Showing 105001 words to 108000 words out of 209297 words
gadon nasa, tasa hannu ta janye bargon tace "to shagwaɓaɓɓe, kazo ka kwanta kaƙi zuwa Asibiti, ka tayarwa da Umma hankali"
A hankali ya buɗe idonsa ya kalli Salma, cikin ƙarfin hali yace "malama fitarmin daga ɗaki"
"bazan fita ba ɗin, meke damunka ummance tace inzo in duba inga me ya kamata ayi maka"
Lumshe ido yayi yaƙi magana, Umma tazo tace "Salma yaya? Za'a iya duba shi a gida"
Salma tace "eh, za'a iya, zanje in karɓo ruwa da allurai in masa, amma ya rage kayan jikinsa, ki shashshafa masa ruwa ina zuwa"
Haka akayi Salma ta sassaka masa ruwa, da allurai sannan Yusuf ya samu kansa.
Washegari da safe da ta dawo, ta tarar da abokan aikinsa sunzo duba shi, babu wanda yasan Yusuf ɗan sanda ne a unguwar dan haka Salma tayi zaton 'yan uwansa ne suka zo duba shi, ta taho masa da Abinci daga gida.
Abbas yace "Yusuf ka samu kaci Abincin mana"
Yusuf yace "bani da appetite ne, amma zanci"
Sakina tace "ko in zuba naka, ka ɗanci ko kaɗanne?"
Salma tace "No karki damu, zeci in kun tafi da kaina zan bashi ko Yayana"
Sunkuyar da kai yayi yai mata shiru, yayin da Abbas suka shiga tsokanarsa, Sakina kuwa ta dinga harar Salma, ta dinga cika tana batsewa, saboda gaba ɗaya Haushi Salma ta bata.
Bayan ya warke ya koma gurin aiki, sedai Sakina ma ta fito da manufarta na soyayyar ta ga Yusuf, sedai Yusuf ya nuna mata sam shi babu wannan, babu maganar soyayya a tsakaninsa da ita.
Salma kuma ya maida ita kamar Ƙanwarsa, dan wataran shike ɗakkota ma daga inda take attachment, kusan duk ta kori samarinta saboda Yusuf, se sukai sha ɗayan dare suna waya, amma sam shi Yusuf ba wai dan yana sonta ba, dan ya ɗauketa ƙanwa ne kuma takan bashi shawarwari masu kyau.
Ita kanta Umma ita duk a zatonta soyayya ce tsakanin su, tana ta jin daɗi tana murna Yusuf zeyi dacen mata, dan Salma akwai kirki sosai.
Wataran Umma ta sai wata doguwar riga me kyau, ta saiwa Salma ta bawa Yusuf tace shi ze kai mata rigar.
Haka Yusuf ya karɓi riga ya kai a matsayin shine ya siya, Salma ta dinga murna tana masa godiya, har ze tafi tace "Yayana nawa nikaɗai"
Yusuf yace "meye kuma? Dare fa yayi ki bari in tafi gida"
Salma tace "Yusuf yaushe zamuyi Aure ne?"
Yusuf yace "what? Aure kuma Salma? Ai babu batun aure a tsakanin mu, ni ƙanwa na ɗaukeki fa"
"Yusuf, ƙanwa kuma? Yanzu duk abunda ke tsakaninmu ba soyayya bace? Yusuf na kori kowa a samarina, babanmu ya tambayeni, nace ni kai na tsayar yace in sallami masoyana, amma ka cemin babu soyayya a tsakanin mu?"
Yusuf yace "Salma, banyi hakan da cutar dake ba, amma dan Allah kiyi haƙuri, ni gaskiya ban shirya yin aure ba"
Ai bata jira me zece ba ta shige gida da gudu tana kuka, Yusuf ya dinga mamakin son da take masa.
Kwana biyu Umma taga kwana biyu ba taga Salma ba, tacewa Yusuf "kaga kwana biyu banga 'yata ba, ko zaka je anjima ka jimin ko lafiya?"
Nan Yusuf ya warwarewa Umma komai, aikuwa ta sameshi ta inda ta shiga bata nan take fita ba, "haba Yusuf, dan wulaƙanci yanzu duk sintiri da ɗawainiyar da yarinyar nan take damu, kace kai bakama san sonka take ba? Ni ina nan na saki baki zan samu Kayi Aure amma ka cemin kai bakama son sonka take ba? Idan ba sonka take ba ubanka take yi? Wani irin mutum ne kai Yusuf? Haba Yusuf haka rayuwa zata yi? Ba zakayi Aure ba haka zamuyi ta zama a cikin gidan nan, kamalar mutum ai aure, amma kai in anyi gabas seka yi yamma, duk abunda mutane ke gani daidai kai Ba haka yake a gurinka ba? Haka rayuwa zata tafi a haka? Wallahi in baka yi wasa ba haƙƙinta ze kama ka "
Ganin ran Ummansa ya ɓaci, yasa ya shiga damuwa ya dinga bata haƙuri, tace idan yana son ta haƙura yaje ya rarrashi Salma sannan ya amince zw Aure ta, tunanin Farko daya fara zuwa zuciyarsa shine waye ze tsaya masa yayi Auren? Amma gudun ɓacin ranta yai shiru.
Yaje gidansu Salma ya tarar bata da lafiya duk tayi wani iri saboda damuwa, Yusuf ya dinga rarrashinta, ya tabattar mata da ya amince da batun Auren, Salma ta dinga murna, take taji tama warke daga ciwon.
Suka shiga soyayya shida Salma, shi dai tausayinta da yake ji yafi yawa, dan baze ce ga takamaimai feelings ɗin da yake dashi akan Salma ba, Sone da tausayi, ko kuma tausayin ne kawai.
Nan aka shiga gulma a unguwa, wai Yusuf daga zuwansa yasa Salma ta kori kowa yana juyata yadda yaga dama, ya maida ita 'yar aikin babarsa, kullum cikin sintiri take a gidansu, saboda Salma yasa ya fara kula yayyenta a hankali sukuma suke jansa cikin jama' ar unguwa dan seka zauna dashi zaka gane bashi da wani girman kai.
Wataran suna sitting room ɗinsu Salma suna hira ita da Yusuf, ta sha ado se zabga ƙamshi take, suna ta taɗi ya miƙe ze tafi aka ɗauke wuta, aikuwa ta rungume shi tana kukan Shagwaɓa wai ita tsoron duhu take.
Yusuf yace "Salma ki cikani, kar wani yazo ya ganmu, amana mummunar fassara"
"Ni tsoro nakeji, tai maganar cikin Shagwaɓa tana sake kwanciya a jikinsa, ga wani ƙamshin turare da take yi, take jikin Yusuf ya fara tsuma, karo na farko daya rungumi mace a jikinsa, ya dinga jin wani irin yanayi yana bijiro masa, sheɗan na ƙoƙarin yi musu lalata, nan da nan yasa hannu ya raba Salma da jikinsa yai waje da saurin gaske.
Ko daya koma gida, ya sauya kaya ya kwanta ya kasa manta abunda ya faru, gaba ɗaya bacci ya ƙauracewa idonsa, tunani iri iri, a nan ya ƙara yadda da tabbas ya kai munzalin da lallai yana buƙatar mace a tare da shi, sedai waye ze tsaya masa, tunda harkar Aure dole seda uba, ko wakilansa.
Azumi ya gabato Yusuf yayi wa Salma siyayyar kayan Azumi, dana salla, Umma ba ruwanta da duk abunda ze siya ya kaiwa Salma, sema dai ta dinga yakamata ka ƙara kaza.
Ya haɗa sha tara ta arziki ya kaiwa Salma, Salma ta dinga murna tana godiya, Yusuf yana kashe mata kuɗi sosai.
Bayan kwana biyu mahaifinta yasa aka kira masa Yusuf, yace ya turo magabatansa ayi maganar Aure, tunda dai sun fuskanci juna, wahalar da yake ta isa haka.
Sedai Yusuf ya koma gida cike da zullumi a zuciyarsa, waze turo? Wa yake dashi banda Allah da Ummansa?
Bayan ya koma gida daya gayamata tayi murna, sedai itama kanta seda jikinta yayi sanyi, amma ta dake tace masa shikenan bakomai, Insha Allah za'a tura a tambayar masa, Yusuf be cikata da tambaya ba ya ƙyaleta.
Umma ta shirya ta tafi gurin Yaya ɗan lami, ta gayamasa cewar dan Allah Yusuf ya samu yarinyar daze Aura ne, tana so ba dan ita ba su wuce masa gaba su tambayar masa Aure, Yaya ɗanlami yace mata ai ba matsala, bakomai dan dai wannan, zasuyi zasuje su tambayar masa Aure.
Umma ta dawo gida tana ta murna tana farinciki, Yusuf ze Aure ze zama cikakken mutum shima kamar kowa.
Wataran ya dawo da yamma, daga gurin harkar furnitures ɗinsa, yazo ya tarar da cincirindon mutane a ƙofar gidansu, se gabansa ya faɗi ya zaci wani abune ya samu Ummansa, dan haka a guje ya ƙarasa cikin gidan yana ture mutane, yaje ya tarar da ita a zaune tana kuka, ga kayan daya saiwa Salma na Azumi dana salla, a baje a gabanta wasu mata suna cewa
"gayyar tsiya ashe bashi da uba, ya lallaɓo ze aurar mana 'ya, to Allah ya rufamana Asiri, seku koma gidan marasa iyaye inda aka ɗakkoshi, a ɗakko masa mata a can ba dai' yarmu ba, banda mutanen nan na kirki ne sunje sun gayamana, da haka zamu bawa mara uba 'ya, ai kema kin san bakiyiwa kanki adalci ba"
Yusuf ransa ya ɓaci, dan yau an masa tozarci mafi muni, dama abunda yake ta gudu kenan Umma takasa ganewa, maimakon a dawo masa da kayansa salin alin, shine seda aka tara wannan gayyar mutane sannan za' aci zarafinsa haka, kuma ma dan baƙin ciki akazo akasa mahaifiyarsa a gaba da cin mutunci kuma aka cika gidan kamar wanda sukai sata ko maita, cikin tsananin ɓacin rai da juriya, Yusuf ya kalli Matan yace "mun muku laifi, Allah ya baku haƙuri, tunda kun gama abunda zakuyi, zaku iya fita"
"Ai dole kace haka mana, tunda ka lallaɓo zakayi cuta, yarinya da samarinta na arziki amma zaka cuceta, yarinya 'yar dangi kyakkyawar gaske"
"Wallahi idan kika kuma gayamin maganar banza sena wanka miki mari, get out from here"
Yadda yayi maganar a fusace ne yasa jikinsu na rawa, sukayi waje dasu da gayyar mutanen da suka cika gidan, anata ƙananan maganganu, wai ashe duk girman kan nasa ma bashi da uba, yana taƙama da wannan kyan nasa yana hura hanci, ashe ma shegene.
Yusuf be cewa Umma komai ba, ya tattare kayan yaje ya ajiye, ya wuce ɗakinsa ya kwanta, zuciyarsa na masa wani irin raɗaɗi mara misaltuwa.
Umma tasan ba kowa ne yaje ya gaya musu wannan maganar ba face su ɗanlami, tayi danasanin zuwa ta samesu akan su wucewa Yusuf gaba akan harkar Aure, yanzu shikenan baza'a auri ɗanta ba saboda wannan dalilin? Dukda tarin nagarta dayake da ita.
Tun daga ranar ko hanyar gidansu Salma ,Yusuf be ƙara biba, ba damar ya fita ko yazo wucewa se yaji ana yada masa da maganganu marasa daɗi, ya goge lambar Salma, da duk wani abu daya shafeta.
Sedai hakan ya zame masa tamkar wani ciwo a ransa, Yana kewarta saboda sun shaƙu sosai.
Wataran ya fito ze fita aiki ya ganta a ƙofar gidansu, ya ɗauke kai ze wuce amma ta sha gabansa tace "Gurinka nazo"
Yusuf ya kalleta yace "meyafaru sauri nake"
"Yusuf, ni kaina banji daɗin abunda akayi maka saboda ni ba, ban san haka abun yake ba, amma abun yafi ƙarfina ba yadda na iya, dan Allah kayi haƙuri, kuma ka bawa Umma haƙuri, ga katin ɗaurin Aurena nan, ina buƙatar addu'arka, kuma ina fatan ubangiji Allah ya baka wadda ta fini, komai da komai nagode da lokacin ka Yusuf "
Ta zira masa katin ɗaurin Auren a gaban babur ɗinsa, ta juya tana share hawaye, shiba katin Aurenta nema ya dameshi ba, kukan da take ne ya bashi tausayi.
Gaba ɗaya ya rufe babin Salma a rayuwarsa, ya koma rayuwarsa sedai mikin nan baze taɓa barin zuciyarsa ba.
Yusuf yayi ajiyar zuciya sannan yace "ko wata biyu ba'ayi ba da abunda ya faru, aka bani aikin nan akanki, da farko nace ba zanyi ba, amma Abbas ya takurani, saboda wai ina da haƙuri, sedai ranar farko dana fara tozali dake, dukda isarki da izzarki, duk da jan aji da wulaƙancinki, se da naji zuciyata tayi bugun da bata taɓayin irinsa ba, ga kwarjininki yasa na kasa haɗa ido dake, ban shirya ba banyi tsammani ba na shiga kokawa da zuciyata akan Sonki da take, na nemi 'yar talakawa ma ban samu ba, saboda rashin asalina, ina ga ' ya kamarki, me Asali me dukiya gashi uwa uba naje a matsayin direba, se akanki na tabattar da Biyayya ce da shaƙuwa tasa na karɓi Salma a wancan lokacin, Amma wannan karon zuciyata ce da kanta ta zaɓi abunda take so, Widad bani da tabbas idan Dagaske Umma take na cewar, hatsari iyayena sukayi aka jefoni ta taga, nasan zata iya gayamin hakan dan hankalina ya kwanta, amma zance mafi yawa shine a gidan marayu aka ɗakkoni, Yanzu zaki yadda ki haɗa zuriya da mutum irina? Ki haihu dani alhalin bani da dangi se Allah se Ummana? Ni ba ina gudun haihuwa bane, nima ina fatan ganin jinina a duniya, amma kinji dalilina Auren nan kansa da mukayi a cikin zullumi nake Widad, ni dai nasan ina sonki amma bani da asalin da za'a nuna, nasan Ko Daddynki baze amince ba Widad, tuntuni nake zullumin gayamiki wannan labarin nawa, zaki zauna dani a haka?, ina sonki Widad, akanki na fara jin shauƙin soyayya, naji zan iya duk wata sadaukarwa saboda ke, dan Allah kar rashin iyayena yasa ki gujeni, ina sonki Widad ni kaina ina mamakin son da nake miki"
Ya ƙarasa maganar yana kuka, shaɓe shaɓe da hawaye kamar mace, Widad ta ƙanƙameshi itama tana kukan, ta rungumeshi kamar jariri a ƙirjinta, ta dinga shafa sumar kansa tana
"Am sorry Yoseef, am sorry kayi haƙuri please"
Kamar ta ƙara tunzura Yusuf, kuka yake sosai harda sheshsheƙa, da alama abun yana cin zuciyarsa.
Tana kuka take cewa "Yoseef dan Allah kayi haƙuri, ka dena kukan nan haka please"
Ya girgiza mata kai yace "ki ƙyaleni inyi inji sassauci a zuciyata Widad, ban taɓa yiwa wani kukan rayuwar da nayi ko na tashi a ciki ba seke, i need a shoulder to cry on, ƙyaleni inyi matata"
Widad ta rungumeshi tana kuka, tana tausayawa irin rayuwar da suka yi, dan daga ita har Yusuf kowa yaga rayuwa, kowa da irin ƙaddarar daya fuskanta a raguwarsa, amma na Yusuf ya ratsata sosai, ya bata tausayi matuƙa, ya wahala a rayuwarsa.
"zan rayu da kai a duk ya kake, zan karɓi kowane ƙalubale daze taso saboda kai, ina son Aurena Yoseef, ina son zama da kai, ba ruwana da waye kai, nagartar ka da gaskiyar ka sun wadatar dani, stop crying my Husband, nima ai kana gani ba dangin ne dani ba, daga Allah se Babana, duk dangin babu, dan haka ina so mu zama ɗaya mu samar da family nida kai, ka dena kuka mijina "
TAMMAT BI HAMDILLAH, NA KAMMALA KASHI NA BIYU ZAN SHIGA NA UKU, WANDA SHINE NA ƘARSHE DA YARDAR ALLAH
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
11/15/21, 4:53 PM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
106_107
Yusuf ya sake ƙanƙame Widad yana cigaba da zubda hawaye.
"Yoseef dan Allah Kadena kukan nan, zaka ɗagamin hankali, ya isa haka please kar kanka yayi ciwo kaji"
"Hmm, my wife tsawon shekaru talatin da biyu, abu yana damuna a zuciya, ban samu nayi kuka yadda nake so ba, dan haka dan Allah ki barni inyi, kin ƙyaleni nika ɗai nasan what i go through, na shiga damuwa da baƙin ciki daban daban a rayuwata, i suppose to cry ko zan rage "
"No Yoseef, kace Alhamdilillah daya barka da ranka da lafiyarka, kuma insha Allah daɗi yana tafe, dan bayan duk wata wuya se daɗi da yardar Allah, ka dena kuka kaji Ɗan uwana, we are now family ai ko?"
Ajiyar zuciya ya dinga saukewa, yace "Widad dagaske zaki cigaba da zama dani, koda mun koma gida?"
Widad tace "dagaske nake, Insha Allah mutu ka raba nida kai, kaine dai dai da rayuwata Yoseef, a yanzu kasanni fiye da yadda kowa ya sanni, ciki harda mahaifina, kasan abunda nake so kasan wanda bana so, you are such an amazing guy, kuma ni labarinka da naji, bazan iya rabuwa da kai ba, ƙaddarorinmu suna kamanceceniya da juna, dan haka zamanmu zeyi dai dai da yanayin rayuwar mu, zan zauna da kai Yoseef, ba ruwana da a inda aka samo ka ko makamancin haka, kuma insha Allah bazaka sake zubda hawaye saboda haka ba, ka dena kuka kaji Mijina "
Tai maganar tana share masa hawaye, itakuma tana zubda hawayen, Yusuf ya ɗago kansa yana share mata hawayen fuskarta itama yace " Am sorry Baby, na saki kuka ko? Yi haƙuri yau nayi ragwanci a gaban matata, zata rainani"
Ya ƙarasa maganar yana murmushin yaƙe, "kwanta muyi bacci, dare yayi kar gobe in Allah ya kaimu a barni da yunwa"
Yai murmushi tare da kwanciya a jikin ta, tasa hannayenta ta zagaye bayansa dashi, tana shafa sumar kansa da hannunta ɗaya, Yusuf yana ta jan ajiyar zuciya, ta shiga ɗan duddukan bayansa alamar rarrashi.
Wani irin kallo Hajiya Halima ta shiga yiwa mutumin, Mutumin yace "kina mamakin ganinane? Ai bekamata kiyi mamaki ba, butulu mara Alƙawari"
Ramlah ce ta fito ita da Amal, Ramlah tace "Mummy ya har yanzun baki tafi ba? What are you still doing their?"
Suka ƙaraso inda take tsaye ita da mutumin nan, Amal ta buɗe baki tare da dafe ƙirji, Ramlah tace "Mummy wannan kuma wanene? Barar ce baza'a bari kifi ta ayimiki ba, se an biyoki har nan, mutane sun fiye zalama kamar zasuyi ƙwace dan azabar son kuɗi"
Amal tace "kai Ramlah, babanmu ne fa, baki gane shi bane?"
Ramlah tace "What? Wannan ɗin kalle shi wani buguzun buguzun dashi kamar korarre"
Hajiya Halima tace "rufemin baki dan ubanki, Babanku ne"
Ramlah tace "Taɓɗijan, God forbid in nuna wannan ince shine ubana, alhalin ina bearing da Sunan Nasir Daula, sannan wannan yazo yace wai shi ne babanmu, Allah ya kiyaye wallahi wannan ko riƙon jakata bazan ɗauke shi ba, ni ubana ya mutu da daɗewa, sedai babansu Anwar"
Ta juya ta shige gidan tana ci gaba da maganganu, mutumin ya kalleta yace "Halima haka mukayi dake? Saboda