Showing 186001 words to 189000 words out of 209297 words
ina jin tsoro Umma, amma kinga Widad tasan koni wayey, tasan Halinda nake ciki amma muka zauna tare a haka, ba tare da ta nuna ƙyamarta a gareni ba"
Umma tace "kaga sauraramin, Itama Nurat ɗin zata iya aurenka ai, yarinyar bata da matsala kuma banga alamar wulaƙanci a tare da danginsu ba, nifa wannan Widad ɗince bana so, abun da ya samemu saboda ita bazan taɓa mantawa ba, duk wannan baƙar azabar ka shata ne saboda ita fa, amma baka gani "
Yusuf yace " Umma, Widad abun tausayi ce, baki san abunda ya faru da ita bane, ni kaina nasa....
Umma ta katseshi ta hanyar cewa "ban san abunda ya faru da ita ba, kuma bana buƙatar in sani, tun wuri ka kiyayeni akan wannan yarinyar, ita 'yar masu kuɗice ka barta taje, taimakon daka mata Allah ya amfana, kaima ka rungumi talaucinka, kuma idan ka sake ka taka kaje inda take zakaga yadda zanyi da kai, kalli dukda kayi free ai yakamata ko dubaka tazo tayi amma ba ita babu dalilinta"
Yusuf ya rasa yazewa Umma ta fuskance shi, Yasan dole Umma zataji babu daɗi saboda yadda take ƙaunarsa, amma Widad taje ta bada wannan shedar, amma taƙi bari ya gayamata abunda yake faruwa, wanda ita bata sani ba.
Babban abunda ya bawa Umma mamaki, be wuce yadda Yusuf ya ɓata rai ba, duk laifin da zeyi tai masa faɗa baya fushi, amma ƙarara a fusakrsa wannan karon, ya nuna beji daɗin hukuncin data yanke ba, ta dinga binsa da kallo, yai shiru bece komai ba.
Umma tace "yakamata kuma kaje ka sake yiwa Nurat gaisuwa"
Yusuf yace 'to, zanje insha Allah "
Ramadan yaji takaici jin labarin mahaifinsi ne ya dinga shirya duk wata manaƙisa akan Daula, dukda tarin alkhairansa a gareshi, babban abunda ya daɗaɗa masa rai kuma shine ba' a samu mahaifiyarsu da cutar HIV ba, amma yana ta sake zullumi akan ance su koma bayan watanni uku a sake yi.
Ramadan yace "Umma, yanzu shikenan Daddy ya lalata rayuwarsa, mu kuma ya bar mana abh mafi muni da abun kunya, ban taɓa jin labarin mutum me butulci kamar mahaifinmu ba"
Hajiya Sarah tace "bari kawai Ramadan, ni kaina nayi haƙuri da shi tsawo shekaru na masa biyayya iyayi na, amma ban taɓa zaton yanawa Daula zagon ƙasa haka ba, dukda wasu lokutan inajin haushin Widad, amma tabbas mahaifinku ya zalunceta, zalunci me muni ina fatan Allah yasa bani da wannan cutar, shi kuma yaje can yaƙarata, ya girbi abunda ya shuka '
Iman tace "waini Mummy, Yaya Fahad baze zo ya duba ki bane? Tunda muka taho Adamawa be neme mu ba, kuma a waya ba wanda ya kira fa"
Hajiya Sarah tace "ƙyaleshi kawai, ki rabu da shi, aini Na zubawa sarautar Allah ido kawai, nasan zaluncin da mahaifinku ya aikata muma se hakkin ya shafemu"
Ramadan yace "karkice haka Mummy, ai Allah baya kama wani da laifin wani, dan haka kiyi hakuri Allah ya yafe mana kurakuranmu"
Suka amsa da Ameen gaba ɗaya.
Ramlah ta farka daga uban baccin da take n shaye2 da tayi, lokaci ya ƙure tana wannan baccin, amma still damuwar dake tattare da ita bata sake ta ba, ji tayi ma kamar an ƙara mata wata damuwarne, akan wadda take ciki.
Ta miƙe a hankali amma bata ga Amal ba, tayi zaton ko tana ɗakinta ne, ta tafi ɗakin nata, ta duba amma nan ma bata ciki sam, ta sakko ta fito harabar gidan ta tarar masu aiki suna wa Amal fifita.
Ta taho da sauri tace "lafiya kuwa?"
Isa yace "wuƙa ta ɗakko ta fito da ita, tana yunƙurin kashe kanta, da ƙyar muka ƙwace wuƙar, shine ta faɗi ta suma"
Ramlah ta ƙarasa ta ɗago Amal tace "why Amal Why? Why will you attempt to kill yourself, why do you attempt to murder yourself? Haba Amal"
Ta kalli Nura tace ya kawo mata ruwa, ya kawo ruwa aka dinga shafawa Amal ɗin, can taja ajiyar zuciya ta buɗe ido, Ramlah tace "Amal meyasa zaki yunƙurin kashe kanki? Komai yai zafi maganinsa Allah"
Cikin kuka Amal tace "Mummy, Mummy na, Yaya Anwar, dan a kainin inga Mummy i love hery, she's my Mum, dan Allah kice ayi haƙuri bazata sake ba, ina son in ganta"
Ramlah ta rungumeta tana rarrashinta, tace "kiyi haƙy, za'a kaiki ki ganta insha Allah, amma karki ƙara yunƙurin kashe kanki, kinji ko?"
Amal ta jinjina mata, ta kama hannunta zuwa cikin gidan, yayin da masu aikknysuka shiga gulmarsu.
Gabaɗaya walwalar Yusuf ta ɗauke, ko Abinci baya iya ci, idan ya kwanta tunanin Widad kawai yake yi, yana son ya ganta sosai, Amma Umma taƙi.
Ya zauna yai shiru a tsakar gida, Umma ta fito da gyalenta a hannu tace "Yusuf bari zan ɗan shiga kasuwa, ba daɗeaayzan ba yanzu zan dawo"
Yusuf yace "to A dawo lafiya"
Tace "Allah yasa" ta sa kai ta fice.
Widad tana zaune ta tasa 'ya' yan itatuwa a gabanta, ta kasa ci ta zuba musu ido, tana kallonsu kamar ranar ta fara ganinsu, kamar an tsunkuleta ta tashi da hanzari, tai waje ta samu ɗaya daga 'yan sanda dake bata tsaro, ta tambayeshi ina wannan ɗan sandan da suka fita tare, yace mata "Ai ya tafi aikin da kika sashi ranki ya daɗe"
Tace "maza kiramin shi a waya"
Ba musu, ya kira shi a waya, aikuwa ya ɗaga ya miƙa mata wayar, Widad tace "ka gano min gidan nasu?"
Yace "eh na gano, naje na tambayi abokan aikina da suka kaishi Asibiti"
"a cikin ƙasa da mintuna uku, ka hanzarta ka turomin Adress ɗin"
Yace an gama ranki ya daɗe, aikuwa ya tura mata, ta karɓa ta duba ta shiga cikin gidan da sauri, taje ta shirya tsaf ta fito, bata sairari kowa ba, ta buɗe wata mota ta shiga, 'yan sandan suka taho kanta suna tambayar ina zata?
Babu wanda ta saurara a cikin su, ta fafari motar tana wani irin mahaukacin horn, wanda ya tilastawa masu gadin buɗe mata, saboda gudun ɓacin ranta, tai waje da motar a guje.
Nan da nan' yan sandan suka ɗau mota suka rufa mata baya.
Yusuf yana nan zaune, ya gaji da zaman tsakar gidan, ya tashi ya koma ɗaki, Sallama yaji a tsakar gida, ya amsa Sallamar daga ɗaki yace "Umman bata nan"
Me Sallamar tace "dan Allah zan sha ruwa"
Haushine ya kama Yusuf, shi ga abunda ya dameshi amma baƙuwa zata addabeshi, ya fito ransa a ɓace kawai yaci karo da Nurat, tai masa murmushi, gaba ɗaya ya ɗan ruɗe yace "dama kece?"
Nurat tace "Nice ko in koma ne?"
"Ni na isa ince ki koma, ɗazu Umma ta fita nasan zuwa yanzu tana hanya, shigo bismillah"
Nurat tace "Yaya Khalil yana waje, tare muka zo"
Yace "bari inje mu gaisa da shi"
Yusuf ya bata gurin zama a falo, shikuma ya fita waje, yana fita suka gaisa da Khalil, Yusuf yace "shigo daga ciki mana, ka tsaya a waje"
Khalil yace "A'a bazan shiga ba, Naga ta gaji da zaman kaɗaicine damuwa tana damunta, nace bari mu fito tazo ta dubaka ta gaida Umman kota samu relief"
Jiki a sanyaye Yusuf yace "Barrister ina matuƙar jin tausayin Nurat, ga kunyarta nakeji gani nake duk nine sanadin shigarta matsala"
"ka dena faɗar haka Yusuf, ai duk mumini dole ze yadda da ƙaddara me kyau ko mara kyau"
Yusuf yace "hakane, shigo mana"
Khalil yace "zan shigo, bari inje in ga abokina a nan ƙasan layin ku"
Yusuf yace "to shikenan" ya koma cikin gidan.
Nurat tana zaune a guri ɗaya, tai shiru Yusuf ya shigo ta ɗaga kai ta kalle shi tana wannan murmushin nata daya zama nature ɗinta.
Yusuf mabya mayar mata da murmushin, yaje ya ɗakko mata ruwa a fridge da lemo ya kawo mata, yace " Sannu da zuwa light, ga ruwa Kisha umma tana daf da shigowa"
Shiru tai tana sunkuyar da kai yace "ikon Allah, kunyata kuma kike ji? Ko kuma ba kya shan irin wannan?"
Ta girgiza kai tace "ni kowanne ina sha"
"Na gidanmu ne bazaki sha ba kenan"
Ta girgiza masa kai tana murmushi yace "idan Umma ta dawo kuwa sekin sha, Umma ba'a zuwa gidanta a ƙi karɓar abunda ta bawa mutum"
Ita dai sedai murmushin, amma ta kasa cewa komai.
Can Yusuf yace "light, wai nikam dan Allah ya akayi kika san da abunda na ajiye a wayarki?"
Cikin sanyin muryarta tace "ai ka taɓa cemin kayi ajiya a wayata, amma baka gayamin meye ba, lokacin da aka kama ka sena gayawa brother, harda ajiyar da kace kayi a wayar, shine yace in bashi wayar, ya dinga bincike a kai, daga nan ya kaiwa wani Abokinsa, ban san yadda akayi suka gano ba "
Yusuf yace " Aini bani da bakin da zan miki godiya Nurat, Allah jiƙan Mummy, Allah yasaka da alkhairi "
Tace " Ameen "
Can kuma tace " dan Allah dagaske kana da Aure? "
Yusuf yai murmushi yace " Waye ya gayamiki? "
" Kai ka taɓa gayamin, da na kiraka a waya, ka cemin kana tare da matarka "
Yusuf yace " A lokacin tsokanar ki nakeyi, bani da Aure amma a yanzu ina da Aure, Widad mata tace "
Ƙirjin Nurat ya buga da wani irin ƙarfi, take annurin fuskarta ya ɗauke gaba ɗaya.
Yusuf yace " ya dai? Ko kina sona ne, kamar kishi fa nake gani a fuskarki"
Ta ɗago manyan idanunta farare ƙal, ta sauke akan Yusuf, take taji ta karaya gaba ɗaya ƙwalla na neman cika mata ido.
"Yoseef!!!"
Yaji an kira sunansa, kuma babu me ambatar sunansa a haka idan ba gimbiyar Daula ba.
AMANA! AMANA! AMANACE!!!
LITTAFIN KUƊI NE.
AYSHERCOOL
07063065680
12/7/21, 11:04 PM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
156_157
Yusuf da Nurat duk suka ɗaga kai suna kallon inda Widad ke tsaye a bakin ƙofa, seda ƙirjin Yusuf ya buga da ƙarfi ganinta a tsaye, fuskarta babu Annuri sam, dan kwata kwata be taɓa zatan ganinta ba a wannan lokacin, ba Yusuf kawai ba hatta Nurat seda hanjin cikinta ya kaɗa, ta shiga fargaba saboda yadda Widad ɗin tai kicin kicin da rai.
Yusuf ya tattaro dukkan jarumtarsa, ya dake ya kauda fargabar dake zuciyarsa ya kalli Nurat yace "Light, gaskiya ki sha ko ruwane kafin umma ta dawo, bazanji daɗi kizo gidanmu ki tafi baki ci komai ba"
Fargaba ce lulluɓe a fuskar Nurat, jikinta se tsuma yake kamar taga zakanya.
Yusuf ya ɗakko ruwan roba, ya buɗe ya zuba a cup ya miƙawa Nurat, amma Nurat ta kasa karɓa se kallon Widad kawai da take yi, Widad ɗin dake tsaye tana huci.
Nurat tace "Amm.. Am naga kamar gurinka tazo bari in baku guri"
Yusuf yace "yi zaman ki kawai, idan wani abunne ya kawota ta faɗa a nan ina jinta"
Widad ta kalli Yusuf, taiwa Nurat wani mugun kallo, ai ba shiri Nurat ta miƙe, a ɗarare ta raɓa ta jikin Widad ta fice daga ɗakin, tana fargabar kar Widad ɗin tayi mata wani abun
Yusuf ya yunƙura daga kan kujerar da yake, ze bar mata ɗakin amma ta sha gabansa ta kalle shi tace "Yoseef, Anya kamin adalci kuwa? Na cancanci haka daga gareka? Bani da kowa se Allah, ba uwa, ba uwa, ba dangi ba kowa kasan bani da kowa se Allah, se kuma kai da nake sa rai, amma kamin haka? Yoseef tunda Allah yasa ka kuɓuta baka nemi inda nake ba, ina ta faman wahala da rayuwata babu me temakona se Allah, bani da wani jigo da zan jingina dashi inji farinciki, kawai se inzo in ganka da wata, bayan kasan zuciyata bazata iya jure hakan ba" tai maganar idonta taf ƙwalla.
Yusuf yace "ni bance ba kimin adalci ba seke zaki gayamin haka? Duk tarin wahalar dana sha saboda ke, amma kika kalli duniya kika bada shedar ƙarya a kaina Widad, baki tausayawa halin dana shiga ba, seni zakiwa kallon ban kyauta miki ba?"
"Yoseef, a tunanina ko kowa be fahimceni ba kai zaka fahimceni, na gaya maka komai, kasan komai game dani fiye da kowa, na baka dukkanin yarda wanda har hakan yasa na gaya maka waceceni, da abunda ya faru da rayuwata, kasan bazan taɓa yin haka dan in tozarta ka ba, dukda na ɓoye maka waye Bukar, ba nayi hakan ne dan komai ba se dan tseratar da rayuwarka, da kuɓutar da kai daga sharrinsu, na ɓoye maka Bukar shine Bulama saboda na bar hakan a zuciyata har ranar da zan kama shi red handed, sedai ƙaddara ta riga fata, amma shikenan tunda baka buƙata ta yanzu a rayuwarka, zan rungumi ƙaddara da irin rayuwar da Allah ya ƙaddara zanyi, amma kafin nan "
Ta saka hannu ta cire dogin hijjabin jikinta, wanda ya kasance har ƙasa, ta cire doguwar rigar abayar dake jikinta, ya rage daga ita se gajeran wando, da kuma half vest.
Tozalin da Yusuf yayi da cikin dake jikin Widad ne yasa shi ya ɗan rikice, tabbas idonsa ba gizo yake masa ba, cikine a jikin Widad gashi nan yayi girma sosai ya fito.
Ta ƙaraso gabansa ta kama hannunsa, ta ɗora a kan cikin nata tace "dan Allah Yoseef, koka watsar dani karka watsar da ɗanka, yau idan na mutu bashi da kowa se kai, dan Allah karka bari yayi irin rayuwar dani ko kai mukayi, Yoseef ka tausayamin ko dan ɗanka da nake ɗauke dashi.
Yusuf ya kalli Widad ya kalli cikin jikinta yace "You are pregnant Widad"
Ta jinjina masa kai, Yusuf yai murmushi yace "'yar baiwa, ashe Allah ya amsa Addu'ar ki, ya baki abunda kike nema, hankalinki ya kwanta" yai maganar cikin farin ciki fuskarsa ɗauke da murmushi.
Ya rungumeta a jikinsa hawaye na zuba daga idonsa, Widad ta rirriƙeshi itama tana kukan tana faɗin "We miss you Daddy me and your unborn, munyi missing ɗinka sosai, we really suffered, banyi zaton zan sake ganinka ba, bam zaci zanyi rai zuwa wannan lokacin ba"
Ta ƙarasa maganar tana sake fashewa da kuka, Yusuf ya sake manneta a jikinsa shima yana zubar da hawaye yace "i miss you too Babyna, i miss you my Queen, I love you"
"I love you too my Husband"
Sosai suke kuka daga shi har ita kamsr ƙananan yara, ya sake ɗagota ya kalli cikin nata, ya rungumota jikinsa ya haɗe bakinsu yana kissing ɗinta, hawayen tausayawa kansu na zuba a idonsa, yayin da itama kukan take.
Ya cire bakinsa daga nata, yana share mata hawaye ya kalleta yace "ɗan sake maimaita min abunda kikace yanzu mana"
Murmushi tai ta miƙa hannunta itama fuskarsa, tana share masa hawaye "tace me kake so in sake faɗa?"
"kin san koda ina prison, kalmomin nan da kika dinga faɗamin ranar da aka kamani sun tsaya a zuciyata sosai my wife"
Fashewa ta sake yi da kuka tace "dan Allah Yoseef ka dena tunamin kayi zaman prison please, zuciyata zata tarwatse, am sorry Yoseef duk sanadina ne ka shiga mummunan yanayi"
Yusuf yace "ni dai a sake cewa ana sona please" yai maganar a Shagwaɓe.
Ta noƙe kafaɗa tace "Anƙi ɗin"
"Ya akayi kika fara so nane?"
"Nima ban sani ba ai, Yoseef dan Allah ka dawo gareni, akwai maganganu dayawa da nakeso muyi, kuma kaga nikaɗai nake rayuwa ina farmhouse, kalli jikina duk ya kumbura, Yoseef zuciyata ciwo take, likitoci sunce idan nazo haihuwa ko dai muyi surviving, ko mu mutu gaba ɗaya ko ɗaya ya mutu ya bar ɗaya"
"Shhhhh hakan baze faru ba insha Allah, zaki haihu lafiya, kinga a yanzu haka ina ta fama da Umma saboda ke, kin san a rayuwa Umma bata son abunda ze taɓani, dan haka abune mawuyaci ta fuskanceni, saboda tana cikin kotu kika bada sheda a kaina, dan haka sena fara shawo kanta tukuna"
"Yoseef, umma bata sona kenan?"
"A'a ba haka nake nufi ba, taji ba daɗine abunda kikayi"
"Dan Allah kayi mata bayani Yoseef, nasan kaika fahimceni kasan komai fa"
"Na sani my wife, kiyi haƙuri, zanyi ƙoƙari inzo har farmhouse ɗin in ganki, yanzu maida rigarki in rakaki mota, nasan Umma na daf da shigowa"
Ai gaba ɗaya sun manga da batun Nurat, dan Widad ta manta ma da taga Nurat tare da Yusuf.
Ta tura baki tace "Nika ɗakko ka samin"
Ya harareta yace "zaki fara sani aiki ko?"
"Eh mana, tunda ka haɗani da aiki ai dole Kayi aiki"
Yusuf yai dariya yace "lallai kinyi baki, mara kunya kawai"
"Ai kaika koyamin rashin kunyar"
"Allah yasa Hari ta jiki, Kisha baƙar magana"
Widad tace "Allah sarki Hari mutuniyata, ina jin bayin Allah nan sosai a raina, ina kewarsu mussman Hinduna da Gwaggo, in komai ya daidaita zamuje insha Allah"
Yusuf yace "kin san kuwa wannan Sunusin, mijin Jamila yaje ya bada sheda a kotu?"
Widad tace "Nasani"
"Ya akayi kika sani?"
Widad tai ajiyar zuciya tace "shiyasa nace maka ina son mu haɗu, ina da magana da kai sosai"
Tai maganar cikin Shagwaɓa tana tura baki.
Yusuf yace "Malama karki sa mu saki layi, matso in saka miki rigarki"
Murmushi tai masa ta ƙara matsowa daf dashi, sedai yaga abu kamar kwanciyar bulala yai duhu akan fatarta, wajen damtsenta.
"Baby meye wannan?"
Yai maganar yana kallon hannun nata.
"Bakomai, samin rigata in tafi"
Shiru yai yana nazarinta, idonsa ya kuma sauka akan gefen fuskarta, nan ma wani tabon ne a gurin, ya sake kallonta zeyi magana tace "waiya kake ƙaremin kallo hakane kamar yauka fara ganina? Bani rigata in saka tunda kallona zakai ba samin ba"
Yusuf ya riƙe rigar yace "bazan taɓa gajiya da kallonki ba" yai maganar yana sake janyota jikinsa, yana sa fuskarsa a wuyanta.
"Naji, amma ka ƙyaleni in tafi, hankalina ya