Showing 39001 words to 42000 words out of 209297 words
BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
66_67
Mummunan labari, Islam 'yar uwar Huda, ta bawa me aikinta guga, yana cikin yi, me gidan ya dawo ya aike shi, koda me gugan ya dawo se ya tattare kayan gugar yace da safe ya ƙarasa, ashe ya manta be kashe dutsen gugar ba, cikin tsautsayi cikin dare dutsen ya ɗau zafi wuta ta fara ci, babu wanda ya farga, har wutar ta shiga gidan Yusuf Yayan Nasir, gobara ce ta tashi sosai, daga gidan Alhaji Abubakar, har gidan Yusuf babu wanda aka iya ceta, gaba ɗaya.
tsautsayin wutar nan ya ritsa dasu, suka ƙone ƙurmus a cikin wannan gobarar, 'yan unguwar sun kaɗu sun shiga cikin tashin hankali da wannan ifyila'i ya faru, se yayyafa musu ruwa akayi aka rufesu dan babu ta inda za' a iya sallatarsu.
Nasir ya kaɗu da samun wannan mummunan tashin hankali, dan bashi ba hatta Huda se kwasarsu akayi zuwa Asibiti, dan babu wanda yake cikin hayyacinsa.
Dukda Ahmad ma ya kaɗu ya shiga cikin tashin hankali, da labarin daya tarar na rasuwar mahaifinsa, dama shi mahaifiyarsa itace Uwargidan Alhaji Abubakar, kuma ta rasu yana da wasu matan amma ba a wannan gidan suke ba, da ya Auro Islam ne ya sakata a wannan gidan, ya dawo da Ahmad gidan, shima ya kaɗu ya shiga cikin tashin hankali, shine babba a gurin mahaifinsa gashi yana ji dashi, dukda ya sha wahalar matan uba, amma Auren Islam yasa ya samu sassauci, dan ita sam babu ruwan ta, dukda wannan masifar tashin hankali da yake ciki, amma ya tausayawa Nasir da Huda, dan duk wanda wannan mutuwar zata taɓa a bayansu yake.
Seda Nasir ya kwana biyar besan inda kansa yake ba, numfashi ma baya iyayi seda taimakon Oxygen, ita kuwa Huda tunda ta farka bata magana, sedai hawaye yaita bin fuskarta, ko Abinci bata iyaci balle magana, fuskarta ta kumbura tai jawur, ga rashin 'yar uwatta, ga ɗan uwan mijinta da matarsa, ga babu mijin' yar uwatta, ga mijinta a kwance shima rai a hannun Allah.
Se a kwana na Shida sannan Nasir ya farfaɗo, ya farfaɗo da kalmar la'ilahaillalah Muhammadur rasulillah salallahu alaihi wassalam "
Likitoci suka rufu akansa, suna monitoring ɗin bugun zuciyarsa, salati kawai yake yana faɗin " Yayana, ɗan uwana, shi kaɗai ne ya ragemin, Anty Nadiya da ɗansu duk babu, innalillahi wa inna ialaihi raji'un "
Wani liktane yace " haba ɗan uwa kamar ba musulmi ba, kayi haƙuri kayi tawwakali, idan kaji ƙaddarar wani seka rufe baki, kayi haƙuri mu samu mu ceci rayuwar ka, an san mutuwa da ciwo amma kayi haƙuri "
Nasir yace " likita, ɗan uwana ya mutu, da zan tafi umara ya muka dinga hira, ashe wasiyya ce, nayi rashi likita, banji rasuwar iyayena kamar yadda naji mutuwar Yusuf da Nadiya ba, har ɗan namu ma na rasa, innalillahi wa inna ialaihi raji'un wayyo Allah yayana"
Yai maganar yana fashewa da kuka, kamar ƙaramin yaro.
Likitan ya dafa kafaɗarsa yace "Allah yasan da kai, kayi haƙuri, Allah shike da rayuwar kowane bawa, ka kwantar da hankalinka, matarka mafa tana can munata ƙoƙari akanta, karta rasa hankalin ta, idan taganka a mawiyacin hali to jikinta ze rikice"
Jinina kai Nasir ya shigayi yana "Allah sarki Hudana, Huda munyi rashi, mun rasa 'yan uwa dagani harke, Allah ka zama gatan mu, Allah kayiwa bayinka Rahama"
Likitan ya amsa da Ameen, yana cigaba da kwantarwa da Nasir hankali.
Nasir yace "likita, ku kaini inga matata"
Likitan yace "A' a ka bari za'a kawo ta, har nan inda kake bama son ka dinga wahalar da jikinka"
A wannan kwanaki biyar ɗin Huda tayi ɓari, amma saboda halin da suke ciki ba'a sanar musu ba, dukda alhini da Ahmad ke ciki, amma a haka yake ta sintiri a Asibitin, wata ƙawar mahaifiyar su Nasir ce take sintirin jinyar Huda, yayin da Ahmad ke kula da Nasir, 'yan unguwa nata zuwa yi musu jaje da kuma duba su.
Duk Wanda yaga halin da suke ciki, sya tausaya musu, gaba ɗaya sun rame mussman Huda abun yafi mata yawa, yanzu ta rasa kowa da komai nata, se Allah da kuma mijinta Nasir, shima gashi a kwance se yadda Allah yayi dashi, ga ɗan uwan mahaifinsu ya sallamasu, dan bezo Nigeria gurin ta'aziyya ba, kuma labarin gobarar ya iskeshi, yace suje can su ƙarata ba abunda yayi masa zafi.
Nasir ya takura akan yana son ganin Huda, a haka aka turo Huda a wheel chair tazo duba Nasir.
Tana ganinsa a zaune ta ɗanji sanyi a ranta, ganin nasa jikin da sauƙi, ana ƙarasawa da ita suka rungume juna suna kuka, Kuka me tsuma zuciya, a hankali Huda tace "zaujee, mun rasasu gaba ɗaya babu wanda yayi rai a cikin su '
Nasir yace " Na sani Huda, babu yadda muka iya se mu rungumi ƙaddararmu, sukuma mu cigaba da yi musu Addu'a "
Nan suka dinga kuka, aka rasa me rarrashin wani, Ahmad ne ya shigo ya tarar dasu a wannan yanayi, suna ta kuka.
Ahmad yaja kujera ya zauna, ya dubi su Nasir cike da rauni da karaya shima ya fara magana yace " Nasir, dama itafa duniya munzone tamkar matafiya, dole wataran mu barta, sannan dukkan ɗan Adam dole ne Allah ya jarrabe shi, Allah baya barin mumini babu jarrabawa, dan haka nida ku mu rungumi ƙaddrara mu, mu yi tawwakali mu barwa Allah komai, shi ze bamu mafita, su kuma da muka rasa muyi musu Addu'a "
Ahmad ya ƙarasa maganar, ƙwalla na zuba daga idanunsa, amma ya cigaba da tausarsu yanayi musu Nasiha.
Seda suka shafe sati biyu a Asibiti, saboda jikin Nasir, dan zuciyarsa ta taɓu saboda damuwa, haka likitoci suka gindaya masa sharuɗa da magunguna, sannan aka sanar dashi ɓarin da Huda tayi, sam da gashi har ita basu san da cikin ba, dan koda zasu tafi umara da aka yi gwaji babu, yanzu kuma an tabattar masa da cikin watansa uku ma, Ba laifi Bulama ma yayi zaryar Asibitin nan sosai, saboda Nasir, dan dukda rashin jituwar da yake da Yayan Nasir ya tausaya masa wannan rashin da suka yi lokaci ɗaya, shima ya dinga rarrashin Nasir, akan ya kwantar da hankalinsa ya rungumi ƙaddara.
A haka aka sallamesu suka koma gida, sedai babu me iya rarrashin wani a cikinsu, idan abun ya taɓosu se su wuni kuka ita dashi, dama ga Nasir da raguwar zuciya, su wuni cikin damuwa babu me ko iya cin Abincin, saboda dukkaninsu mutuwar tana dukan su.
Kusan watanni Uku, da mutuwar har ɗan gara Nasir ya fara jarumta yanzu, amma Huda kam babu wannan batun, musamman gari ya waye da ta saba ta tafi gidan Nadiya, ko Yayarta Islam taje taita musu rainon 'ya' ya kasancewar tana matuƙar som yara, amma lokaci ɗaya Allah ya karɓe su gaba ɗaya.
Yanzu Nasir na iya zaman rarrashin ta, yaita bata baki yana tausarata, yace "Huda, ni dake Allah ne gatanmu, shiya haliccemu gaba ɗaya, kuma yafi mu sonsu daya karɓesu, ni dake dole muyi kukan maraici, nasan zakiyi tunanin ya rayuwarki zata kasance a nan gaba? Huda a duniya bayan iyayena ina jin maganar Yayana fiye da tunaninki, kuma nima nasam abunda ya dace, nasan gwagwarmayar da akayi kafin in Aureki, dan haka ko sau ɗaya karki sawa zuciyarki Nasir ze juya miki baya, nida ke yanzu gaba ɗaya muna cikin maraici gaba da baya, dan haka mu rungumi ƙaddararmu mu rayu tare, mu jure duk wani ƙalubale mu kasance a tare har zuwa namu wa'adin, in dai ta ɓangare nane, Insha Allah bazaki zubda hawaye ba"
Huda tayi ajiyar zuciya tace "Zaujee, nima nasan abune mawuyaci in fuskanci ƙalubale ko juya baya daga gareka, ina da kyakkyawan yaƙini akanka, amma dole in koka, munyi rashin da ba zamu mayar da wannan gurbin ba, kamar yadda ka faɗa insha Allah, duk tsanani zan jure duk wata ƙaddara in rayu da kai, bani da kowa se Allah sekuma kai"
Nasir yace "Insha Allah, bazan baki kunya ba Huda, nasan halaccin da kikamin a rayuwa, dan haka insha Allah zan kasance dake, zan kasance me baki kariya, kuma zan zame miki mijin marainiya insha Allah"
Haka su dinga kwantarwa da junansu hankali, suna bawa junansu haƙuri.
Amma duk da haka, Huda ta kasa sakin jiki ta haƙura gaba ɗaya, ƙarshe seda Nasir ya bar unguwar gaba ɗaya ko hankalinta ya kwanta, dan ko fita tayi tazo wucewa ta layin gidajen ƙarshenta idan ta fara kuka hadda suma.
A haka Nasir ya daddafa ya cigaba da kasuwancinsa, kuɗi ko ta ina shigomasa suke, a haka har Ahmad yayi Aure, Bulama ma ya tattago maganar Aure, kusan Nasir ne yayiwa Bulama komai na Auren, dan har gidan daze zauna shiya bashi.
Shikuma Nasir likkafa se ƙara cigaba take, gaba ɗaya ya zama busy man, yawo ƙasa ƙasa kasuwanci kala kala, duk ba wanda ba yayi.
Shine saida kayan sarƙoƙi, motoci, kayan masarufi, ga shaguna da yake dasu a kasuwa, na siye da siyarwa, hannun jari dayake siya a manyan kamfanunnuka.
Nan da nan ya zama kamar bashi ba, gashi dai matashi amma ya tara kuɗi.
Nasir ya ɗauki Huda sukaje ƙasarsu can Maroco, amma baffanta yayi musu wulaƙanci, Kasancewar besan Nasir ya fara arziki ba, yayi musu fata fata yace yadda aka cinye 'yar uwatta itama haka za' a cinyeta, haka suka dawo Nigeria da ɓacin rai.
Ganin Huda ta kasa samun nutsuwa har yanzu, ga tarin damuwa data sa a ranta, hakan yasa ya ɗauketa ya tafi da ita ƙasashen waje, can Dubai inda yafi harkokinsa, ya koma makaranta a can, sedai tun bayan ɓarin nan Huda bata sake samun ciki ba, kullum cikin addu'a take ubangiji Allah ya bata rabo itama.
Ya zamana Huda tana Dubai, kowani abun zezo yi Nigeria, ita tana can duk dan ya samu ta rage damuwa.
Seda suka shekara takwas da Aure bata sake yin ko ɓari ba, abun duniya duk ya addabeta, shikam ko a jikinsa, dukda yana addu'a sosai a ransa a bun yana damunsa, amma sam baya nuna mata, ta takura masa sukaje Asibiti akayi musu gwaje gwaje, amma akace lafiyarsu ƙalau.
Se a shekara ta tara Allah yasa Huda ta samu ciki, aikuwa Nasir yayi murna babu adadi, nan suka shiga rainon cikin nan da tattalinsa, gefe guda kuma ya zama matashin ɗan kasuwa na farko, wanda sunansa yake zagawa a cikin Nigeria, a hankali yasan manyan 'yan siyasa da attajirai, saboda har harkar kwangila yake yi, nan dangin mahifinsa suka shiga ƙoƙarin nuna ai ɗansu ne, amma fafur yaƙi yadda su raɓe shi, a cikin dangi can suka haɗu da wani Musa, sun ɗan haɗa alaƙa amma ba irin ta sosai ɗin nan ba, ɗan unguwarsu ne dai, ya dinga shisshigewa Nasir, tun Nasir na basar dashi, har ya fara sakewa dashi.
Musa ya nuna sha'awarsa ga harkar siyasa, Nasir ya haɗashi da manyan 'yan siyasa, ya goyi bayansa akan harkar siyasar, nan da nan mutane suka karɓi Musa, a dalilin Nasir, kasancewar Nasir mutum ne na mutane, mutane na ƙaunarshi saboda hannunsa a sake yake, ga shaharar da yayi ganin Nasir ne ya talatta Musa da kansa, hakan yasa mutane suka karɓe shi hannu biyu biyu.
Bulama kam basa jituwa da Ahmad, dan haka ya dinga shiga yana fita danya raba Ahmad da Daula, gashi kusan duk wani harkar kasuwanci Ahmad ne yake jan Daula, dan tun yana ƙarami Mahaifinsa ɗan kasuwane, dan haka yasan sirrin kasuwanci sosai, Ahmad yana yawan ankarar da Daula akan ya kiyayi Bulama, amma se Nasir yace ai Bulama ya zamani na zama shi, rabuwarmu abune me wahalar gaske.
Bulama ya kunno musu wata rigima akan harkar kasuwancin da suke, ya shiga ya fita seda yasa Daula da Ahmad sukayi baran baran suka rabu, ya zamana shine ma gaban Nasir.
Watan cikin Huda tara cif ta haifo sankaceciyar jariryarta mace, Daula ya rasa inda zesa ransa dan murna, sedai haihuwar ta fama musu mutuwar mutanen da suka taka mahimmiyar rawa a rayuwar su, yau gashi kamar yadda Nadiya ke fata, Nasir ya amsa sunan Daula, ga rabo sun samu, amma babu ɗaya a mutanen nan daze taya su farinciki.
Haihuwar jaririyar nan tasa sun zubda hawaye, har damuwa taso ta maye gurbin farincikin da suke ciki, wani abun mamaki jaririyar nan ta ɗakko kamanin Islam Yayar Huda, dukda Huda da Islam suna kama sosai, amma kamanin Jaririyar nan sunfi karkata ga Islam.
Huda tana zaune rungume da jaririyar nan tace "Duk wanda yake ƙaunata, ya ƙaunaci jaririyar nan, duk wanda yaƙi jaririyar nan to tabbas ni yaƙi, a duniya yanzu banda Allah, se mijina da wannan 'yar, su kaɗai Allah ya mallakamin, inajin son' yar nan a raina, kamar yadda nake son mahaifinta, Allah yasa ta zamo me jinƙi da tausayi kamar mahaifinta "
Nasir ya rungume Huda da jaririyarsu yace" tabbas nima duk me sona, to ya ƙaunaci Huda da jaririyar nan, Allah yasa mun ƙara yawa, ya azurtamu ta samun ƙaruwa, yanzu wani suna kike ganin zamu saka mata? Ko mu mayaf da Sunan Anty Islam '
Girgiza masa kai Huda tayi tace "A' a idan ka mayar min da sunan Islam, bazan iya tsawatar mata ba, kamaninta ɗaya da Islam zan dinga ganin kamad itace, haka idan ka samun sunan Anty Nadiya, nan ma bazan iya tsawatar mata ba, saboda ina girmama Anty Nadiya, tambarin mutjwarsu baze taɓa barin zuciya ta ba, gara mu sa kamata wani sunan daban, mu sama ta Widad, wato soyayya da Abota, na zaɓi sunan ne saboda yana da kyakkyawar ma'ana, Ina sonta kuma itace babbar ƙawata"
Nasir yayi murmushi yace "muna sonta dai'
Haka akayi gagarumin shagalin suna, a Nigeria, nan dangin mahaifin su Nasir suka dinga rige rigen zuwa, saboda Arziki ya samu, Bulama ya taya Nasir murnar haihuwar Widad sosai, duk da saɓanin da suka samu da Ahmad, seda yazo yayiwa Nasir barka, ya bawa Widad kyaututtuka, Bulama ne ya saiwa Widad Haikika, yayi Ƙaton Akwati da kayan jarirai, haka nan yaji yana ƙaunar yarinyar, sanadin abunda yayiwa Widad, yasa mafi yawa na ƙiyayyar da Huda ke masa ta ragu, dan taji haushin rabuwar Nasir da Ahmad, abunka da abun masu Arziki da neman gurin zama, nan masu kuɗi suka dinga bajinta suna gwangwaje jaririyar nan da manyan kyautuka, dan kawai su birge Daula, ko ace wane ya bada kaza.
Kafin su koma Dubai, kusan kullum se Bulama da matarsa sunzo, dan ya ɗauki Widad, ko kuka take ya dinga rarrashinta kenan, Yana matuƙar son yarinyar.
Kwanansu Arba'in Nasir ya ɗauke Huda suka koma, Bulama ma albarkacin Nasir ya fara kama ƙasa, nan da nan ya shiga aure Auren mata, ya auri wannan ya saki, ya Auri waccan ya kora, tun Nasir yana masa faɗa harya ƙyaleshi.
Kadarorin da Aka tarawa Widad na suna, Daula ya haɗa ya siyar bisa shawarar Huda, suka haɗa kuɗi suka buɗe kamfanin sarrafa ƙarafa, manyan mutane har daga ƙasashen ƙetare suka zuba hannayen jarinsu cikin kasuwancin, nan fa Sunan Daula ya ƙara shahara, ya zama babban attajiri, me sana'a goma maganin me gasa.
Widad ta fara wayo a hankali tana girma, ta isa shiga makaranta se Daula ya koma England, saboda mafi akasari yanzu yafi ta'amalli dasu akan harkar kasuwancin motoci, aka saka Widad a makaranta, Huda kuma ta dage da koyar da ita na Addini, dukda akwai wani ustaz dayake koyar da yaran musulmai a ƙasar.
Sedai gaba ɗaya rayuwar Widad da girmanta, ya sha ban ban dana sauran yara, sun raba gari da duk wasu ɗabi'u na yara, duk inda yaro yake an sanshi da son kallon fina finan cartoon, kona dabbobi amma banda Widad, idan za tayi kallon film, daga wrestling, se film wanda ake yaƙe yaƙe ko harbe harben bindiga, kokuma fina finan horo na ban tsoro, kona harkar fashi, suke birgeta, sam bata kallon wani film ɗin Indiya ko soyayya da tausayi, basa gabanta, Huda taita fada tana mita, amma Nasir se yace ta ƙyaleta, nan gaba zata dena.
Huda taita mita tace "yarinya kamar ba mutum ba, ke duk abunda mutane suke yi ko suke so, ke kunyi hannun riga dashi?"
Widad tana da miskilanci, bata magana seta ga dama, idan har kaji ta zage tana surutu, kodai da mahaifintane ko kuma Bulama ne ya kawo musu ziyara, bata wasa da 'yan uwanta yara, sedai taita gwada tsalle tsalle, da harbin bindiga da take gani a film, shine wasanta sosai abun yake damun Huda, Nasir yace tayi haƙuri irin tata ƙuruciyar kenan.
Widad tafi sakewa Da Babanta akan Amminta wato Huda, Huda tana da zafi sosai akan tarbiyyar Widad, yayinda Babanta duk abunda takeso shi yake so, amma duk da haka akwai soyayya da shaƙuwa a tsakanin Widad da Amminta, babban abunda yake haɗasu shine rashin son mutanen Widad da kuma wannan kallon da take yi.
Widad ko ƙawayen kirki bata da su, saboda rashin son maganar ta, sedai tana ji da magenta, tana nuna musu soyayya, sune abokan wasanta, dasu take hirarta.
Tun bayan haihuwar Widad me abun mamaki, Huda bata sake samun haihuwa ba, tana ta Addu'a tana fatan ubangiji Allah yasa ta kuma samun rabo.
A wannan lokacin shaharar Daula ta wuce iya Nigeria, da taimakon Allah Daula ya goyawa Musa baya da maƙudan kuɗaɗe, ya tsaya takara a wata jam'iyar siyayasa a wannan lokacin, a dalilin son da mutane suke wa Nasir Daula suka zaɓi Musa.
Tunda Musa yaci zaɓe nan ya ɓarke da bushasha, bashi da aiki se gantalin ƙasashen duniya, ya manta da al'ummar da suka zaɓeshi, da irin Alƙwarirukan daya ɗaukarwa mutane, Ya kai 'yarsa Nurat makaranta a ƙasar waje, inda Widad take karatu, Nurat tana matuƙar son Widad, Kasancewar Widad ce bahaushiya' yar uwatta a makarantar, duk sauran yaran turawa ne, tun Widad bata damuwa da Nurat harta fara kulata, a hankali suka fara sabawa