Showing 51001 words to 54000 words out of 209297 words
suna da daɗi Sosai, dan bana missing chocolates da ice cream yanzu tunda ina cin waɗan nan"
Suka cigaba da hira, ba tare da sun yi faɗan da suka saba ba, bayan sun kammala Yusuf ya gyara gurin, yaje yayi wanka sannan itama ta ɗau bokiti taje ta karɓi ruwan wanka, Hari taita mita wai zuwa yanzu yaci ace Widad tana wanka da ruwan sanyi, amma dan gajeren fi'ili kullum se an bata ruwan ɗumi.
Widad bata saurareta ba ta tafi wankanta, bayan ta fito ta shiga ɗaki, ta ajiye bokitin ta nufi shimfiɗar ta domin sa kaya, tana hasakawa da fitila taga Yusuf kwance akan katifarta, daga shi se gajeren wando, ya lumshe ido da alama bacci nema ya ɗauke shi, da farko seda ta firgita ganin sankacecen mutum dogo kwance a gurin, daga baya kuma taga Yusuf ne.
Ƙafarsa ta haska taga ciwon da yaji yana warkewa a hankali, sannan ta hasak jikinsa, tun daga kansa har fuskarsa zuwa ƙirjinsa da ƙafafunsa, lulkuɓe suje da dogayen gashi.
Inda akwatinta suke a gefen Yusuf ne, gashi ya kwanta a gurin, kuma bata son ta tasheshi dan da alama a gajiye yake, ta zarwle hijjabin jikin ta ta shanya saboda a jiƙe yake da ruwan wanka, tazo ta zauna kusa da Yusuf tana son ta ɗakko Akwatin, amma se taga kamar ze tashi, ta ɗan ƙura masa ido, duk ya rame se dogon hancinsa da yake tsaye kyam, ga ƙasumba data fara fito masa wadda da bashi da ita (kasancwarsa jam'in tsaro, basa tara gemu) .
A hankali hannunta yana rawa, ta kai hannunta kan sajensa, wanda yake a kwance kamar na Fulani, a hankali ta dinga shafa gashin ta gangaro har ƙirjinsa inda gashin yafi yawa, ta dinga wasa da gashin a hankali, tana yi tana zancen zuci, yunƙurawa tayi zata ɗauke hannunta taji ya riƙe hannunta, zaro ido tayi a firgice tace "dama idonka biyu?"
Gaba ɗaya ya janyo ta jikinsa, ya kwantar da ita akan katifar, yace "me kike yi ne tun ɗazu? Duk abunda kike ina jinki fa"
Haɗe rai tayi tace "ɗagani Malam, wai baka san kana da nauyi bane?"
"Ya za'ayi in sani, kin zauna tun ɗazu se taɓani kike"
"jika wai se taɓaka nake, me zan taɓa wannan gashin daka tara duk abun ƙyama ma, abun amai shine ɗin zan taɓa, ni cikani in sa kaya, kar towel ɗina ya cire"
Dariya yayi, ya haska fuskarta da fitila yace "meye abun ƙyamar? Gashin jikin nawane abun ƙyama ko kume me?"
Rufe idonta tayi tana tura baki, ya kama hannuta ya ɗora akan Ƙirjinsa, yace "da abun ƙyamane dabe burgeki kin taɓa ba"
Tace "meye abun burgewa anan, sakarmin hannuna ko in tsige gashin nan ɗaya bayan ɗaya"
"gaki na gashi ai, yi yadda kike so dashi my Queen naki ne ai"
"Sarkin daɗin baki, da zakayi politics se an zaɓeka saboda wannan daɗin bakin naka"
A kunnenta yace "ko banyi politics ba, dama ban iyaba amma ina fatan ki zaɓeni a matsayin abokin rayuwarki Weeeedaat, ina sonki masoyiyya ta, na taɓa soyayya a baya amma yanzu nake gane a baya shirme nayi, yanzu ne nake Soyayya, saboda ban san takamaimai a ina nake jin sonki a cikin zuciya ta ba"
Shiru tayi ta ƙanƙame Yusuf tana saurare kalaman da yake gayamata, sedai tun ba'aje ko ina ba, al'amarin ya fara canza salo zuwa wani abu daban, da fari kamar Widad zata dake daga baya kuma tace bata san zance ba, ta tubure masa gaba ɗaya, but Yusuf he shows her the superiority of a Man.
Tashi tayi zaune, ta janyo bargo ta rufe jikinta, tana neman towel ɗinta, yana daga kwance ya kai hannu ze taɓa ta Amma ta bige hnnunsa, tana ta faman zumɓura baki, zaune ya tashi shima zeyi magana, amma ta fashe da kuka.
yace "Am sorry please, dan Allah kiyi haƙuri, is not intentionally kuskurene mun riga munyi shi sedai.. "
Katseshi tayi ta hanyar cewa "eh dama is not intentionally mana, tunda maye kake, kullum haka kake cemin is wasn't intentionally kuma bayan kana sane, kuma karka sake cewa munyi kuskure kayi dai"
Yusuf yace "jimin mara kunya, amma ina kwance kika zo inda nake ai"
"kazo inda nake dai, waye yace kazo ka kwantamin akan katifata?"
"Amma dana kwanta akan katifarki, shine akace ki zauna kina taɓani?"
Rasa me zata ce tayi, kawai ta fashe da kuka Yusuf ya lura kukan Shagwaɓa ne kawai takeji, amma yace "shikenan am sorry, ya isa haka kukan, ba zata sake faruwa ba, semu kiyaye gaba"
Ƙwacewa tayi daga jikinsa tace "ka kiyaye gaba dai, kawai nayi wanka na zan kwanta, kawai ka ɓatamin"
Ta cigaba da ƙunƙuninta, ta miƙe ta sake zura hijjabi tayi waje, yayin da Yusuf ya koma ya kwanta yana murmushi, dan shi wasu lokutan wannan rigimar tata birge shi take.
Taje bakin rumfar da ake girki ta tsaya daga baya, Hari tayi daren Abinci tana ta tankaɗe zata tuƙa tuwo, Widad tace "a zubamun ruwa zan wanka"
Ta ɗago ta kalli Widad tace "sannu Agwagwa, ko kuma ince tarwaɗa sarkin wanka, ba ɗazu Yaya ta zuba miki ruwan kikayi wanka ba?"
"Eh wani zan kumayi" Widad ta bata amsa
"waike sau nawa kike wanka a rana ne? Ke ko ɗan tsallaken nan bakya yi, kullum se kinyi wanka, ni a rana ma bansan sau nawa kike wankan ba, kuma yanzu ko Awa biyu ba'ayi da wankan naki ba kin kuma ɗakko bokiti kin dawo"
Widad tace "Allah ya kiyaye inyi fashin wanka, an gayamiki kowa irinki ne? Kawai mutum ya zauna be wanka ba har ya kwana ya tashi, ni ki zubamin dan Allah"
Hari tace "ko dame kike yawo bazan baki ruwan nan ba, wannan wane irin wanka ne sekace me iskokai?"
"Zaki zubamin ruwan ko sena gayamiki abunda yasa zan kuma wankan?"
"Ina ruwana da abunda yasa zaki sake wanka, keta shafa mace sekace wata kifi kullum cikin ta'annati da ruwa, ba dare ba rana, haba ni matsa ki bani guri"
"Hari za'aji kanmu dake a daren nan fa, kin fiye samun ido da shisshigi gaskiya, zuciya ta na gaya min in faɗi wani abu"
Hari tace "aike in mutum ya biye miki yana tsaye ze bar musulunci seya sake wankan shiga musulunci"
Widad ta nemi guri ta zauna a tsakar gidan, Hari ta tashi taje ɗaki ɗakko abu, dukda Widad bata san hayaƙi haka ta toshe hanci, taje gaban murhun ta ɗebi ruwanta ta ƙara gaba.
Hari na fitowa taga Widad ta kwashe ruwa fiye da rabi, nan ta tsaya ta dinga zazzaga masifa, Widad ta fito ko takanta bata bi ba tai wucewarta ɗakinsu.
Gwaggo ce taita bawa Hari haƙuri, saboda yadda ta wage maƙogoro tana ta zazzaga bala'i a daren nan, kuma Widad ta shareta tana ta surutu.
Wani daddaɗan bacci ne yayi awon gaba da Yusuf, dan duk neman maganar data fita tayi be sani ba, kallonsa tayi taga baccinsa ma yake yi.
"Tasarmin daga kan katifa, zan saka kaya in kwanta" tai maganar tana dukan filon da yake kai, a hankali ya motsa, ba tare da yace komai ba ya miƙe ya bata guri, shima ya fita dan yin wankan, ba tare da yasan me Widad ɗin taje ta aikata ba.
Umman Yusuf tana zaune tana lazimi, ta kunna radio, dan gaba ɗaya ji take duniyar ta mata faɗi saboda rashin Yusuf a gidan, ba ta jin daɗin komai, ji take ta rasa wani sashi me girma, Tana ta laziminta hankalinta ya ɗauke, jin an ambaci cikakken Sunan Yusuf a radio yasa ta dawo daga tunanin da take yi, ta maida hankalinta kan radion ta ɗakkota ta ƙaro sautin.
Rahoton da aka faɗane na bincike ya tabattar da Yusuf ne yai garkuwa da Widad dan ya karɓi kuɗin fansa yasa tayi jifa da radion a gigice, jikinta ya hau rawa, take ta fashe da kuka tana girgiza kai, cikin kuka tace
"baze yuwu ba, Yusuf ɗina ba haka yake ba, ni ɗana baze taɓa aikata wannan mummunan aikin ba, innalillahi wa inna ialaihi raji'un, wayyo Allah ɗana, wayyo Yusuf aikin ɗan sand be maka rana ba, wannan aiki da kayi yayi silar rushewar farincikinmh, yau nayi baƙinciki fiye da wanda muka rayu a ciki ni da kai, wayyo Allah ɗana, Allah ka kuɓutarmin da Yusuf "
Sosai take kuka, kamar zata shiɗe haka tayi zaman daɓaro tana ta rusa uban kuka babu me rarrashinta, gwanin ban tausayi.
Amal idanunta har sun kumbura saboda kukan da tayi, Hajiya Halima ta shigo ɗakin ta tarar da ita tace " Haba Autan Mummy, kukan ne har yanzu baki dena ba, haba Amal ɗina"
Tai maganar tana rungume Amal a jikinta, ta cigaba da cewa "haba Amal, meye abun kuka, dan Allah ki cire yaron nan daga ranki, kinfi son Asirin Mummy ya tonu a idon duniya? Kin san bani kaɗai ba har ku ta shafa, duk fafatukar nan da nake danku nake yi"
Amal tace "Mummy, nasani amma abun yayi yawane, haba Mummy ki duba lamarin nan fa ki gani, Abunda akayiwa Yusuf yayi yawa Mummy"
Hajiya Halima tace "ke bafa sharri akayi masa ba, tunda akace ya gudu daga hannun wancan mutanen meyasa basu dawo ba? Kina ta kuka akansa, shi kuma ba kya gabansa sam, kina kallon yadda ya dinga yanƙwanaki, yana wulaƙantaki shida waccan fitsararriyar mara mutuncin, suka dinga wulaƙantaki bama ke kaɗaiba harni ba kunya ba tsoron Allah suka dinga cin mutuncinmu, dan haka meye a ciki dan suma an musu? Ki dena kukan nan kinji, ki share hawayenki, danku nake wannan faɗi tashin, ki dena kuka kina ɗagamin hankali kinji"
Amal ta jinjina kai, tana share hawayen Fuskarta.
Haka nan Yusuf yaji jikinsa yayi sanyi, kamar wani abu yana faruwa, jiki a sanyaye yaje yayi wanka ya dawo ɗaki, Hari tana ganin ya shiga banɗaki da bokiti tace
"la'ilahaillalah, ta tabatta Wudas bata da kunya yarinyar nan, innalillahi kai Allah yayi mana maganin wannan zamani, Taɓɗijan ashe abunda yasa ba yau gobe cikin sintirin banɗaki take yin wanka, to Allah ya maganta"
Babban abun takaicin, Hari ba a hankali take magana ba, Yusuf ji yayi kamar karya fito daga banɗakin nan saboda nauyin maganganun Hari, a matuƙar kunyace ya fito ya wuce ɗakinsu, Widad ta lura kamar jikin Yusuf a sanyaye yake, kamar wani abu yana damunsa.
Yazo ze ɗauki kayan shimfiɗarsa, yaji ta kira sunansa "Yoseef"
Ya amsa da "Na'am"
Widad ta tashi zaune tace "meyafaru ne?"
"Me kika gani?"
"Naga kamar kana da damuwa ne, wani abu yana damunka"
Murmushi yayi yace "bakomai, yi kwanciyarki kawai"
"Yoseef" ta kuma kiran sunansa
Ya sake amsa mata kamar ɗazu.
"Dan Allah ka gayamin abunda yake damunka, zaka sani a damuwa fa"
Yaji daɗi a ransa, da yaga ta damu da damuwarsa, "kece kike ganin wani abu yana damuna, ni lafiya ƙalau nake"
Harya juya ze tafi inda yake kwanciya, yaji ta riƙe rigarsa, tsayawa yayi ya juyo yaga ta zuba masa ido.
Zama yayi akan katifar yace "ya akayi kuma?"
"Yoseef, ba yau nafara ganinka ba, ina gane fushinka ko damuwa, just recently kake walawala, suddenly kuma mood ɗinka ya canza, me nayi maka?"
"Ni ba abunda kikamin banda bani joy da happiness i ever expected to get"
Yai maganar yana jan hancinta, "kana son ka koma gida ko? Nima na damu mu koma dukda ina jin daɗin zaman gurin yanzu, amma ina kewar Daddy sosai"
Gyara zamansa yayi yace "Dole ne muyi kewar iyayenmu da masoya Widad, kasancewar ƙaddararki na kamanceceniya da tawa, sedai sun sha banban, Akwai dalilin da yasa Allah ya haɗamu a nan, se mucigaba da haƙuri muga hukuncin da Allah zeyi, amma ni ba abunda kika yi min kinji masoyiyya, ni farinciki kika bani ma, wanda baze taɓa gogewa a zuciyata ba, I love you so much Baby "
Yai maganar yana rungumeta, ba tace komai ba se murmushi da tayi, Yusuf yana daga cikin mutanen da bazata manta dasu ba a rayuwarta, dan Ya canza mata gurɓataccen tunaninta, yayi sadaukarwar da bata taɓa tunanin wani zeyi akanta ba, yana haƙuri da dukkan halinta me kyau ko akasin haka.
Ya nisa yace "bari in baki guri ki kwanta, nasan lokacin baccinki yayi"
Dukda a cikin duhu ne, amma ta niƙe kafaɗa tace "mu kwana anan tare mana"
Murmushi yayi yai ƙasa da muryarsa dai dai kunnenta yace "haka kawai inje wani abu yafaru, kiyi ta haɗemin rai kina hararata, yanzu ma ban san yadda akayi ba naga an ƙyaleni, dukda haka ban fidda ran da safe inga an ɗauremin fuska ba"
"Kai kuma abunda ke ranka kenan, nidai mu kwana tare kawai"
Yusuf ya gyara kwanciyarsa yace "as you wish your majesty, ni dama haka nakeso, saboda hakan yana ƙara danƙon soyayya a tsakanin ma'aurata"
Bata kula shi ba, sedai sake shigewa da tayi jikinsa sosai tana lumshe ido.
Yusuf yace "Babyna, baki ƙarasamun labarin nan bafa"
"shhh, lokacin bacci yayi kayi bacci kawai, bana son in ƙara maka damuwa"
"wai waye yace miki ina cikin damuwa ne?"
"Hmm Yoseef kenan, tunda kaƙi yadda ai shikenan"
Haka suka wanzu a haka, bacci ya ɗauke Widad yayin da Yusuf ya kasa samun nutsuwa, yana sake ji a jikinsa akwai wani abu mara daɗi dake faruwa a wani guri, wanda hakan ya shafeshi ko kuma ya shafi Widad.
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
74_75
Yadda Uman Yusuf taga rana haka taga dare, gaba ɗaya ta rasa wanda zata kira ta gayawa halin da take ciki, unguwarsu kuwa tuni labari ya cikata, akan ga abunda Yusuf ya aikata, beji ba be gani ba an ɗaura masa mugun sharri, wasu suna ƙaryene, wasu suna ba'a shedar mutum.
Mata suka dinga shiga da nufin suyi mata jaje, hadda wanda tun ɓatan Yusuf basu yi mata jaje ba, se yanzu da wannan labarin ya fasu.
Saleh ne a office ɗin Suleiman, ya kai gwauro ya kai mari, ya kalli Suleiman yace "ni gaba ɗaya kaina ya rufe ruf, na rasa me yakamata inyi, gaba ɗaya mutanen nan sun shammaceni, banyi zaton ta nan zasu ɓullo ba, duk yadda nake tunanin zaluncinsu sun wuce nan, na rasa mema zanyi ko me zance"
Suleiman dake zaune akan kujera yai shiru, ya nisa ya ɗago daga jinginar da yayi yace "ni kaina bansan me zan iyayi ba, naje na samu Sp amma yaƙi saurarata, wai sakamakon da aka bashi shiya sanar, nabi duk nayi ƙoƙarin da zan iya, na tuntuɓi masu ruwa da tsaki akan abun, amma kowa ya nunamin ba ruwansa, ma'aikatan gidan nan gaba ɗaya hankalin mu a tashe yake, kuma nasan muddin mukayi wani yunƙuri, to muma baza'a barmu ba, zasu ɗau mataki akanmu ne, amma yanzu meye abunyi? "
Saleh yace " Abunyi be wuce inje in ƙara tabattar da na toshe duk wata kafa, wadda zata sa a gane inda suke ba, sannan in ja masa kunne da wannan uwar taurin kan yarinyar, akan duk tsanani karsu sake su bar gurin nan, idan har bani ne naje nace su baro gurin ba"
Suleiman yace "gaskiya, ka gaggauta zuwa ka same su kam, sannan ni gaba ɗaya kunyar mahaifiyar Yusuf nake ji, ban san me zance mata akan wannan al'amarin ba, ni nake bata ƙwarin gwiwa akan ɓatan nan nasa, akazo kazo da labarin sun kuɓuta, amma still hankakinta a tashe yake, ban san ya zata yi ba idan ta samu wannan Mummunan labarin "
Saleh yace " dole zata damu sosai, Amma haka nan za'ayi ƙoƙari a kwantar mata da hankali, dan barinta haka babu me rareshinta shima wata babbar matsala ne"
Suleiman yace "hakane, ubangiji Allah ya shiga lamarin bayinsa, bari in tashi insha Allah zanje in gaisheta, a sake bata haƙuri da kwantar mata da hankali"
Daren Yau kusan kwana su Alhaji Haruna sukayi suna meeting, sunyi farincikin da jin mafitar da Bukar ya samo musu, dan ba suyi zaton irin wannan mafitar ze kawo musu ba, dan haka yanzu kallo ze koma ga sauraren 'yan sanda aga ta inda zasu fara kamo Yusuf.
Alhaji Musa yace "yanzu idan aka gano su, yaya zamuyi da wannan shu' umar yarinyar me jarababben taurin kan bala'i"
Alhaji Munir yace "kai dai bari, yau shekaru kusan goma muna bibiyar abun nan, amma 'yar masu baƙin halin yarinyar nan ta hana, ba abun mu kashe ta ba kuma muzo muyi biyu babu"
Alhaji Haruna yace "idan muka kashe ta ai kuma zamu tashi a tutar babu ne gaba ɗaya, ya zamana duk wannan wahalar ta tashi a banza, ai yadda naji Bukar yace, shi wannan ɗan sandan yaron da an kamosu shi zamu fara kawarwa, saboda Kasancewar sa tare da ita matsala ne a gare mu, idan aka kauda shi, itakuma tunda babu wanda yasan inda ubanta yake, zamuyi poisoning ɗinta ne, a fita da ita waje neman lafiya, idan yaso kodai ta faɗi inda suke kokuma a aikata"
Alhaji Munir yace "Amma fa kun san rashin sanin inda Daula yake, itama wata babbar barazana ce me zaman kanta, muna ruwa fa idan Daula ya bayyana bamu samu abun nan ba, yakamata ace mun san inda yake a hallaka shi tunda wuri"
Alhaji Musa yace "Ai ana nan kan bincike, an duƙufa sosai gurin gano inda yake, kuma akwai alamun nasara, sannan idan aka gano shi kasheshi kawai za'ayi, karma a ɓata lokaci, tunda dama an bada sanarwar duk wannan yaron shine yayi garkuwa dasu"
Alhaji Haruna yace "nifa a gurin nan kamar anyi wauta, in ba hakaba ta yaya za'ace waishi ne ya sace Daula, duk tsaron dake Asibitin nan"
Alhaji Musa yace "nima da nayi wannan tunanin, amma Bukar yace ya san abunda yasa yayi hakan, ni wai ya maganar wannan yaron da