Showing 159001 words to 162000 words out of 209297 words

Chapter 54 - Akidata Book 2 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

726

gidan yari "

Cikin tsawa Mummy tace " dan ubanki bazaki min shiru ba, seya miki wani abun tukuna? "


Nurat tace" Mummy nifa gaskiya nake faɗa, kuma ni zanje in bayar da shedar abunda ya faru, mahaifina yasan komai fa"

Alhaji Musa ya tako a hankali, yana zuwa bece komai ba ya danƙi hannun Nurat ya fara jan ta, a gigice Mummy tace "ya haka? Ina zaka kaimin 'yata? Ina zaka kaita? Karka cutarmin da ita dan Allah, ita kaɗaice' yata karka cutar da ita na gaya maka"

Be tankamata ba, ya dinga jan Nurat, Nurat tana faɗin "Daddy kaji tsoron Allah, a wannan shekarun naka me kakae nema a duniya haka, wanda zesa kasa hannu a zalunci wani, da Alhaji Nasir kake da matsala bada 'yarsa ko wanda beji ba be gani ba, dan Allah Daddy ku ƙyale Daula ya huta, da kunnena naji kana magana kune kuka saka aka sace Widad da direbanta, kuma yanzu kun sauya maganar kuna gabi aka kaishi kotu aka yanke masa hukunci akan abunda bejiba be gani ba"

Yana jan Nurat, tana biye dashi yayin da mahaifiyarta ke binsu tana masa magiya, wani ɗaki yaja Nurat can bayan ɗakinsa a ƙarshen bene, ya jefa ta ciki yasa mukulli ya kulle ta, ya juya ze tafi, Maman Nurat ta sha gabansa tace "meyasa zaka kullemin yarinya a wannan ɗakin ita kaɗai? Me yasa haka? Dan Allah ka buɗe mata ƙofar nan ta fito, karta cutu dan Allah"

Alhaji Musa yace "wallahi bazan buɗe ta ba, ashe kune manyan maƙiyanaba gidan nan? Dole ta bar ƙasar nan ko tana so ko bata so, kuma kema daga yau, bake ba fita ko ina, kuma duk sena karɓe wayoyin ki, munafukar banza da ta wofi"

"Niba munafuka bace, karka ƙara kirana da munafuka, halin rashin gaskiya 'yarka ce ta fara gano kana yi, dan haka babu laifina a cikin wannan batun? Dan Allah ka buɗemin' yata dan Allah ka barta ta fito, wallahi bazan bari tayi komai ba, dan Allah kayi haƙuri "

Tsaki yayi, ya raɓa ze wuce ta, amma ta sha gabansa tana kuka akan ya buɗe Nurat, aikuwa ya Tureta ze wuce bisa ga tsautsayi ta gangaro daga kan benen nan, ta ƙwala ihu da ƙarfin gaske, tun daga ƙafar farko har ƙasa, da sauri ya bita sedai kan ya ƙaraso tuni ta ƙarasa, ta faɗa da fuska aikuwa tuni jini ya wanke gurin, jikinsa yana rawa yazo ya ɗagota, fuskarta ta wanke tsaf da jini, gashi ko motsi ba tayi, akan idon me gadinsa ta faɗo daga kan benen.

Nurat ta jiyo ihun mahaifiyarta, amma bata san meyafaru ba, dan haka hankakinta ya tashi, ta shiga dukan ƙofar ɗakin da ƙarfin gaske tans kuka, tana kiran sunan Mummy.

Aka ɗauki Maman Nurat, zuwa Asibiti cikin gaggawa, ana zuwa aka karɓeta a Asibitin, da gaggawa aka shiga da ita emergency.



Sabuwa ta dawo gidan da Widad take, ta shiga gurin Widad tace "Nifa naje na kai musu, amma basu bani komai ba, sun karɓi takardar sun karanta, sun bani wata takardar, sun karɓi ledar sunce in tafi kawai, hadda tambayata wai waye ya aikoni?"

Widad tayi murmushi tace "inaga basu da ita ne, bani takardar da suka baki"

Ta miƙawa Widad takardar da suka bata, ta karɓa ta karanta, tai ajiyar zuciya tace "nagode sosai Sabuwa, sunce basu da irin wadda nake so, se Allah ya kaimu jibi kije ki karɓa"

Sabuwa tace "to yanzu ya zakiyi? Ga jini na zuba?"

"no karki damu, zan iya maleji zuwa lokacin da zasu kawo ɗin, bana iya amfani da kowacce se ita ne"

Sabuwa tace "to shikenan, Allah sarki ashe cikin ya fita dagaske?"

Widad tace "eh ya fita, ina son zan ɗan kwanta"

Sabuwa tace "to shikenan, se anjima"


Fahad fa ya rasa inda zesa kansa, da yaga mamansa, se yaji tausayinta ya kama shi, se yaji ƙwalla ta tarar masa, maimakon yaji haushin kansa, haushin mahaifinsa ya dinga ji, dan dabe nemi mata ba da babu abunda zesa mahaifiyarsa ta samu, gashi ya rasa ta inda ze mata wannan baƙin bayanin mara daɗin ji.

Gidansu Amal ma gidan sam babu daɗi, idan Ramlah taga dama a falo, haka take zuwa ta kama shan shisharta, kota kunna sigari tana busawa, ta baje kayan coadine ɗinta taita yiwa kanta caji, Hajiya Halima yanzu kam tsaro Ramlah take bata, sam bata iyayi mata magana, tana kallon ta, tana yi amma bazata iya cenata bari ba, Amal kuwa dama tuni ta fita daga harkar su.

Hajiya Halima na ɗakinta, ko izininta bata tambaya ba ta fice ta tafi Asibiti dan a dubata, sedai ta razana da sakamako ya fito aka tabattar mata da tana ɗauke da juna biyu, ta shiga ɗimuwa da tashin hankali, tun a Asibitin ta lalubi lambar Alhaji Haruna ta sanar masa da tana ɗauke da juna biyu, kuma ko yasan yadda zeyi da ita ko kuma tayiwa duniya Albishir da tana ɗauke da cikinsa.

Abubuwa fa suka rincaɓe sosai, Wata Nurse inyamuda ta jata gefe tace mata tasan inda zata kaita a zubar da cikin, in dai bata son cikin, ba musu ko tunanin komai Amal ta amince da a zubar da cikin.



Yusuf yana cikin fursunoni, yana zaund shiru kamar yadda ya saba zama, akace yayi baƙi ya kalli gandiroban ya ɗauke kai kamar beji ba, "Malam da kaifa neka" gandiroban yai maganar a ɗan hasale"

Yusuf yace "bazani ba"

"Kamar yaya bazaka ba?"

'me zanje inyi? An riga an yanke min hukunci, burinku ya cika kuda iyayen gidanku, me kuke nema a gurina kuma? Ko waye bazani ba"

Gandiroban yace "koda mahaifiyarka ce kuwa?"

Da jin haka Yusuf ya miƙe da sauri, se kuma yaji bashi da karsashin tunkararta ya kalleta, dan yasan abune mawuyaci sukuma rayuwa da Ummansa kamar da.

Yusuf yabi bayan gandiroban jiki a saɓule, yana dogara ƙarafarsa da kyar saboda ciwo da take masa.

Yana zuwa yaga wasu mutane a zazzaune, wanda be sansu ba sam, aka bashi guri ya zauna yana ƙare musu kallo.


Ɗayan ya kalle shi yace "sannu Malam Yusuf, sunana Barrister Hafiz wannan abokan aikinane" yai maganar yana miƙawa Yusuf hannu.

Amma Yusuf ya ƙeƙashe ƙasa yaƙi bashi hannu, ya kalle shi yace "me kuke nema a gurina? Bayan shari'a tazo ƙarshe an yankemin hukunci, me yayi saura kuma me kuke so inyu muku"

Yai maganar cike da karaya, ƙwalla na taruwa a idon sa.

Hafiz jiya yi kamar yayi kuka shima, ya maze yace "haba Yusuf, ai ka tsaya kaji meke tafe damu ai, Barrister miƙo takaddar nan"

Barristern dake gefensa ya ɗakko takadda ya miƙawa Hafiz, Hafiz ya karɓa ya miƙa masa yace "ga saƙo inji matarka"

Jikin Yusuf na tsuma ya karɓi takaddar yana buɗewa yaga rubutun Widad "



_Bani da abunda zan iyayi maka a halin da nake ciki I love you My Yoseef, but I will do my best to see what I can do for you, please pray for me, is either we should meet again or the time you will be free i pass away_

Yusuf yace " Innalillahi wa inna ialaihi raji'un"



AMANA! AMANA!! AMANA!!!

AYSHERCOOL
07063065680
11/30/21, 8:20 AM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"

_(INNALILLAHI WA INNA IALAIHI RAJI'UN  ina amfani da wannan damar gurin miƙa saƙon ta'aziyya ga Ɗaukacin zuriyar Hajiya Aisha Muhammad (Baba) bisa babban rashi da mukayi na rasuwar ta ina fatan ubangiji Allah ya jiƙan ta yai mata rahama, ya kai haske kabarainta, ubangiji Allah ya duba zuriyar da ta bari, ya bata ladan ɗawainiya da iyalI da tayi tsawon ranta, ubangiji Allah ya jiƙan kafatanin  wanda suka rigamu gidan gaskiya Musulmi, idan tamu tazo Allah yasa mu cika da kyau da imani_)

IN THE MEMORY OF LATE HAJIYA AISHA MUHAMMAD, I DEDICATED THIS PAGE TO LATE HAJIYA AISHA MUHAMMAD (BABA) MAY ALLAH SUBHANAHU WATA'ALA, GRANT HER JANNATUL FIRDAUSI AMEEN _

Ina ma'abota son gyaran jikinsu yau ga maman sayeed collection tazo muku d gangariyar maganin gyaran breast (nono)

      Maganinmu yayi fice gurin gyaran nono kikai amfani d maganinmu cikin 1week zakiga result maganinmu yana ciko d nono suyi bul² nono ko yakai silifas y mushewa kikai amfani dashi zakiga canji

  Maganinmu Bashi d side effect mun hadashi d tsirrai d saiwoyi kala² domin Y'an uwa mata

Muna kano muna tura maganinmu ko wane state d yardar Allah meso yakira wannan number 08120337219
Chat 08063114606








144_145




Ai zumbur ta miƙe zaune tace "ban gane a kasheshi ba? Anwar ɗin nawa za'a kashe? Me yayi masa haka?"

Alhaji Musa yace "ke nifa tuni na dawo daga rakiyar mutumin nan, Azzalumi ne kawai, kansa ya sani bashi da imani sam, ni kaina yanzu haka muna Asibiti nida su Nurat, amma gaba ɗaya ko yamin jaje se masifa da tashin hankali da yake min, shiyasa na kwashi kuɗina na saka a siyasa, in samu su bani takara in huta da wannan mulkin mallakar da yake mana, ga uwar dukiyarmu da muke narkawa amma har ynzu babu wani bayani "

Hajiya Halima ta fashe da kuka tace " ni Bulama zeyi wa haka? Anwar kamar ɗa yake a gurinsa amma shine zece a kashemin shi? Baze yuwu ba kuwa "

Ta ajiye wayar, ta miƙe ta shiga ɗakinta ta zura doguwar riga, kusan ƙarfe goma saura na dare, amma tayi waje ta ɗau mota ta fita ta tafi gidan Bulama a daren.

Shikuma Bulama yana zaune yana ta nazari akan yadda ze ɓullowa al'amura da suke neman damalmale masa, ya dinga kiran layin su Me Adda amma shiru babu Labari, waya taƙi shiga sam.

Masu gadi kansu sunyi mamakin ganinta a wannan daren, kamar wata mahaukaciya ko gabanta bata gani sosai saboda tashin hankali, kai tsaye ya shiga falon dake ƙasa tana bala'i  "Ina Bulama yake? Ina Bulaman?"

Iman ce zaune a falon tana kallon zee world tace "Mummy lafiya kuwa?"

"ban sani ba, ina uban naku yake tsohon macuci azzalumi?"

Iman ta kalleta da mamaki jin irin furcin da take akan mahaifinsu wanda ya kasance ɗan uwa a gareta, Iman tace "Mummy ya riga ya hau sama, inaga ma ya kwanta fa"

Ai bata tsaya jiran me Imana zata kuma ce mata ba ta haura saman da kanta, ba zato ba tsammani ya ɗaga kai yaci karo da Hajiya Halima a tsaye a kansa.

Ya kalleta yace "Halima, lafiya kuwa zaki zo a daren nan? Bakya jira ayi miki iso kawai ki hauromin ɗaki haka?"

"Dalla rufemin baki, me zaka gayamin har wani iso zan jira ayimin, munafuki azzalumin banza dana wofi, tsawon shekaru ina maka aiki, kana sani duk abunda kaga dama ina maka, dan ka cinma burinka ba tare da na nuna gazawata ba, shine halin naka na baƙin kumurci zaka gwadamin, shine kayi umarni da idan anga Anwar a kasheshi, ɗan nawa za'a kashe? Wallahi baka da imani ba kada Alƙawari tun wuri ka dakatar da wannan maganar idan ba haka ba Wallahi ran ɗana baze tafi a banza ba"

Zazzaro ido Bulama yayi ya dinga ƙifta mata ido akan tayi shiru, amma tace "bazan shirun ba, wallahi babu inda zani se an dawo min da ɗana"

"Halima wai wace irin magana kike hakane? Kamar yaya nace idan anga Anwar a kasheshi? Me Anwar yayi min wanda zesa ince a kashe shi, ni da na kaiwa jam'ian tsaro maganar dan ayi bincike akansa a gano inda yake ya zakice nace a kasheshi? Wani munafukin ne ke neman haɗani da 'yar uwata?"

" Kaga bana son kame kame da ƙaryar banza, wanda ya gayamin baze maka ƙarya ba, macucin banza da na wofi kuma wallahi idan ɗana ya mutu you must pay for it, wallahi aka kashemin Anwar seka fanshi ransa, nima kasan halina ka san abunda zan iya aikatawa "

Gaba ɗaya Bulama ya dirirce ya rasa abunyi, ya shiga tsuma yana fatan Allah yasa wani beji abunda ta faɗa ba.

Ya biyo bayanta ya leƙa, yaga ba kowa a falon ƙasa dukda ɗakin a rufe yake babu wanda ze iya jiyo me sukayi, ya koma bedroom ɗinsa ya tarar da Hajiya Sarah tana ta baccinta hankali kwance, yai ajiyar zuciya tare da tunanin bata jiba, amma ya zauna yai shiru akan gadon yana tunani, tabbas babu wanda ze gayawa Halima wannan maganar idan ba Alhaji Musa ba, tabbas dole yayi maganin Alhaji Musa.

Cikinsa ne ya murɗa ya tashi ya tafi banɗaki, kusan kwana huɗu kenan yana fama da gudawa taƙi tsayawa, dan haka ya sa ransa idan ya gama da wannan matter ɗin zeja yaga likita.

Yusuf se sake juya takaddar nan yake, yana tunanin wani hali Widad ɗin ke ciki, tabbas yasan da  tana da dama bazata barshi a gurin nan ba, dole akwai wani abu da yake gudana a ɓoye, idan ya kalli sentence ɗinta na ƙarshe na ba lallai su sake haɗuwa ba se yaji gabansa ya faɗi, lallai ko a ina take tana cikin mawuyacin hali, "Allah ya ƙara haɗa fuskokinmu my wife, Allah yasa kina hannu na gari, i love you too" yai maganar a hankali tare da lumshe idonsa.
Rayuwar da suka yi tare a ƙauye ta dinga dawo masa, koba komai zamansa da ita ba ƙaramin farinciki ya samu ba, zamansu a ƙauye yasa Ƙwaƙwalwarsa da zuciyarsa ta samu hutu na wani ɗan lokaci, ya daɗe beji cin zarafi da gorin rashin iyaye daga mutane ba, sedai matukar kewar Ummansa da yayi, be sake zaton ze samu wadda zata aureshi ba saboda rashin nasaba ba, sedai cikin hukuncin Allah ya auri yarinyar da zuciyarsa ta mato a sonta, dukda nisa da ratar dake tsakanin su, yarinyar da manyan wanda suka isa ma basa gabanta, soyayyar ma bata yadda da ita ba, amma Allah ya ƙaddara Aurensu, har suka yi zama cikin farin ciki, ya dinga tuna irin Shagwaɓarta wauta da yarinta wasu lokutan, ya tuna lokacin da take koyar tankaɗe, da sanda take wa Abincin garin kallon banza, da yadda ta dage ita seta samu ciki, da irin kallon da take masa idan ya tsokane ta.
A hankali ya sake lumshe ido yana murmushi, sekuma ya tuna yadda ta shiga damuwa daya bata labarinsa, da yadda ta dinga kururuwa tana kuka tana gaya masa tana sonsa lokacin da aka kama shi a garin, da yadda taje kotu ta bada sheda akansa, ga shekarun da aka yanke masa a gidan yari, ga abunda ta rubuta masa kawai se yaji ya karaya hawaye ya shiga bin gefen idonsa, baya tunanin ze sake wata rayuwa me daɗi a nan gaba, mussman kasancewa da Widad a inuwar Aure.

Da ƙyar likitoci suka samu Nurat ta dawo hayyacinta ta samu bacci, aka sa mata ruwa, sedai harta farfaɗo ɗin numfashinta da vital signs ɗinta suka daidaita bata gane mutane sosai, saboda ta galabaita an samu dai bacci ya ɗauketa cike da fatan idan ta tashi zata iya dawowa hayyacinta gaba ɗaya, mahaifiyarta kuwa gaba ɗaya har yanzu ba'a gano kanta ba, tana kwance ne kawai, numfashi ne kawai a ƙijinta, banda haka babu abunda yake aiki a jikinta, sam bata san abunda ke faruwa ba, shi kansa numfashin nata da ƙyar take yinsa wasu lokutan, saboda ta zubar da jini sosai, kuma ana kyautata zaton ta samu rauni a cikin kanta, sakamakon buguwa da tayi, likitoci sun rubuta mata hoton Ƙwaƙwalwa dan tabattar da abunda yake damunta.

Abu kamar wasa, jini yaƙi tsayawa Amal, se aikin zaryar banɗaki take, jini se zuba yake babu ƙaƙƙautawa, ta rarrafa ta haɗa Abinci tana ci kota samu sauƙin wannan wahalar haka, zuciyarta tana ƙuna akan yadda Alhaji Haruna ya cuce ta, Hajiya Halima ta fito falon ta zauna ta dafe kai ta kalli Amal tace

"wai kuwa lafiyarki ƙalau kuwa? Gaba ɗaya kin wani ɗashe kinyi fari ƙal, kamar baki da jini a jiki, ko baki da lafiya ne?"

Amal tace "lafiyata ƙalau, period kawai nake shiyasa"

Hajiya Halima tai ajiyar zuciya tace "Amal kin kuwa san abunda Bulama yaimin?"

"A'a sekin faɗa"

"wai an gano inda Anwar yake, amma yace wai a kasheshi saboda karya tona Asiri"

Da sauri Amal ta kalleta tace "A kasheshi kuma? Me me kikace masa?"

"Naje har gidansa jiya da daddare, na ƙare masa tatas, nace wallahi aka kashe min ɗana seya fanshi ransa da nasa ran kona 'ya' yansa"

Amal tabi mahaifiyarsu da kallo, wani irin baƙin ciki ya turnuƙeta, duk mahaifiyarsu ta ɗaiɗaita rayuwarsu da kanta, kowa yana karɓar nasa kason ɗaya bayan ɗaya.

Ramlah ce ta fito tana tangaɗi, tana magana cike da maye ta tsaya a tsakiyar falon tace  "Wai ni.... Waini Fahad baze Aureni bane... Bazaki ce ya aureni ba ko? Wa.. W.. Wallahi kuwa bazan dena shaye2 ba tunda ya lalatani, ku.... Kuma... Kumaaa ai shikenan tunda nasan Na sakawa Bulama cutar tunda shima ya sakamin... Wallahi idan baka Aureni ba sena sakawa Wannan yaron Ramadan ma, idan yaso kow... Ko..... Kowama ya samu ni za'ayiwa hauka? Ya.. Ya ɗauka bani da wayo hmm baka san Rmalha bane"  kawai ta faɗi a gurin tana juyi tana ci gaba da sambatu marasa kan gado sam.

Hajiya Halima ta kalleta tace "Ramlah wai wace cutar kike magana akai ne? Wace irin cuta?"
Ramlah bata san me take ba, juyi kawai take yi tana wasu surutan irin na marasa kan gado, Amal kam tasan babu mamaki idan akace Fahad yana ɗauke da wannan cutar me karya garkuwar jiki, amma sedai dagaske Ramlah take tana mu'amala da Bulama ma kenan, gaban Amal ne ya faɗi kardai ace itama tana da wannan cutar, miƙewa tayi da sauri zata tafi ɗakinta, Hajiya Halima tace  "Amal ina zaki? Kina jin maganar da gake faɗa? Ko dai duk a cikin maye take ne?"

Amal tace "tunda ki kaji ta faɗa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login