon hankalin Ramlah ya tashi, kawai se yaga ta ƙyalƙyale da dariya irin ta mugwayen nan.....



AMANA! AMANA!! AMANA!!!

Ayshercool
07063065680
11/29/21, 8:55 AM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"


140_141

Seda Ramlah tai dariya me isarta, yayimda Fahad ya bita da kallon mamaki irin dariyar da take ƙyaƙyatawa, tace  "Fahad ai duk yadda kake tunanina na wuce nan in gaya maka, shiyasa nake ta binka Allah ma'aiki ka aureni, ban nuna maka nasan kana ɗauke da cutar HiV ba harka samin ba, nake ta lallaɓaka amma baka gane ba, to na ɗau matakin daya dace, dan haka zan maka Albishir, Danni agurin Albishir ne, ina me farincikin sanar da kai cewa Ubanka Bulama ma yana ɗauke da wannan ƙwayar cuta "

Ai a razane besan ya miƙe tsaye ba akan ƙafafunsa, ya dinga binta da wani ƙasƙantaccen kallo, yace " mekike nufi? "

" Kurma ne kai? Ko yaren da nayi magana dashi ne baka ji, nace ubanka mahaifi wato Bulama, shima yana da cutar, na saka masa dan haka seka hanzarta kaje kasa shi ya fara shan magani akan lokaci, tun kan ciwon ya huda shi sosai, sannan yama da kyau ka binciki babarkama, ko itama ta rabauat seku duƙufa shan magani, kaga rabajau daku idan wannan ya manta lokacin sham magani yayi, se wannan ya tuna muku "

Kamar Fahad ze fashe da kuka yace" kina nufin, Dad ɗina yana ɗauke da wannan cutar ne? "

" babu ko shakka " ta bashi amsa

" Amma wace irin tinkiyace ke Ramlah, yanzu sekiyi mu'amala dani ki koma kiyi da mahaifina saboda mugun abu? "

Ramlah tace " duk cikin iya takune, da farko shiya fara ɓatamin rayuwa, na rufa masa Asiri, har na fara sonka, tun a wancan lokacin ya fara take taken baya goyon bayan soyayyar, kaima kazo ka nemeni na bada ksi bori ya hau ina zaton zaka Aureni, amma kaƙi kuma na kasa rabuwa da kai, duk da yadda Anwar ya dinga nusar dani, kawai naga magani a jakarka, na tambayeka na mene kace min na gyaran jiki ne, nai nai ka bani ka hanani, shine nai snapping nace a samomin maganin, aka gayamin na meye, nayi kuka na shiga damuwa amma nakasa gayawa mowa damuwata, na cigaba da shaye2 daka koyamin dan ragewa kaina tension, naga babu hanyar da zanbi in huce takaicin nan daka ƙunsami , seta hanyar sanyawa Ubanka wannan ciwon, se duk muyi jinyar tare, nake ta binka ka aureni kana rainamin hankali kana ganin ka cuceni, kuma ina me tabattar maka da cewa dukda kamilewa irin ta ƙaninka Ramadan, shima zan iya bashi nasa rabon, dan haka seka san abunyi tun dare be maka ba ".
Ta ƙarasa maganar tana hararasa, ta bar ɗakin.
Ya dafe kai ya zauna yana faɗin" Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Allah ya isa tsakanina dake, kin cuceni, ba kowa aka cuta ba se Mother, tana gefe ta kawamme kanta ta riƙe Aurenta an kwasa mata masifa, Daddy why? "

(dama ita zina haka take, idan ka yi da ɗan wani za'ai da naka, idan ba ayi da naka ba in one way or another, dole se wannan illar zinar ya shafi wani naka, zina bata da wata riba sam, ga zunubi, ga cuta ga ɗaukar alhakin wanda basuji ba basu gani ba, Allah ya shirya al'ummar musulmi baki ɗaya)

Fahad ya cigaba da kuka yana tunanin, ta yaya ze fara gayawa Mummy abunda ya faru, wama ze tunkara da wannan Mummunan labari haka?
Babu wanda aka cuta sama da Mummyn mu, dama har yanzu Daddy yana biye biyen mata? Innalillahi wa inna ialaihi raji'un.
"Ramlah kin cuceni, tsakanina dake Allah ya isa kawai ban yafe ba Wallahi, wayyo Allah na, ban taɓa dana sanin irin rayuwar da nayi ba se yau, ubangiji Allah yasa Mummy bata ɗauka ba, saboda abun kunya da Allah wadai, ace inbi yarinya mahaifina ma yayi, wace irin rayuwa ce haka? Ta yaya zan tun kari Mummy in sanar da ita ta binciki lafiyarta?
Fahad ya zauna zaman dirshan a ƙasa yana kuka, sekace ɗan yaye kuka harda majina, ya rasa inda ze saka kansa dan baƙin ciki da takaici, yau a dalilinsa za'a sakawa mahaifiyarsa wannan larura, koma an riga an saka mata, yanzu ta yaya ze tun kare ta da wannan maganar?


Seda aka watse daga kotu sannan Bulama yabi Justice A duste chamber, A dutse yai murmushi yace "ya kaga shari'ar tamu? Naga tunda muka fa fara shari'ar baka zuwa"

Bulama yace "ya za'ayi inzo, sannan shari'a tayi dan yi, shekaru talatin ai kan nan komai yayi dai dai , amma abunda ya bani mamaki shine meyasa zaka ce wai yana da damar daze ɗaukaka ƙara, ɗaukaka ƙarar na mene kuma? Tunda ka yanke hukunci, meye kuma na wani ze iya ɗaukaka ƙara kuma? "

" Bulama kenan, har yanzu baka san meye shari'a ba, babu yadda za'ayi aiwa mutum hukunci a irin kotunanmu sannan ka hanashi ɗaukaka ƙara idan hukuncin be masa ba, ba'ai haka ba haka ƙa'idar aikin take ba, nan da kwanaki talatin yana da damar daze je ya ɗaukaka ƙara "

Bulama ya ɗanyi ƙaramin tsaki yace " to yanzu meye abunyi? "

" Eh to, iyakaci kuyi ƙoƙarin toshe duk wata dama da zata saka ya ɗaukaka ƙararar, idan kuma ya ɗaukaka ƙararar, to se ka faɗi ka tashi suma ka siye su "

Bulama yai tsaki yace " Aini daya ɗaukaka ƙarar da kar ya ɗaukaka idan na samu abunda nakeso, can ta matse musu, ni yanzu zanje in maida hankali in samu abunda nake so "

A dutse yace "Shikenan, as you wish"

Bulama yace "Nagode sosai da gudunmuwar ka"
Suka musabaha, ya bar chamber.



Bulama kai tsaye gidan da Widad take ya nufa, yana zuwa ya tarar da ita a zaune cikin zumbulelen hijjabinta, ta ƙara zabgewa, duk babu ƙibar nan, Widad lazumi kawai take a zuciyarta, dan tasan yaune ranar daza'a yankewa Yusuf hukunci a kotu, sedai zuwa yanzu bata san wani hukuncin za'a yanke masa ba.

Bulama yazo ya sakata a gaba yana ƙare mata kallo, shikansa yaga yadda duk ta rame ta fita hayyacinta, mutum baya ce ita ce Widad Nasir Daula ba.


Tunda ya shigo bata motsa ba, balle ta ɗaga kai ta kalle shi, ta zuba guri ɗaya ido ko motsi ba tayi.

"Ina fatan kinji hukuncin da aka yankewa wannan sakaran xa kike iƙrarin mijinki ne? Koda yake ba lallai ki sani ba, amma shekarun babu yawa, shekaru talatin da ɗaya ne, se tarar miliyan biyar, sakamakon kama shi da laifin garkuwa da mutum, laifin fyaɗe da kuma sata, ina fatan yanzu kin san me Bulama ze iya aikatawa? Koda yake tun ba yau ba kin san irin abunda nake iya aikatawa idan ina buƙatar abu"

Widad bata motsa ba bata kalle shi ba, tai shiru abunta tana cigabs da ƙurawa guri ɗaya ido.


"Yanzu kin shirya gayamin inda abubuwan nan suke ko sena je nasa an kashe Uwar Yusuf"?


A hankali ta ɗaga kai ta dube shi, tace "kai a tunanin ka zan bar mijina ya shekara talatin da ɗaya a gidan yarine? Lallai baka da hankali, kuma ga dukkanin alamu ka manta wacece Widad ko? Zan baka mamaki kuwa, Yoseef baze zaman gidan yari ba, kuma bazaka samu abunda kake so ba"

"Kin zaɓi mahaifiyarsa ta mutu kenan?"

"Ba zata mutu ba se lokacinta yayi"

"Shikenan, tunda haka kika zaɓa, zaki gani kuwa"

Widad tace "meye ban gani ba Bukar, zalunci da mugunta wanne ne bakamana ba? Kasa aka kashe mahaifiyata, kasa aka haukatani, kai kutungwila ka aurawa mahaifina matar da ta dinga azabtar da shi tsawon lokaci, yana bauta ita da 'ya' yanta amma suna azabtar dashi, hakan be isheka ba kasa aka dinga kaimin farmaki dan a kasheni akan dukiyar nan, banda message na razanarwa da tashin hankali da kake turomana, ƙiri ƙiri ka rabani da ƙasata ta haihuwa saboda mugun zaluncinka, kasa nayi rayuwa kamar matacciya, babu me raɓata ka jefa tsoron mutane a zuciyata, kasa aka dinga farautata kamar dabbar daji, Allah ya kawo Yoseef na fara samun sassauci, nan ma akasa akayi garkuwa damu, muka kuɓuta ya dinga wahala dani, amma a ƙarshe kalli sanadin zaluncinka abunda aka masa, nida abun a kaina ya ƙare da sauƙi, shi meye nasa a cikin lamarin nan? Wallahi wata shari'ar se a lahira shi kaɗai ze sakamin wannan zalunci da kamin "

Bulama ya ƙyaƙyace da dariya yace " ke yanzu da duk kin san ni nake shirya wannan abubuwan amma kika ƙyaleni nake cin karena ba babbaka? Lallai kin iya wauta, meyasa kika ƙyaleni kikemin kallon uba bayan kin san ni maƙiyinki ne "

Widad tace " talala na maka, tun ranar da aka kashe mahaifiyata aka ambaci sunanka, bazan taɓa manatawa ba, sedai na ƙyaleka ne saboda muddin nai wani yunƙuri zaka kashe min mahaifi, shiyasa na ƙyeleka, amma a yanzu inaji a jikina kana daf da yin faɗuwar baƙar tasa"

"Hmm, lallai yarinya dole a sarawa ƙoƙarinki, da iya takunki tun kina ƙarama kanki yake kawo wuta sosai, kin iya lissafi sosai, Amma ki sani ni tsohon hannune a duniyanci, tunda hukuncin da akayiwa mijinki be zama izina a gareki ba, zan sa a kamo min uwarsa, inzo in yankata a gabanki tunda ke taurin kai baze barki ki ƙwaci kanki ba"

Wani mugun kallo tayi masa, ya tashi ya fita daga ɗakin nata, bayan tafiyarsa Sabuwa ta shigo ɗakin Widad tana dube dube tace "dan Allah ban yarda memory ɗina a ɗakin nan ba, tun jiya nake nemansa ban ganshi ba sam"

Widad tace "nima ban ganshi ba gaskiya, dan Allah Al'ada ne yazomin, tunda aka ciremin cikin nan ban ƙarayi ba se yanzu, dan Allah ki aramin dubu ɗaya, in rubuta miki irin wadda nakeso ki kai kowane shago a baki, idan Allah ya fitar dani zan bi yaki"

Sabuwa tace "to shikenan" taje ta samo biro da takadda ta bawa Widad ta raba takaddar biyu, Widad tai rubutu akan kowacce takaddar, da yake Sabuwa bata iya karatu ba, Widad ta rubuta ta bata ta ɗakko wata leda tace "dan Allah karki gayawa kowa na aike ki, ki kai shago kice a bani abunda na rubuta a jiki, ki haɗa musu da wannan ledar ki basu"

Sabuwa ta karɓa tace "shikenan, zan sawo maki insha Allah"

Widad tace "nagode sosai"



Mum Nurat taga sam bata ga gilmawar 'yarta ba, dan haka ta tafi ɗakin Nurat ɗin, tana zuwa ta tarar tayi wujuga wujuga saboda kuka, se rusa uban kuka take kamar ubanta ya mutu.

A ɗan gigice tace "ke lafiya kuwa? Meye ya faru dake haka? Me akayi miki ne?"

Maimakon ta bata amsa, sema sake rushewa da kukada tayi, "ke bana son sakarci fa, menene haka? Meya sameki kike rusa wannan uban kukan haka?"

"Mummy baki ga hukuncin da aka yankewa Yusuf bane?"

"To idanma na gani me zanyi, ko kuma me zance? Allah ya bayyana gaskiya kawai, amma shine zakizo kina wannan uban kukan haka? Ai koni na mutu iyakar wannan kukan kenan"

"Mummy wai meyasa kike basarwa ne, baki san menene yake wakana ba? Kin san fa komai Mummy? Daga gidan nan fa ake shirya maƙarƙashiya fa kin sani fa"

Da sauri Mummy ta ƙarasa, ta tishe mata baki tace "dan ubanki yana cikin gidan nan, so kike ya jiyo yazo yai miki wani abun?"

Nurat ta fizge tace "Haba Mummy, meyasa zamu ɗauke ido akan gaskiya Mummy? Wallahi ranar lahira muma harda mu a cikin wannan zaluncin da akayi, Mummy da saka hannun Daddy fa aka sace su Widad, Mummy da kunnena fa naji shi"

Maman Nurat na juyawa taga Alhaji Musa a ƙofar ɗakin, yana kallon su.

Nurat taƙi yin shiru tace "gaskiya Mummy idan mukayi shiru bamu da adalci, wallahi da saka hannun Daddy akan abunda ya faru, kuma kema kin sani, Wallahi da Daddy ake shirya komai, Mummy ya zakiji idan ɗankibaka yankewa hukuncin shekaru talatin da ɗaya a gidan yari? Kefa uwa ce Umma, bakya tunanin me mahaifiyarsa zataji a ranta a yanzu haka? Ancd shikaɗaine ɗanta amma an yanke masa hukuncin shekaru talatin da ɗaya a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login