Showing 144001 words to 147000 words out of 209297 words
ze shafa muku ciwo, dan yana ta'amalli da mata a guest house ɗinsa, idan kin musa ina da sheda, zan iya turomiki idan kina da buƙata"
Wani gumine ya fara tstatsafo masa, ya dake yace "wannan wane irin shirme ne za'a turomiki ki yadda, kawai a turomiki magana ki yadda, wataƙila ma bake za'a turowa ba"
"ɗan saurara karka rainamin hankali mana, idan ƙarya ake maka saƙon ya rasa wayar waze faɗo se tawa? Kuma yawan fitar cikin dare da kake wataran bako sallama ina kake zuwa?"
"wannan kuma harkar aikine ke fitar dani"
"harkar banza dai, wans irin aiakine baza'ayi shi da rana ido na ganin ido ba se a takatainin dare, wallahi kaji tsoron Allah, kome kake aikatawa Allah yana kallonka, kuma wallahi idan na tabattar da abunda naake zargi seka sakeni wallahi, kuma sena tona maka Asiri a idon duniya, bani wayata ni"
Ta saka hannu ta ɗauke wayarta, tai waje ranta a matuƙar ɓace, ya dafe jansa kallai wanna kafon ya ɗebo ruwan dafa kansa, ga ya haɗu da mskira 'yar damfara.
Kiran Bukar ne ya shigo wayarasa, jiki na rawa ya ɗaga suka gaisa yace "Haruna na gaji da wannan zagaye zagaye da raini hankamin da kakemin, ka fito ka gayamin gaskiya mske faruwa, ina takaddar nan take? Idan kuma wata manufar ce da kai kuma seka ajiye agurinka"
Alhaji Haruna yace "Babu yadda za'ayi takaddar nana tana gurina inƙi kawowa, wata 'yara matsala aka samune, kuma ba da daɗewa ba zan warwarwta a ɗan ƙara ɗagamin ƙafa"
"Bana alfarma a karo biyu, daga ta farko bana ta biyu, Amma ka sani daga wannan shikenan, idan wani ya samu takaddar nan Asirinmu ya tonu, ze zama hujja akanmu, gara idan ɓataraa kayi ka nemota tun wuri, idan kuma ɓoyewa kayi kaje ka cigaba da ajiyar ta karka fito da ita "
Ya kashe wayar, Alhaji Haruna ya rasa abunda zeyi, aka kuma kiransa da ovt number, kamar kar ya ɗaga amma ya ɗaga," ɗan duba what's app ɗinka akwai saƙo"
Be ɗauki muryara waye ba, amma dai muraya mr mace ce, ya kunna data ya shiga what's app ɗinsa, messages suka gama shigowa sannan ya shiga dubawa.
Video ɗin tsiraicinsa ne da wata wadda besan kowacce ba a guest house ɗinsa, daga ƙasa aka rubuta "dukda wannan abubuwan da na maka banji na fanshi mutuncina daka keta ba, wallahi idan baka biniba sannu ba sena yaɗawa duniya, kuma yanzu a haka akwai video ɗin nan a wayar mutum huɗu, isan har wani abu ya faru dani zasu watsa a duniya"
Ko ba'a gayamasa ba yasan message ɗin Amal ne, yace "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, be taɓa gamuwa da masifa a rayuwar sa irin wannan ba, ya ɗebo ruwan dafa kansa over.
Widad kam seda gari ya waye yayi haske sannan tai alwala ta fito tayi sallar Asuba, ta dinga kai kukanta ga Allah, kuka kama dama ya zame mata jiki, dan inda sabo ta riga ta gama sabawa.
Tana cikin kukan ne Sabuwa ta shigo mata da abun karyawa, Widad ta kalleta tace "yanzu dan Allah jiya baki ji ihuna ba cikin dare?"
Sabuwa tace "idan nace vamji ba nayi ƙarya, sedai kona fito ba abunda zan iya yi miki, saboda Kinsan nima aiki aka ɗaukeni inyi, idan na shiga hurumin da ba nawa ba, zasu kasheni ne, seda akamin wannan sharaɗin sannan na fara aikin kula dake ɗin nan"
Widad ta jinjina kai tace "ɗauke wannan Abincin bana ci"
"Saboda me?"
Widad tace "kawai bana ci"
Haka Sabuwa ta kwashe kayan Abincin nan ta fita dasu.
Widad tana nan zaune sega Bulama ya shigo ɗakinta, shida wasu ƙarti su biyu, aka kawo masa kujera aka ajiye, ya hau kai ya zauna ya kalli Widad yace "karo na ƙarshe, ki gayamin inda takaddun nan suke"
Widad ta kalle shi tace "gargaɗi na farko kuma na ƙarshe, ka jawa ɗanka kunne, idan ya sake zuwa inda nake, wallahi sena kasheshi har lahira"
"ina miki magana kina gayamin wani shirme daban? Ki kasheshi ɗin karki fasa, ina takaddu suke su nake tambayar ki"
"Na miƙasu ga masu shi"
Bulama yace "zan azabtar dake, azaba irin wadda ba'a taɓa yi miki ba, ina suke?"
"Duk Azabarka a duniya ne kawai, kuma babu wanda yake da ikon yin azaba se Allah, na gaya maka na bawa masu dukiyar nan dukiyarsu, ka ƙyaleni ka rabu da rayuwata haka"
Bece mata uffan ba, taga na jona wani abu a jikin socket, an miƙawa Bulama ya karɓi abun yayo kanta gadan gadan, bata motsaba ta tsaya tana kallonsa, kawai ya jona mata abun a hannunta, ji tayi kamar ba a duniya take ba, ta rasa meke mata daɗi gaba ɗaya ta fita hayyacinta.
"zaki faɗa ko bzaki faɗa ba?"
Girgiza kai ta dingayi tana kuka, amma taƙi magana, yasa ƙafa ya take yatsunta yana murzawa ciki mugunta, amma dayake Indai taurin kaine Widad ta iya shi taƙi magana.
Ba azabtarwar da basu mata ba amma taƙi faɗa, haka suka gaji Bulama ji yake kamar yasa wuƙa ya yanka ta, amma yaga idan ya kashe ta beyi Achieving komai ba, haka suka tashi suka fita, suka barta a galabaice.
sedai fitar sa babu daɗewa wani irin ciwon kai ya kama Widad, ko iya gani ba tayi sosai, ga ƙirjinfa daya riƙe gam, nan ta kwanta tun tana kwnace, harta fara juyi ya zamana bata iya ganin komai, se dishi dishi daga baya kuma ta dena gani gaba ɗaya.
Daga nana bata sake farkawa ba se a gadon Asibiti, taji anayiwa Bulama bayanin zuciyartace ta kumbura kuma ga jininta ya hau, Ba tausayi ba imani Bualama yayiwa doctor Hamisu umarnin ya cire ɗan cikin Widad koda tsiya ne.
Ta buɗe idonta fes a kansu, amma hakan besa Bulama yai shiru ba, ya bada umarnin a cire cikin.
Haka doctor Hamisu yaje ya ɗakko allurai, yazo ya haɗasu yayi mata duk tana kallonsa, sedai ta kasa motsa koda ɗan yatsanta ne, gaba ɗaya tama rasa inane yake mata ciwo, haka ya kwance cannula yai mata wata allura, sannan yasa wata a ruwa, ya gama ya fice tana kallonsa.
Sosai Yusuf yake jinsa a damuwa, hankalinsa yaƙi kwanciya sam, yake jin jikinsa ba daɗi, tunanin Widad ya cika masa zuciya.
"To wai kai Haruna ya akayi ka bari haka ta farune? Ta yaya yarinya ƙarama zata dinga wasa da hankalinka haka?"
Alhaji Haruna yace "kai dai bari kawai Alhaji Musa, wallahi nikaina ban san abun ze kai haka ba, ganin irin kuɗaɗen dana bata, ni nama rasa abunyi wallahi, babban abun tsorona shine video na data ɗauka, karta saki a duniya mutuncina ya zube"
Alhaji Musa yace "rabu da ita, duka barazanar banzace ba zata saki ba ƙarya take"
"Ya zakace ƙarya take? Bayan har Salma ta turawa message a kaina?"
"ni nace maka ka ƙyaleta ai, to ka ƙyaleta ba zata iya yaɗawa ba, sannan batun takadda ka gayawa Bulama gaskiya kawai, ai da tun farko ka faɗa masa ma da tuni an wuce gurin, ƙilma yai maka maganinta"
Alhaji Haruna dai yai ajiyar zuciya yai shiru kawai.
Bacci ne ya ɗauki Widad me nauyi, sedai wani irin gigitaccen ciwon mara yasa ta farka babu shiri, ji tayi wani irin ciwo yana ratsata, tun daga mararta zuwa bayanta da ƙafafuwanta, wani irin ƙarfine yazo mata, ta zabura ta fizge cannula, aikuwa take jini ya shiga zuba daga inda ta cire cannulan.
Ta faɗo daga kan gadon, Nurses ne suka shigo da sauri, suka ga yadda Widad ta faɗo ƙasa, ta riƙe mararta hawaye na zuba daga idonta, alamar tana jin jiki, ɗayar ta kalli ɗaya tace "Sister, ki kira likita da sauri yazo ya dubata"
Tace "shikenan bari inje"
Tana zuwa ta sami doctor Hamisu a Office tace "doctor, patient ɗin Alhaji Bulama ta Amenity she's unconscious fa, harta faɗo daga kan gadon"
"Ku kaita labor room kuyi mata abunda yakamata, Abortion ne cikin jikintane ze faɗi"
"doctor, amma naga kaman ba case ɗin Abotion aka kawota ba, cardiac failure ne, da hypertension kawai, ya za'ayi within a minutes ace kuma Abotion yai occurring"
"Are you going to teach me my job? Wace makarantar kika yi ne, baki san cardiac failure na uwar ze iya shafar abunda ke cikinta bane? Get out from here kije kuyi abunda nace"
Jiki a saluɓe Nurse ɗin ta fita daga Office ɗin ta koma ɗakin Widad, ta tarar da ɗaya Nurse ɗin rungume da Widad tana mata sannu.
"Sister ina doctor ɗin?"
"naje yamin wulaƙanci, wai mukai ta labor room abortion ne, muyi mata abunda yakamata, shikenan babu wani taimako da za'a bata se a bari cikin ya fita?"
'haka yace miki? "
" Gashi kuwa ina gayamiki, zan masa ƙaryane? "
Widad kam banda aikin gumi babu abunda take yi, fuskar nan tayi jawur saboda azabar wahala, haka taita wannan wahalar tana addu'a tana ambaton Allah, tana roƙon Allah ya bar mata cikin nan.
Ɗayar taje ta samo wata allura a pharmacy tayi wa Widad, cikin ikon Allah se bacci ya ɗauketa, can sega doctor Hamisu ya shigo yana cewa "Yaya? Cikin ya fita dai ko?"
Ɗayar tace "ta samu relief bacci take yi"
"Ya faɗin dai ko?"
Nurse ɗin tace "Eh ya faɗi, mun gyarata ne ta samu hutu, amma babu wani wanda suka zo tare da ita ne?"
"Ba ruwan ku da wannan, tunda mun samu ya faɗi Alhamdilillah, a bata medication ɗinta na dare"
"To insha Allah, za'a bata"
Bayan fitarsa ɗaya ta kalli ɗayar tace "Sister Habiba, kijimin ikon Allah, ni anya ba doctor ne yai mata wani abuba akan cikin nan ba kuwa?"
Sister Habiba tace "ya za'ayi in sani, amma nima ina zargin hakan wallahi, Allah sarki tana murƙusus amma fatanta Allah ya bar mata cikin ta, Insha Allah be zube ba, ko akanme ze damu cikinta ya zube oho"
"Hmm kedai bari, shida wannan Bulaman dama basu fiye ƙulla abun Arziki ba, naga shiya kawota kika bibiya karuwarsa ce, ko kuma dai cutarta sukayi suke so su rabata da cikin, kin san ɗan Bulaman Fahad ya saba kawo mata nan a cire musu ciki"
Sister Safiyya tace "ai kedai bar masu kuɗin nan kawai, Allah dai ya shirya naga ta samu bacci, gashi babu kowa a gurinta, balle idan ta farka a bata Abinci"
Sister Habiba tace "ai kamar yadda kika faɗa ɗinne, kika bibiya dai ba ta hanyar Allah aka samu cikin ba, shine suke son su zubar mata ta ƙarfin tsiya"
Baiwar Allah, ita Widad sam bata san meke faruwa ba, wani galabaitaccen baccine ya ɗauketa, wanda fal yake da mafarkin Yusuf cike da bege da shauƙin son ganinsa, se kuma mafarkin daddy da take yi.
Ɓangaren Ramlah kuwa, taga kwata kwata kusan Fahad yayi dumping ɗinta aside, kwata kwata baya ta tata yanzu, dan haka ta shirya da kanta ta tafi Hotel ɗin da yake zuwa, tana zuwa kuwa ta sameshi da wata mace a ɗakin, Ranta ya ɓaci matuƙa ta dube shi tace "Lallai Fahad, ka cika tantirin butulalle, a wani postion ka ajiyeni ma tukuna?"
Fahad yai murmushi yace "postion ɗinki dai na farko, a nan ns ajiye ki, me kike tunani"
"dalla saurara, karka gayamin maganar banza mana, ban gane postion ɗina na farko ba, ina maganar Auren mu da kai?"
Fahad ya kwashe da dariya yace "haba tawan, meye muma na ɗaga jijiyoyin wuya haka? Maganar Aure tana nan mana, ki bari idan na Auri Widad kema se inzo daga baya in Aure ki"
Ta kalle shi tace "Fahad, yau wace irin giya ka Shane haka? Data gaya maka ƙarya wadda harta saka ka kalli idona kake gayamin maganar banza da iska?"
"irin wadda na saba sha ce dai, sedai ban sani ba ko nasha expired ne"
"Lallai Fahad kana wasa, baka san abunda ka aikata me ze haifar ba ko? Ds kyau wallahi ka ɗebo ruwan dafa janka in dai Ramlah ce, zakaga tsiya"
Ta juya buguzun buguzun tai waje, bata zame ko 'ina ba se ofishin Bulama, tana zuwa ta tarar yana aiki a Office, sedai tayi mamaki ganin ɗinki haka a fuskarsa, koda yake ba wannan yakawo ta ba.
Ya ɗago ya dubeta yace "Ramlah lafiya kuwa? Ya kika shigomin Office haka?"
"Kamawa tayi na shigo a haka, ina maganar ds mukayi da kai?"
"wace maganar kenan?"
"Maganar da mukayi akan wannan mutumin, da yake iƙrarim shi mahaifin mu ne, kace zaka ɗau mataki akansa, amma har yanzu bani da tabbas na ka ɗauka kokuwa?"
"Banda abunki Ramlah, nima fa ban san takamaimai inda yake zaune ba, ta yaya zan ɗaukar miki matakin? Nasa aje inda nasan shi, amma baya nan baya zama a guri ɗaya sam"
Tai tsaki sannan tace "waima ni wane irin hatsari ne dashi haka, wanda yasa Mummy ke tsoronsa?"
Bulama yace "wannan tambayar ai ita zakiyiwa bani ba, kije ki tambaye ta zata gayamiki komai"
Tai ajiyar zuciya, tare da jinjina kai tace "idan kai baka ɗau mataki ba, nika gayamin inda yake in ɗau matakin daya dace dashi mana"
"Haba Ramlah, kema kin san da nasan inda mutumin man yake aida da kaina zam ɗauksr miki mataki akansa"
Kallon Bulama kawai take, ba wai dan ta gamsu da abunda yake faɗa ba, ta suri jakarta tai waje tana ƙwafa.
Fafur Nurat ta dena fitowa ko falo, saboda karma su haɗu da mahaifinata yai mata zancen komawa ƙasar waje.
Dayake yau Weekend ne sam be fita ba, yana gida amma still bega gilmawar Nurat ba, ya tafi ɗakin matarsa ya tarar tana kwance tana chatting, yace "wai ina yarinyar nan ne? Wunin yau banga gilamawarta ba"
Ta tashi zaune tace "tana ɗakinta mana, kasan halimta wasu lokutan bata san shiga mutane, tafi son zaman kaɗaici a ɗakinta, balle kuma ka ƙwace wayoyin ta"
"Ina fatan dai tana nan tana shirin tafiya?"
"tafiya ina? Ai wannan maganar kuce kai da ita"
"kamar yaya kenan?"
"kamar yadda nake gayamaka mana, kai ds ita kukayi magana, dan haka babu ruwana ka tambaye ta idan tana shirin da kanka"
Ya jinina kai, kwanan nan yaga zam iyalin nasa sun dena tsoronsa kamar yadda suke tskronsa a baya, ya rasa dalili.
Yana shiga ɗakin Nurat, ya tarar tana tilawar Al'qur'ani mai girma, ya jira ta kai aya ta ɗago ta kalle shi, dan taga magana yake son suyi.
Yace "dama zuwa nayi in ji ko kina shirin tafiyar nan kuwa? Jirginku ze tashi jibi in Allah ya kaimu fa"
Nurat ta miƙe taje ta ajiye Al'qur'anin ta sannan tace "nifa ba inda zanje Daddy, tsawon shekaru ina maka biyayya, dukda yi maka biyayya umarnin Allah ne, amma nima kayimin adalci mana, wallahi idan na tafi karatun nan bashi zanyi ba, rayuwata kawai zanyi"
A fusace yace "ni kike gayawa haka?"
"wallahi Daddy kace sena tafi guduwa zanyi daga gidan nan, ni bana son tafiyar"
Ya ƙura mata ido na wasu mintuna, sannan yai ƙwafa ya tashi ya fita.
Widad tana gadon Asibitin nan, ko iya miƙesa ba tayi, amma a haka aka sakata a wheel chair, Aka kaita mota aka maida ita wannan gidan da ake ɓoye ta.
Haka aka maida Ita, yau s bsta wannan maganin gobe a ɗurma mata wannan Allurar, haka take ta fama ga ciwo yaƙici yaƙi cinyewa, banda izayar da Bulama ke mata akan ta bada takaddun nan.
Kwanci tashi asarar rai, Yusuf ya cika sati uku cif a gidan yari, rana ta zagayo aka koma dashi kotu domin ci gaban shari'arsa.....
IDAN KIN SAI LITTAFIN NAN KE KAƊAI KIKA SIYA, KUMA AMANACE TSAKANINA DAKU, IDAN KUKA FITAR BAKUMIN ADALCI BA, TUNDA BAMUYI DAKU ZAKU FITARMIN BA.
AYSHERCOOL
07063065680
11/23/21, 10:26 PM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
134_135
Yauma kotun a cike take maƙil da ɗan Adam, 'yan jarida kota ko' ina, ga 'yan sanda da sauran mutane domin sauraren cigaban ƙararar, seda akayi kusan shari'a uku sannan aka gabatar da ƙarar Yusuf, Barrister Sadik ya fito ya sake gabatar da kansa a gaban kotu, sannan yace ze fara gabatar da shedun su akan Yusuf.
Barrister Sadik yace "zan fara gabatarwa da kotu shedarmu ta farko akan cewar Yusuf shine yayi garkuwa da 'yar gidan Alhaji Nasir Daula"
Nan Barrister ya kira wani mutum, mutumin ya fito ya tsaya ya fuskanci kotu, Barrister ya taka gaban sa yace "ko zaka iya faɗawa kotu sunanka?"
Mutumin yace "Sunana Sada"
"Kasan wannan" yai mavanar yana nuna masa Yusuf.
Sada yace "eh nasan shi"
"Meye a tsakaninka dashi?"
Sada yace "Eh nasan shi, sunanshi Yusuf, yana kawomin gyaran motoci"
Barrister Sadik yace "yaushene ganinka na ƙarshe dashi?"
"Eh ganina dashi na ƙarshe shine, ranar daya kawomin wata mota yace in siya, nace masa gaskiya ni bana siyan mota sedai zan haɗashi da masu saida mota, bayan na haɗashi dasu se aka kawon lambar motar da na kawo maka, wadda ta kasance lambar motocin gidan Daula ne "
Aikuwa aka kawo lambar mota aka nuna a kotu, wannan lambar ita ce lambar dake jikin motar da Yusuf suka fita aka sace su a cikinta, tunda Yusuf yake be taɓa ganin wannan mutumin ba me suna Sada, amma yau an samoshi an masa sharri.
Yusuf yai shiru ya dafe kai, ya kasa cewa komai.
Barrister Khalil yace "Sheda na gaba da zan gabatarwa da wannan kotu shine wanda ake zargin tare suka haɗa kai da Yusuf suka sace 'yar gidan Nasir Daula wato Saleh"
Aka shigo da Saleh, yana takawa da kyar wanda gaba ɗaya ya fita a hayyacinsa, kallo ɗaya zakayi masa kasan bashi da lafiya aka rakitoshi.
Akaje aka tsaida Saleh, Barrister Sadik yace "Malam Saleh, ko zaka iya gayamana waye kai a gidan Daula?"
Cikin murya ƙasa ƙasa yace "Ni tsohon sojane, kuma